Dr.TAHEER HAUSA NOVEL

Suna zaune parlor gaba dayansu da daddare…ummi na kallonta tace”iceko dai kin gama hada kayanki Layla…banaso sai gobe kizo kina cewa bakiga kaza ba ko kin manta kaza”..a hankali Layla ta daga Mata Kai tace”na gama tun dazu ummi”…toga abincin Taheer can dauki kije ki Kai mai naga har yanxu bai shigo ba”…ba musu ta mike zuwa inda abincin nashi yake ta dauka snn ta tafi..a zuci take addu’ar yau dai Allah ya dorata a kanshi ya saurareta.
Bata ganshi parlor ba don haka ta ajiye abincin snn ta nufi bedroom dinshi.. Saida tayi sallama a bakin kofan ya amsa snn ta bude kofan ta shiga ciki…Yana zauna kan gado da system a gabanshi ya tattara hankalinshi gaba daya kanta..da alama abu mai muhimmanci yakeyi a ciki….a sanyaye Layla ta karasa ciki ta zauna kan bedside kanta a kasa tace”daddy ummi ne tace in kawo maka abinci”..ya Dan kalleta ta gefen ido kafin yace”ohk”…a hankali ta baro inda take tazo tayi kneeling a gabanshi tana hawaye tace”daddy Dan girman Allah kayi hakuri…wlhy ba laifina bane”ba tareda ya kalleta ba yace it’s ohk…ya riga ya wuce ai”…ta shiga girgiza kai tace”wlh daddy nasan baka hakura ba…kullum haka kake cewa amma baka dena yin fushi Dani ba”…a hankali ya ture system din dake gabanshi tareda saukowa daga gadon Yana kallonta yace”ba damuwa kije abinki…nace maki ya wuce koh”yana gama fadan haka ya juya zai shiga toilet…Layla ta mike da sauri zatai hugging nashi yace”Maryamm”…cak ta tsaya tana zaro ido…tun tashinta zata iya irga sau nawa ya kirata da sunanta…ko Layla baya fada amma yau shine ya kirata da”Maryam”…tasa hanu ta toshe bakinta kar kukan dake cinta ya fito snn ta juya da sauri ta fita daga dakin….Taheer kasa shiga bathroom din yayi…ya koma gefen gado ya zauna tareda dafe kanshi da hannu bibbiyu yanajin yanda zuciyarshi ke tsalle tana bugawa kmr zata bar kirjinshi…yasan abinda yake ba daidai bane Amma ya kasa Bari…dukda tausayinta dake cinshi kullum amma da zaran ya tuna zata auri wani zaiji kaman zai zauce…harda wnn dalilin yasa ya kasa sakin jiki da ita bayason abubuwan dayake ji a zuciyarshi gameda ita…kmr Wanda akama allura ya mike zumbur tareda ficewa daga dakin…direct ya nufi part dinsu…ba kowa parlor don haka ya wuce dakinta.
Tana kwance tana rusan kuka kmr zata shide kawai taji yasa hanu ya dagata zaune…da mamaki ta tsaida kukan tana kallonshi…sai kuma ta shiga murza idonta wai ta tabbatar ba mafarki take ba…ganin shi din ne yana Mata murmushi ta fada jikinshi tareda fashewa da matsanancin kuka…a hankali Taheer ke shafa bayanta yanajin kukanda take har cikin brain dinshi…Saida tayi me isarta snn ta dago ta bude baki zatayi mgn yai saurin dora yatsanshi a kan bakin yace Mata”shishshssh…don’t say anything okay?…just relax kiyi baccinki…we shouldn’t talk about it at all…not now not ever…banason jin mgnr kwata kwata”…a hankali ta daga mai Kai snn tace”Amma daddy ka denayin fushin Dani?…zaka koma yanda kake a da?…yai murmushi ya shiga share Mata tears din fuskarta yace”ni dama ba fushi nakeyi dake ba baby…wnn daddyn(yayi pointing kanshi)bazai taba iya fushi da wnn babyn ba”(itama yayi pointing dinta)…Layla batasan sanda wani kyakykyawan murmushi ya subuce Mata ba…ta sake rungumeshi tace”na gode sosae daddyna…I love you”…Saida ya lumshe ido snn ya bude don dadi…he wish I love you din nn ba a matsayin daddy take fada mai ba…a matsayin hubby yakeso yaji tace I love you din nan…da hakan zai faru ko da baisan farin cikin da zai samu kanshi a ciki ba…a hankali yai breaking hug din tareda kwantar da ita…ya lullubeta tareda yi mata peck a goshi…yana murmushi yace Mata”to Saida safe”…a hankali ta amsa mai da good night snn ta lumshe idonta..shi Kuma ya kashe mata hakse snn ya juya ya fita…he’s feeling extraordinary happy…shima duk sanda yake fushi da ita tamkar Yana fushi da kanshi ne…bai taba samun peace of mind har sai an shirya…Yana zuwa daki ya fada bathroom yai wanka tareda Shirin bacci snn ya kwanta..aiko nan da nan baccin daya jima bai samuba yayi gaba dashi.
(Umh asuba ta gari daddyn baby????)
Washe gari da wuri suka kammala shirinsu.. driver ya kwashesu sai airport…basu bata lokaci sosae ba kuwa suka shiga jirgi sai Kanon Dabo✈️
Sun sauka a gidan umma…bayan an huta anci abinci…sai aka dasa hira a nan parlor..shikuwa Taheer ficewa yai zuwa wurin wani friend dinshi.
The following day bayan sunyi breakfast sunyi wanka…gaba dayansu suka nufi Sallari gidan qanin mahaifin Taheer mai suna Alh Adam Jakada.
Bayan sun sauka an gama gaggaisawa ummi ta sanar dashi abunda ke tafe dasu…yayi farin ciki sosae ya Kuma tabbatarwa ummi cewa zaizo Abuja next week zaaje ayi mgnr auren Taheer kmr yanda ta bukata…su ummi nata murna amma Taheer abinda yakeji is not close to murna at all…Sam bayajin dadin ma mgnr.
Sun jima a gidan don sai wajen 4 snn suka koma gida…Taheer ya sanar da ummi kan zasuje Danladi Nasidi shida Layla..gidan wata cousin sis dinshi mai suna Amina Aminu Kibia…’yar qanwar dad dinshi ce and ba karamin shiri sukeyi da itaba.
Suna tafe a hanya duk inda sukazo sai ya fada Mata sunan unguwan haka har suka isa Danladi Nasidi.
Daidai kofar gidan Sis tashi yai parking snn ya dau waya ya shiga dialing number dinta..Allah yasa bataje wurin aikiba don bai sanar da ita he’s coming ba..he wanted to surprise her… ringing biyu tayi picking call din tace”doctor yau an tuna dani knn”…Taheer yai Dan dariya snn yace”yanxu dai kina Ina?..tace Ina gida wlh..yau Ina off”…bai sake cewa komai ba kawai yai hanging wayar…ya kalli Layla yace”let’s go tana ciki”..ya bude motan ya fita snn itama ta fito suka shiga cikin gidan…daidai entrance din gidan suka tsaya…Taheer ya danna doorbell…ba’a dau lokaciba wata yarinya tazo ta bude musu kofan..”sannunku da zuwa”yarinyar ta fada snn ta basu hanya suka shiga ciki…Saida suka zauna a parlor yarinyar ta gaishesu snn tace Bari in kirata…ba bata lokaci sai gata ta shigo parlon…kyakykyawa da ita tanada dan qiba amma ba sosae ba fuskanta dauketa fara’a sosae ta karasa ta zauna idonta a kan Taheer tace”dama saida jikina ya bani wlh…inajin ka kashe waya nace maybe you are coming”Taheer yai dariya yace”ai muna kofar gidan nn ma na kiraki…mun shigo gari ne nace gsky bai kamata in koma ba tareda nazo mun gaisa ba…Ina Maimunatou?…Amina na dariya tace”aiko ba karamin kyautawa kayiba wlh…jiya muka gama mgnrka da abban Hanan yace kwana biyu yajika shiru… Maimunatou tana bacci wlh Bari insa Abu ta taso muku ita ku gaisa”…da sauri yace”no a barta tayi baccinta”…Amina na kallon Layla da fara’a tace”baby koh”…Layla dake kallonsu tun dazu tana murmushi tace”eh nice…Ina yini”…lfy Lou baby ya skul…Layla tace alhamdulillah ya Maimunatou…”Maimunatou tana nn qlou wlh… Abu…ta kwalama mai aikinta Kira sai gata ta shigo ta risina tace”gani anty”…Amina tace”ki kawo musu lemuka da abinci snn kije dakin Maimunatou tana bacci ki kawo musu ita su ganta”…yarinyar ta amsa da toh snn ta mike ta fita…Saida ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye snn ta tafi dauko Maimunatou…Taheer yai pouring drink a cup ya mikama Layla ta amsa…shima ya zuba a wani cup din Yana sha yace”so yau kina off knn”…Amina tace”wlh kuwa…jiya na gama night yanxu sai nayi off din kwana Hudu snn zan juya evening…ya aiki..yasu ummi”…yace”aiki alhamdulillah ana nn ana fama wlh…ummi itama tana nn kano…tana Janbulo gidan qanwarta…tace tana gaisheki sosae”…Amina tace”Allah sarki ummi Ina amsawa wlh…Ina nn zuwa Abuja ai Amma sai bikinka”Taheer yadan harareta yace”aiko Zaki dade baki jeba yarinya”…daidai nan mai aiki ta kawo musu Maimunatou…Taheer ya karbeta yana kollonta yace”MashaAllah…kiga yadda yarinyar nn tayi girma…kmr su daya da babanta”.. Amina na dariya tace”ai Maimunatou akwai saurin girma…duk Wanda ya ganta sai yace tayi girma”…a hankali Layla ta taso daga inda take ta matso kusa dashi tana murmushi tace”daddy Dan bani in dauketa nima please…yarinyan tamin kyau”..ba musu Taheer ya Mika Mata Maimunatou ta karba…tayi shiru kawai tana kallon yarinyar kyakyakyawa da ita…su Kuma sunata hirarsu…basu suka bar Danladi Nasidi ba sai after magrib…shima da kyar Amina ta barsu suka tafi don cewa tai saiya jira mijinta ya dawo sun gaisa…ta cika Layla da kayan mk up su turaruka snn ta rakosu har mota suka tafi.