NOVELSUncategorized

SOORAJ 4

????????????????????????????????????????

                *SOORAJ*

     *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

*????Kainuwa Writers Association*

_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_


*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

            *WATTPAD*
      @fatymasardauna

         
            *CHAPTER 4*

Tunda ya zauna ya tallafe kansa da duka hannayensa biyu  baisake wani ƙwaƙƙwaran motsiba, numfashi kawai yake fitarwa a hankali..

Mas’oud dake tsaye akansa tuntuni yasanya hanu ya dafa kafaɗansa.

Jin sauƙar hanu akan kafaɗansa ya tabbatar masa da cewa Mas’oud ne, ɗago kansa yayi ya kalli  Mas’oud da rinannun idonsa.

Yanayin yanda Mas’oud yaga cikin idanun SOORAJ saida ya tsorita,  saboda bai taɓa ganin abokinnasa acikin matsananciyar damuwa irin wannan ba.  Zagayowa yayi ya zauna akusa da SOORAJ ɗin. Cike da kulawa yace.  
 “Basai na tambayeka ba RAJ nasan kana cikin damuwa, amma kuma bantaɓa ganinka acikin irin wannan yanayin ba, ina fata dai ba halinnaka kasake gwadawa ba?”

Sauƙe hannayensa dake kansa  yayi ƙasa, haɗe da furzar da wani irin iska mai zafi daga bakinsa, kallon Mas’oud ɗin yayi kamar zaice dashi wani abu saikuma ya fasa, kawai ya kawar da kansa gefe.

Murmushi Mas’oud yayi  tare da girgiza kansa, tun suna ƙanana suke tare shida SOORAJ saboda haka kusan gaba ɗaya halayyar SOORAJ ɗin Mas’oud yasani,  idan SOORAJ bayason yin magana, akwai wani irin kallo dayakeyi, dazaran Mas’oud yaga SOORAJ yayi irin wannan kallon, to yasan mene kallon ke nufi.

“Bazan tilastaka kacemin wani abuba RAJ amma kuma kada kamanta cewa nidakai tamkar ƴan uwan juna ne, har sai yaushene zaka tsaya kana ɓoye damuwarka? yanada kyau ko bazaka faɗa duniya tasani ba, muda muke tare dakai, muncancanci musan damuwarka, amma maiyasa ako da yaushe kake ware kanka? idan har bazaka iya faɗamin damuwarka ba RAJ banda wani amfani awajenka, haka tarayyata dakaima bata da wani amfani!”  Mas’oud yafaɗi haka cikin ƙunan zuciya, saboda shi kansa al’amarin SOORAJ yasoma basa haushi, koda yaushe SOORAJ acikin damuwa yake, abune mawuyaci kaga dariyan SOORAJ, gaba ɗaya yasamo wani banzan hali ya arawa kansa, baida aiki sai zaman ƙunci.

Kallon takaici Mas’oud yashiga bin SOORAJ ɗindashi, ganin ko alamar ɗaukar maganarsa baiyi ba, azuciye yatashi zaibar wajen.  Riƙo hanunsa SOORAJ yayi, cikin wata irin murya mai sanyi yace.  

“Bazan iyaba Mas’oud, niba namiji bane dazai iya riƙe mace, itama Nasaketa!”

Idanu Mas’oud yazaro waje cike da mamakin jin kalaman dake fita abakin SOORAJ ɗin.

“Kasaketa fa kace?” Mas’oud yatambaya cike da mamaki.

Kai kawai SOORAJ ya kaɗa masa alamar “Eh”

Wani irin tuƙuƙin baƙinciki da takaicin SOORAJ ɗinne suka turnuƙe Mas’oud, yanzu kam ya yarda cewa  akwai matsala a ƙwaƙwalwar SOORAJ domin maihankali bazai aikata irin abun da SOORAJ ke aikatawa ba.

“Anya kuwa kana cikin hankalinka RAJ? kodai asiri akayi maka ne? shin kakuwa san abunda kake aikatawa? kasaketafa itama kace? mata huɗu fa kenan yanzu ana aurama kana sakinsu, daga ankai maka mace yau washe gari kake sakota,  wai kodai aljanune dakai ??”  Mas’oud yatambayesa cike da tsananin mamaki, saboda duk wani maihankali dole ya tsoraci lamarin SOORAJ.

Kallon Mas’oud ɗin SOORAJ yayi da jajayen idanunsa, araunane yace   “Inada hankali Mas’oud kamar yanda kaima kake dashi, abu ɗaya kawai nasani shine wannan itace ƘADDARATA!”  yana kaiwa ƙarshen zancennasa ya miƙe tsaye tare da soma tattara kayan training ɗinsa,  Mas’oud na kallonsa ya tattara komai nasa yafice daga cikin ɗakin  training ɗin. Mas’oud kam kasa tashi yayi yazauna daɓas, sosai al’ajabi da kuma mamakin abokinnasa RAJ ke ƙara kamasa, shikam yanzu yayarda cewa aljana ce tashafi Abokinnasa.

SOORAJ kuwa yana fita daga wajen training ɗin direct  motarsa yanufa,   yana shiga yayi mata key tare da cillata kan titi.. 

Yana komawa gidansa yayi wanka, dakansa yashiga  cikin makeken kitchine ɗinsa, wanda yazuba masa kayan amfani, babu abun da babu na amfani acikin kitchine ɗin.     Ruwan tea yadafa kana ya juye a flask, kan dinning area yadawo yazauna tare da haɗa tea, ahankali yake sipping tea ɗin yayinda ɗayan hanunsa ke riƙe da wayarsa yana latsawa.  Safiya rana dare SOORAJ bayida wani abinci sama da ruwan tea,  arana sai yasha tea sama da sau uku,  abune mawuyaci yazauna yaci abinci kamar yanda kowa yakeci.  Yana shanye tea ɗin ya miƙe tsaye,  mug ɗin da ya haɗa tea ɗin aciki ya ɗauka ya wuce kitchine, wankewa yayi yamaida shi mazauninsa.   

Falo yadawo yazauna akan ɗaya daga cikin lallausan kujerun  falon,  remote ɗin receiver yaɗauka, ya sanja tasha.  Knocking ƙofar falon akasomayi,  cikin gajiyawa yace “Yes come in” 

Piter ne yashigo hanunsa riƙe da wasu zabga zabgan tsintsiyaye dakuma moper, ɗurƙusawa yayi cike da ladabi yace “Good Morning Sir”

“Morning” kawai yace tare da tashi yatattare wayoyinsa ya nufi bedroom,  don bawa piter daman yin aikinsa da kyau.  

Yana shiga ɗaki yafaɗa saman gado haɗe da jawo pillow yaɗaura kansa akai. Shiru yayi yana mai lumshe idanunsa, tun ɗazu kalaman Abbansa ketayi masa yawo acikin kunnuwansa, tabbas yasan dolene iyayensa suyi fushi dashi, amma shima bayin kansa bane, ƘADDARA ce baikuma isa kauce mata ba, amma yanda iyayen nasa suka ɗauki zafi sosai shine abun dayasanya yaji gaba ɗaƴa duniyar tayi masa ɗumi,   shi kaɗai yasan kansa, shikaɗai yasan wanene shi, shine wanda yasan matsalarsa,  taya ayanda yake zai iya zama da mace? sai yaushene  iyayensa zasu fahimci matsalarsa? sama da shekaru 7 kenan yana fama da matsala guda ɗaya, shiɗin namijine, baida wani wanda zaije yafaɗawa damuwarsa,  dole shine zai nemi maganin matsalarsa, haryau  kuma akan neman maganin matsalannasa  yake amma  baidace ba, shikansa bazai iya fitowa fili yafaɗi abun dake damunsa ba,   yabarwa kansa cewa matsalansa itace sirrinsa,   zama da mace kamar mafarin tonuwar asirin sa ne, yajima yana tunanin cewa shi ba’ayisa don yazauna kuma yasan wata ƴa mace ba, amma dazaran yafara wannan tunanin yake saurin furta astagfirullah domin yasan saɓone yakeyi, to amma yazaiyi shima bayida zaɓi ne, akullum akuma koda yaushe da Allah kawai ya dogara….  

***   Tana zaune aɗaki tayi jigum abubuwane suka haɗe mata, aƴan kwanakinnan sosai take mamakin sauyan da  Inna Ma’u tayi, tarage sata yawan aikace aikace, sannan kuma koda aikanta ne yanzu andainayi bakamar daba da kullum ƙafarta na waje tana yawon zuwa aika,  yanzuma tana zaune ne aɗakinta tana sauraran hayaniyar ƙawayen Inna Ma’u dake tashi a tsakar gidan,  itadai batasan meke gudana acikin gidannasu ba amma tabbas tasan cewa akwai wani abu da za’ayi acikin gidan.   Zulai ƙawar Inna Ma’u ce ta yaye  yagalgalellen labulen dake ƙofar ɗakin nata. Ayatsine ta watsowa Ziyada dake zaune harara,   “Uwar munafurci saiki fito ae” cewar Zulai, tana gama faɗan haka kuwa tasake labulen tayi tafiyarta.

Jiki asaɓule Ziyada tafito daga cikin ɗakin nata,   Gani tayi su Inna Ma’u sun baje akan tabarma yayinda suka kwaɓa lalle awani babban fanteka.

“Zo maza ki zauna” ɗaya daga cikin ƙawayen Inna Ma’u tace da Ziyada.

Cikin sanyin daya zame mata sabo taƙaraso ta durƙusa agabansu, ƙirjinta sai bugawa da sauri yake saboda tsabar tsoronsu da take.

Zaunar da ita sukayi agabansu, yayinda suka sanya ta kwaye musu cinyoyinta,  da ƙarfin gaske suka shiga durza mata ƙwaɓeɓɓen lallen ajikinta, hatta fuskarta saida suka mulke mata shi da lalle,   itadai ganin abun take awani baƙon yanayi, saboda tasan agarin nasu  idan za’awa mace aurene kawai ake yi mata haka,  suna gama shafa mata lallen sukace taje ta wanke,  wani irin daɗine yaziyarci zuciyarta, domin albarkacin wannan lallen da suka shafa mata yasa zatayi wanka, bata mantawa rabonta da wanka yau sati guda kenan, dokace mai zaman kanta Inna Ma’u takafa mata akan cewa duk randa tayi wanka, bazata sake yi ba sai bayan wani satin, ruwa takandama abaho tayi bayinsu, alokacin da tacire kayanta tasoma watsawa jikinta ruwa, saida ta sauƙe wasu lafiyayyun ajiyar zuciya harsau uku, saboda wani irin sanyin daɗi daya ratsata, dama ita tuncan haka nan Allah yayita, tanada tsananin sonyin wanka, amma kuma bata samu tanayi saboda uƙubar Inna Ma’u.   

Inna Ma’u kuwa masifa ta rufe ƙawayennata dashi wai akan mai zasu kwaɓa lalle su shafawa Ziyada.  Zulai ce tagyara zama haɗe da turo ɗaurin ɗankwalinta gaba.    “Wallahi yanzu na tabbatar baki da wayo Ma’u, kinga wannan lallen damuka shafa mata, shizai sanya jikinta yaƙara kyau, hasken fatarta yasake fitowa, kinsan yarinyar shegiya ɗanbanzan kyaune da ita, to kinga yanzu zata ƙara kyau akan nada, idan Tsoho Ɗan Dashe kuwa yaganta, saiya ƙara susucewa akanta, kinga ke kuwa kinsamu hanyar da zaki amshe masa ƴan kuɗaɗe kice kuɗin gyaran jiki, ai abirni haka akeyi kinsan nifa nayi zaman birni”

Shewa Inna Ma’u tasanya haɗe da bawa Zulai hanu suka tafa, cike dajin daɗi tace “Wallahi shiyasa nake mugun sonki Zulai, kinsan kan duniya,  aikuwa ayau yau saina karɓi wani abu daga wajensa”     sake tafawa Inna Ma’u da Zulai sukayi daidai lokacin Ziyada tafito daga wanka, zanine ɗaure aƙirjinta kanta gaba ɗaya yajiƙe yake da ruwa, tana shigewa ɗakinta, Zulai tadawo da kallonta ga Inna Ma’u cike da mamaki tace “Wai Ma’u dama haka wannan yarinyar keda diri da kyau? nikuwa anya basu haɗa iri da larabawa ba?”

Taɓe baki Inna Ma’u tayi, domin ita aduniyarta babu abun datafi tsana kamar taji anyabi Ziyada,  “To wama yasanine tsinannu, ai tunda nasamu nagama da uwarta itama yarinyar bawuya zata bani ba, wannan shegen idanun nasu masu kama dana aljanu yana ɗaya daga cikin abun dayasa na mugun tsanarsu, gashi komai na halittar uwarta ta kwashe!” Inna Ma’u tafaɗi haka cike da baƙin ciki. 

“Aikuwa Ma’u kinyi farar dabara da kika haɗa auren ta da Ɗan Dashe, kinga zata ƙare rayuwarta cikin ƙasƙanci, kinsansa baya riƙe aure, duk da yagama tsofewa, amma baijirayi kansa ba,  dakin tsaya kuwa kina nan zakiga wani sarki ko senata sunzo neman aurenta”  cewar wata daga cikin ƙawayen Inna Ma’un, wato Lantana.

“Cab iye bakinki Lantana, ina darai kam ƙaryane wani mai arziki ya raɓi Ziyada, sam hakan bamai yiwuwa bane, koda kuwa zanyi yawone tsirara na gwammace nayi, dana bar jinin Maryama ta auri wani mai kuɗi, nama kashe maciji bansare kansaba kenan” Faɗar Inna Ma’u.  Dariya suka sanya sudukansu, yayinda ƙawayennata sukacigaba da fonfata….

Ziyada kuwa tsabar taji daɗin jikinta da tayi wanka tana kwanciya kawai sai bacci ɓarawo ya saceta…

Washe Gari. 

*** Tun tashinta yau takejin faɗuwar gaba, babban abun daya ɗaure kanta shine, ƴan uwan mahaifinta da tagani sun cika gidan, da’alama dai kamar biki za’ayi agidannasu bata kuma san bikin waye za’ayi  ba.   Tazo wucewa zata shiga banɗaki  wata ƴar addar babanta  ke cewa “Amarya Amarya bakya laifi Amarya agidan Tsohon najadu” 

Jitayi gabanta yafaɗi cike da mamaki tajuyo tana kallon Hajara wacce tafaɗi maganar, bakinta na rawa tace.   “Yaya Hajara wacece amaryan?”

Harara Hajara ta watsa mata domin dama tun can su bawani sonta suke ba.   “Wace amarya kuwa inbanda ke, ko baki da labarin cewa gobe za’a ɗaura miki aure da tsohon najadu?” Dariya Hajara tasanya haɗe dacigaba dacewa “Abun yayifa yarinya ta auri wanda yagirmi ubanta” sai takuma sake bushewa da dariya.

Jikin Ziyada ne yasoma rawa, lokaci guda taji cikinta yayi wani irin murɗawa atsorace ta ƙaraso gaban Hajara tazube aƙasa, murya na rawa tace  “Dan Allah Adda Hajara kifaɗamin gaskiya, auren waye za’ayi?”

Kallon kinma rainamin wayo Hajara tashiga yiwa Ziyada  ahasale tace..   “Bansaniba munafuka, waye baisan cewa kema son auren kikeba? dama ai kowa yasancewa ke tsohuwar hanuce, wayasanima koshima Tsohon najadun ya ɗana”   

Kuka Ziyada ta fashe dashi da gudu ta tashi tanufi ɗakin Inna Ma’u, tana shiga ta zube agaban Inna Ma’u dake tsaye, cikin kuka tace. 
“Dan Allah Inna Ma’u kimin rai, kifaɗamin cewa maganar da Adda Hajara kefaɗi bagaskiya bane, wai dagaske aurena za’ayi, kuma ɗan dashe zan aura?” 

Wata uwar tsuka Inna Ma’u taja haɗe da ɗauko ashar ta bankawa Ziyada cike da takaici tace 

“To idan bakiyi aure ba kwaɗaki zamuyi mucinye?   inbanda ƙaddarama me Ɗan Dashe zaiyi dake, shima dai dayake tsohon maye ne shiyasa, amma bacin haka banga maiyagani awannan busheshshen jikinnaki ba, da Allah nitashi kibani waje, kuma aurenki da ɗan dashe babu fashi, gobe iwar haka kinzama matarsa”   

Kuka Ziyada tashiga rerawa hadda majina tana roƙon Inna Ma’u, amma Ina Inna Ma’u haka ta murje idanunta.

Komawa cikin ɗakinta tayi hankalinta amatuƙar tashe, zama tayi daɓas aƙasa haɗe da ɗauko wani mayafin mamanta ta rungumeshi ƙam acikin ƙirjinta, kuka take tamkar zararriya… 

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button