MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL
MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Yafada yana kada mata yatsunsa,Bakinta na rawa Tace”Ba..ni…da..wa…Ni….”Harara ya sakarmata yana Fadin”Au baki da wani ko? kodayake banyi mamaki ba,saboda ba addinin aka sani ba,comon jare,ki koma ki sako hijabi ko na waye kizo mu tafi in ba haka ba,i swear bazaki shigarmin mota da wannan Shigar ba,ba dan iska bane ni…”ya fada yana zagayawa bangare Direba da hanzari.
Batayi gadddama ba,da hanzari ta koma cikin gida.bata ga kowa afalon ba,dakin hajiya kawai ta shiga ta bude wardrope dinta taci karo da wani Farin hijabinta,dauka kawai tayi ta saka tana Ficewa daga dakin Da hajiya sukaci karo,wacce ta kalli malika da mamaki kafin tayi mgana Malikar ta rigata da cewa”Yi hakuri mommy na Ari hijabinki ne..”Tafada tana mata mirmishin yake.
Baki Hajiya ta washe tana fadin”,Masha Allah…Maza Allah ya kiyaye hanya kai madallah da samun Surikiin kwarai yau Malikar Daddy ce harda Hijabi..? Tafada tana Mata dariya,mirmishi kawai tayi kafin ta juya Ta fice,hajiya ta bita da kallon mamaki tana mai jin dadi sosai na gamin yadda komai zai tafi kan lokaci
Hajabin yadi uku ne,itama hajiyar Joda ta dinkamawa,so bai kai mata kasa ba,ammh tayi kyau sosai kamar ba malika ba,don yau itace rana ta farko data taba saka hijabi haka,Tun daga nesa yake hangota sakin baki yayi yana kallonta aransa yana Fadin So cute ashema hijabin yafi mata kyau,tana kariso ya riga daya bude mata gaban motan,shiga kawai tayi,shikuma yana kokarin tada mota dama alreday ya daura Set belt,tana jinsa yana karanta addu”ar matafiya kafin ya tada mota,suyi kwana, hon ya zubama megadi da hanzari ya wangale musu get suka sulala waje su peter na daga musu hannu.
Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan MALIKA MALIK Akan Naira 200 kachal????,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar 09069067488 Sai kun zo ina maraba daku masoyana..
Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal????shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani…
07065481260..Ko kuma 09069067488
Shakira.
MALIKA MALIK…!
(Sai na rama..)
ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ????
Mallakar:Janafty????
KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH????
15
………………………”Tunda Suka dau hanya bai kara koda kallon inda take ba,Tukinshi kawai yake,sai da sukayi nisa kana ya Saka karatun alqur’ani cikin kira”ar Mallam Abdullahi Abba,cikin Suratul Maryam,cikin kwarewa da zakin murya da hadda mai dorewa yake bin karatun…..
Tun tana rakube gefe,tana kallonsa Abun na burgeta hardai ta saki jikinta tana morema kallonshi,sai taga kamar zai waigo,sai tayi saurin kauda kai tana Kalle kalle,shiko yana ankare da ita,kawai ya barsane saboda baisan yawan mgana kada yarinya ta rainashi,duk da mawuyacin abune hakan tafaru,duba da yarda ya darsar da Tsoro mai girma azuciyarta.
Tuntana jin dadin Tafiyar har ya Fita kanta,don wannan Shine karo na Farko datayi tafiyan mota mai tsawo haka,Tun tana kalle kallen hanya,har dai wani Barci mai dadi da Nauyi ya kwasheta,bata farka ba sai dataji yana daka mata tsawa da Fadin
“Ke…”Firgita tayi tatashi da hanzari tana mutseke idonta daya chanza kala,saboda barci,tsaki yaja ya bude murfin motan ya Fita,sai lokacin ta waiga taga motar su ta tsaya abakin wani masallaci haka,agabansu taga wani Symbol an Rubuta WELCOME TO ZARIA..
Gyara zama Tayi tana bin wajen da kallo yadda yake da Hada hadar mutane,ga masu saide saide,nan kowa nata sha”aninsa waje kamar kasuwa,tabe baki tayi tana ganinshi ya tsallaka titi yaje ya dauki buta ya zuba Ruwa yashige wani lungu,da alamu zai kama Ruwa ne,sai zuwa chan taga ya Fito yaduka yafara alwala,har ya idar tana kallonshi ta kuramai ido ta cikin mota,tana mamakin yadda taga shi alwalanshi dabam dana mutane????kodai naki ne daban Hajja malika.
Agaban idonta ya Shiga masallacin ya dau tsawon mintina kafin ya Fito,kai tsaye ya tsallako Titin yazo ya bude mota ya shiga itako Tun lokacin data hangi wani mai doya da kwai yana soyawa taji miyanta ya tsinke taji shi take bukatar ci,har ya tada motar tana ta kallon Doya da kwan,inda take kallo ya kallah kafin yace”Ke lafiyanki kuwa kika kurama bawan Allah ido yana kan sana”arshi..”?
Hadiye miyau tayi tana kyafta ido,kamar wacce tayi karya,Sake baki yayi yana kallonta yadda takara kafe mai doya da kwai da ido,Girgiza kai yayi yana Fadin”Wai miye haka? ko zaki ci ne..? Da sauri ta gyada mai kai tana kara kallon mai doya da kwan,Sake baki yayi yana kallonta kur kafin yace”Ke kina da hankali kuwa? wanchan doyan da ya wuni awajen tun safe all Diseases sun gama sauka akanshi..?
Sadda kai tayi tana Share kwallah kamar wata yarinya bai yi mgana ba,illa balle murfin mota dayayi ya Fice da kanshi ya tsallaka wajen mai Doya da kwan ya Siyomata na 1k cikin leda,ya kawo mata,jikinta na rawa ta cafki ledan ta bude har miyanta nabuzowa ta Shiga ci hannu baka hannu kwarya.
Hannu ya harde kawai akirji yana kallonta yadda take tusa doyan kamar ta samu abinci,aransa yana mamakin kodai yunwa takeji ne? bai samu zarafin mgana ba,saboda ganin ta kusa cinye doya da kwan,haba ya rike kawai yana kallonta cike da mamaki,Haushin kanshi ma yaji da kallonta dayakeyi tsaki yaja ciki ciki ya Kunna motar yatadata suka Fara tafiya cikin slow.
Itako Malika hankalinta kwance take cin Abunta,sai dai kuma chan sai zuciyarta tafara tashi,dakatawa tayi tana yamutsa Fuska,ta ture ledan tana toshe bakinta sboda yunkurin Amai data Fara,Kallonta yayi rabin hankalinsa naga driving Yana Fadin”Ke wai lafiyan ki kuwa..?
Hannunta na bakinta tace”Amai nakeji..”Tsaki yaja da karfi yana kokarin samun wajen parking yake Fadin”Ba dole kiji amai ba,kalli fa Abunda kika yabama cikinki,kina ci kuma babu Natsuwa…”Yafada daidai yana parking din motar,kogama tsayawa batayi ba ta balle murfin motan ta Fice da gudu,nan bakin Titin ta gudu ta Shiga kelaya amai gwanin ban tsausayi,Fitowa yayi yana kallonta cike da takaichi yadda ta tara mai jama”a marasa gani su kyale,wani ma cewa yayi haba yallabai kamata mana wai sannu baiwar Allah”Haushin hakane yasa yaki karisawa gareta,sai dai kuma karfinta ya kare,don duk Abunda ke cikinta sai da ya Fito,tun tana yunkurin Aman harta kai tana neman Faduwa daga durkushewan.
Cikin Zafin Nama ya isa gareta ya Rikota da hanzari yana Fadin”Ke miye haka..? luuu tatafi jikinsa tana neman gadashi,Rikon ya tsaurara yana binta da kallo yadda ta bata gaban Hijabinta da amai da kuma bakinta,Saboda yadda jikinta yayi lakws ko idanuwanta bata iya budewa,Rasa yadda zai yi da ita yayi kawai sai ya zaunar da ita da karfi akasa yana Fadin”Ki zauna Dakyau zani mota na dauko miki Ruwane,in kuma kika saki jiki wlh kisha kasa no my water inside..”Ya fada yana Sakinta da hanzarin ta Daba duka hannyenta akasa ta dafe kada tasha kasa don ta lura Saleem kan babu mutumci A al”amarinsa.
Cikin motan ya koma ya dauko mata ruwan goranshi,tun da sh ma’aboci shan Ruwa ne,baya rasashi yana zuwa ya bude ya mika mata,jikinta na rawa ta karba sai dai kuma ruwan na neman barewa saboda Bata da karfi jiki,saurin rikewa yayi yana zabgamata harara bai Saurareta ba ya shiga kwararamata Ruwan agaban Hijabinta aman ya Gangara,ammh bai saka hannunshi ba,hannunta yace ta tara ya zuba mata Ruwa,Ta kuskure bakinta ta zubar sau uku kafin ya zubamata ta wanke Fuska,yana shirin zubda Sauran Ruwan ne tace ahankali..”Zan sha ruwa…”Bai kalleta ya mikamata kawai aransa yana jin Haushin kansa,kawai an cuceshi an hanashi kuka.