MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL
MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Tafada cikin kulawa Tana kallonsa,kur da ido,ajiyar zuciya ya sauke yana Sauko da kafafunsa kan lallausan Cafet din dake malale abedroom din,Dukar dakai yayi yana Jin Damuwa tayimai yawa,yana da bukatar Abokin shawara,Kuma yanzu bashi da kowa akusa dashi sai Binta,dalilin daya sanya ya dago yana kallonta kafin yace”Binta akaro na Farko Tun bayan aurenmu zan sanar dake damuwata ina Fatan zaki bani shawara don Allah..?
Gyada mai kai tayi tana Fadin”insha Allahu Alhaji,dama amfanin zaman tare kenan…”Kada kai yayi kafin ya shiga zayyanamata yadda sukayi da IGO KUMO,har zuwa karshe ya karishe da Fadin”Ya kike ganin za”ayi Binta wlh ina tsoron sanar da Sweetbby wannan al”amarin bansan da wani Fuska zata kalli Abun ba infact ma ni banison Abunda zai bata ranta ,ammh mganar gaskiya inason Malika ta auri Dan wajen Kabir kumo,ko don samu ingantattacen tarbiyan dani mahaifinta na gaza bata…”Yafada cikin Raunin murya.
Hajiya tayimai zuru tana kallonsa cike da mamaki kafin tace”Tabdijam babban mgana Alhaji,ammh azahirin gaskiya najima malika murna,domin ko ba komai Aure wani Nau”i ne na Bautan Ubangiji,da kuma Fatan Rabauta ranar gobe kiyama,ammh kuma wani hanzari ba gudu ba Alhaji a yadda ka bata yarinyarnan bana jin ko kai dakake mahaifinta zata saurareka balle kuma wani,…”Tafada tana jinjina Abun.
Dafe kanshi yayi yana Fadin”Shine babban damuwana,Binta yanzu menene mafita..? Ajiyar zuciya ta saka kafin tace”Mafita dayane Alhaji,sai dai aboye wannan mganar kada asanar da malika sai bayan an daura auren kana,koda zatayi borinta na dan lokaci ne Tunda anrigaya da an Daura auren..”
Kallonta yake yana jinjina kai alamun gamsuwa da shawaranta yace”Shawara mai kyau Binta,kinga yadda ma Tafiye Tafiyen kamfafoninnan suka gabato zata kashashe biyu ina jin kwanannan,Allah barshi sai ansanya lokacin bikin daidai lokacin da zata dawo…”Hajiya binta tace”hakan ma yayi Alhaji Allah dai ya Shigemana gaba…Da Ameen ya amsa kafin ya cigaba da sanar da ita sauran Shirinsa ammh zai ijeye komai sai yaron yazo su Tattauna.
Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan MALIKA MALIK Akan Naira 200 kachal????,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar 09069067488 Sai kun zo ina maraba daku masoyana..
Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal????shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani…
09069067488
SHAKIRA
MALIKA MALIK…!
(Sai na rama..)
ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ????
Mallakar:Janafty????
Masu tambayan MALIKA MALIK ko yakoma Free ne,No bai koma ba,yanan Ana saidawa kan Farashi mai sauki gamai bukatar Siyan Malik malik zai iya Turamin 200 kachal????ta wannan account Nombar 0552179550,bayan kin Turonin hoton sreenshoot din payment din ta wannan nombar wayar 09069067488,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar wayar shima 09069067488,kai tsaye bayan an dauki hoton katin
Ina maraba daku masoyan gaskiya????
7
“”Washegari da misalin karfe 10 da wani Abu na Safe Saleem yadau hanyar katsina bayan ya kira Abbi yasanar dashi,shikuma yakira Alhaji Abdulmalik ya sanar dashi ga saleem nan zuwa.
Shi ya tuka kansa,shiyasa ya isa akan lokaci domin dama Saleem akwai gudu amota kamar zai tashi sama,koda ya shiga cikin garin katsina bai sha wahalan gane gidan ba,sakamakon gidan Alhaji Abdulmalik Dankasuwa ba boyayye bane a katsina,cikin lokaci sai ga motarsa ta tsaya abakin makeken gidan,wanda yake kama da wata al’karya guda.
Hon ya zuba Kafin megadi ya leko yana Tambayansa sunansa kai tsaye yace”Saleem kabir kumo…”Bai yi watawata ba ya wangalemai kofar get din motarsa kirar 4matic ta sulala ciki domin dama Tuni an san da zuwanshi.
Aparking space ya Faka motarsa kafin ya Fito yana bin haraban gidan da kallo,wanda wasu tafka tafka motoci iya kallon ka mallam,sukama gidan kwanya gefe daya kuma excorts din Malika keta zagaye suna wani Mazurai Dan ware ido yayi yana bin benen gidan da kallo yana jinjinama fasahar bazanin da maginin harda wanda aljihunsa yayi kuka,domin duk Abunda yake zato,toh ya ganshi Fiye da Tunaninsa.
Komawa yayi ya jingina da motarsa Yana wasa da key din motarsa,sanye yake da Shadda mai Ruwan kasa wacce taji yarari da maiko,dinki tazarce ne yayi matukar amsansa,gefe daya kuma ya dora wata hula zanna bukar itama mai alaman zanen Ruwan kasa,hannunsa sanye da agogon Fata na kamfanin Rado,shima mai kalan Ruwan kasa,bayan takalminsa shima Rufaffafe ne na Fatar damisa,shima kalan Ruwan kasa,kallo daya zakamai kaji kakasa kara kallonsa saboda yadda kwarjinsa da haibansa ke tasiri a idon wanda ya kallesa
mace kuwa komin Girmanta da ajinta,da isarta da takamarta da duk Abunda take takama dashi,in ta kalli saleem sai taji ta raina kanta da duk Abunda ta mallaka.
Bai Dade da tsayuwa ba,yaji muryan wata mace cikin hadadden Turanci wanda dagajinsa kasan mutum ba haye yayi ba,ya kware ne,daga gefensa kamar bazai daga kai ba,sai yadaga idonsa ya Fada kan Malika wacce ke Tahowa daga bayan gidan Daga ita sai wani karamin mini sikat,da wata riga kai breziya ce ma,domin banda kokon nono bata tare komai ba gashin kanta ajike yake da karamin Towel akanta tana gogewa da hannu daya,dayan hannu kuma tana mgana awaya,fararen kafafunta da cinyoyinta awaje suna kyalli,bayan kafarta na sanye da wani Takami flat mai taushi.
Bayanta Merry ne da Dose,merry na Rike da robar Ruwansha,ita kuma Dose tana rike da wani karamin Towel din,dukkansu suna biye da ita kamar rakumi da akala,bai gama mamaki ba sai da yaga tabiyo ta gabanshi cikin wannan banzar Shiga ko ajikinta ta kuma ratsa ma,’aikatan gidan,wadanda suka kame mata kamar wata matar Shugaban kasa,Bayanta yabi da kallon Tir,yana jin wani takaichi aransa ganin yadda gabadaya idon kardawan arnan samudawan ke kan Hips dinta wanda ke Juyawa kamar wanda ake controle dinsu.
Saurin Kauda kai yayi yana kiran Sunan Allah,wani Siririn tsaki yaja yana Fadin”Lalle yarinyarnan ta Wuce da Tunanina,ashe tsinanniyace ta karshe bansani ba….’Yafada yana rike haba,yana bin Kofar data bi da kallo,Bai gama mamaki ba,sai ga Alhaji Abdulmalik ya Fito da hanzari cikin Fararen kaya yana saba babban Riga ya kariso wajen Saleem yana Fadin”Am srry na barka awaje ko..?
Yafada yana kokarin mikasa hannu ammh sai Saleem yaki bashi hannu sai ya rankwafa yana Fadin”Ina Wuni Daddy…”Yafada yana sadda kai,Dagosa Daddy yayi yana Fadin”Ash Tashi Tashi mana,Saleem ko..’,?Yafada cikin Fara”a,
Gyada kai Saleem yayi yana Sadda kai,kafadansa Ya kama yana Fadin”Masha Allah…”Yana kallonsa murna da Farinciki sun cikashi ganin Saleem amtsayin Surikinsa koshi dayake Namiji kwarjinsa ya dakesa sosai,Yana Rike dashi Har zuwa Babban Falonshi na saukan baki,ya zaunar dashi bisa kujera,wanda Saleem din yayi saurin zamowa kasa yana dukar dakai.
Yar Dariya Daddy yayi yana Fadin”A”a Haba Saleem,maza tashi ka zauna da kyau nan ma fa gidanku ne,nima Abbanka ne ko Kumo bai sanar dakai bane..?”Yana duke ya murmusa yana Fadin”Ya sanar dani Daddy kayi hakuri kabarni anan…”Dariyan Farinciki Daddy yayi yana Fadin”Toh indai ka dauke ni a mtsayin Daddynka toh na baka Umarnin katashi ka koma bisa kujera kaji..”ba yadda ya iya,sai tashi ya koma bisa kujeran yana Kallon Cafet din daya karama Falon kyau.