SALAHADEEN COMPLETE NOVEL

馃挮鉁� TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)馃専
(Tsintsiya mad’aurinki d’aya)馃
鈽� [ T.M.N.A] 鈽� 馃摉馃枈锔�
Bismillahir rahamanir rahim
1锔忊儯3锔忊儯
Cikin d’an firgici ta kalleshi ta dafe hannunshi tace “Mr. ka d’agani na tashi, kar mamie ta same ka fa ko matarka.”
Fuskarta ya kalla yace “Ke fa? Ai ke ma matata ce.”
Da wani murmushi tace “Ta jahu ba.”
Jin ta rik’e hannunshi d’ayan saiya d’ora d’aya kan mamanta ya rik’oshi da kyau tare da saita bakinshi ya cabki nipple d’inta, zabura tayi tare da rufe idonta da sauri, dukan k’irjinta ne ya k’aru da k’arfi da kuma sauri, bata tab’a samun kanta a irin wannan yanayin ba sai yau, wata hallita a duniya bata tab’a d’ora hannunta kan nononta ba, hasalima ko rumgume juna wanda zaisa aji shauk’i ko dan sha’awa ko soyayya bata tab’a yi ba da wani, mugun tsaro Abhi ya saka mata ta yanda bata isa ta keb’e da wani baligin d’a namiji ba, gaisawa tsakanin hannaye ko sumbatar kumatu wannan tayi da dama da abokanta yan makaranta da abokan kasuwa ko huld’a. Amma yau ga wani dan babu Abhi tare da ita har ya hau ruwan ciki yana tsotsar mamanta kamar ita ta haife shi.
Shi fa har ga Allah dad’in yanayin yake ji sosai, basu da girma sosai ka rantse da Allah kace dama dan shi akeyi su, duk hasken fatarta sai suka fi zama jawur dasu musamman nipple d’in, wani irin d’umi ne jikinta ke fitarwa daga b’argonta zuwa fatar jikinta wanda yake jinshi kamar bargon rufa a muk’umuk’un sanyi, hakan yasa yake ta k’ara matseta a jikinshi ba tare daya raba bakinshi da mamanta ba.
K’arfi tasa sosai tayi nasarar ture shi gefe ta zabura ta tashi zaune tana kallonshi, cikin kayan daya siyo mata ta finciko wata riga ta rufe jikinta, yana ganin haka ya k’arasa kwantawa kan katifar yana kallon sama amma idonshi rufe yana sauke numfashi da k’yar.
Ganin bai motsa ba yasa ta mik’ewa tana tattara kayan da nufin shiga uwar d’akin, tunawa da tayi abun cajin wayarta jiya Iffa ta tafi dashi d’akin yasa ta tahowa da wayar a hannu dan ta jonata anan, kai tsaye ba tare da neman izini ba dan tasan Sarah ce kawai ta shigo. Kwance ta ganshi ido rufe inda Sarah ke tattare kayan zata shige d’aki, bata san sanda wayar ta kubce a hannunta ba tana k’ara kallonshi.
Fad’uwar wayar ce ta farkar dashi ya tashi zaune, suna had’a ido da ita yaji duk jikinshi yayi sanyi, yunk’urawa yayi zai tashi Farha ta juya da gudu ta bar d’akin, Sarah ma na ganin haka da sauri ta shige d’aki suka barshi. Wani tsaki yayi na jin haushi da shi kanshi baisan manufarsa ba, mik’ewa yayi da k’yar yana had’a hanya da shi fa ya gama kunnuwa.
Duk underwear d’in nan sun matseta sosai har bras d’in saboda bata da ciwo shara shara ce, hakan yasa ta sanya wata riga mai hannaye wacce bata kama ta ba da kuma wando slim wanda bai k’arasa sauka k’asa ba kamar na kayan data zo dasu, falon ta dawo ta zauna ta had’a kai da gwiwa tana kallon d’akin da tunanin abinda Salahadeen ya mata.
Yana shiga ya sameta zaune tana kuka, zaune yayi shima ya kai hannu zai rik’ota ta janye jikinta tana fad’in “Karka tab’a ni yaya Salahadeen.”
Kallonta yayi kamar zaiyi bacci yace “Lafiya kike kuka? Me aka miki?”
Da wani mamaki ta kalleshi tace “Me aka min? Me aka min ma kake tambayata yaya Salahadeen? Na sameka da wacce kod’add’iyar a d’aki Allah kad’ai yasan abinda kuka aikata, kuma ka tambaye ni me aka min?”
Zuba mata idonshi yayi yana kallo dan shi dai ba zai ce baiyi ba sai dai tayi duk abinda zatayi, mik’ewa tayi tace “Ka fad’a min gaskiya yaya Salahadeen, dan Allah me ye tsakaninka da ita tun farko? Budurwarka ce ko kuma karuwarka?”
Wani kallo ya mata ya yatsina fuska yace “Karuwa? Haka kike kallona dama?”
Had’e hannaye tayi ta kawar da kai tayi shiru, mik’ewa yayi ya kalleta yace “Babu komai tsakani na da ita bayan igiyar auren data d’auremu zuwanmu nan, kuma ki sani da mama bata amince ba da ban aure ta ba, karki ga Sarah a k’aramin gidan nan naku ki d’auka wata k’ask’antacciya ce har ki nemi taka ta, ba dan juyawar da rayuwa tayi da ita ba, wallahi da zakiyi wata kina neman ki ganta na minti biyar ma abun ya gagara, yanzu haka da za asan tana rayuwa anan to da rabin k’asan Tha茂lande ce zaki gani a k’ofar gidanku sun zo ganinta, kar kiyi anfani da kishi kice zaki raina min wayo.”
Juyawa yayi zai fita tayi saurin cewa “Indai babu komai tsakaninku to kawai ka sake ta, gaskiya ni ban yarda da auren nan ba naji hankali na ya fara tashi.”
Juyowa yayi ya kalleta yayi murmushi yace “Almakashin datse igiyoyin suna hannun Mama.”
Fita yayi ya barta inda ta bishi da kallo, k’wafa tayi tace “Shikenan bari Mama ta dawo zansa ta datsa igiyoyin da kanta.”
12:00 su Iffa suka dawo ita da Mamuh, Mamuh kad’ai ta mata magana kafin ta shiga ta watsa ruwa, ko da suka kimtsa Iffa ta shiga girkin rana Mamuh kuma ta fito da kayanta dana Mama ta shiga wanki.
K’arfe 01:00 na rana mama ta dawo, kallonta Sarah ta shiga yi da mamakin kayan jikinta, saida ta zauna ta kalleta tace “Saratu kinci abincinki?”
Girgiza kai tayi alamar a’a, da mamaki ta bud’a ido tace “Baki ci ba? Me kika zauna yi? Ba kya cin shi?”
Kallonta kawai tayi ba tace komai ba, kamo hannunta tayi ta taso daga kan kujerar ta zaunar da ita k’asan carpet inda take, kallonta tayi tana shafa kanta tace “Me yasa baki ci abinci ba?”
Duk da kuka ne ke son taho mata amma saita had’eshi gam ta zuba idonta k’asa kawai, juyawa tayi inda ta aje mata abin karinta, yanda ta aje shi haka ta ganshi, gimtse baki tayi tace “Kenan Salahadeen baiji abinda na fad’a masa ba?”
Saida ta cire safar k’afarta ta ciro k’aramar wayarta a jakar ta danna ma lambarshi kira, da sauri ya datse kiran tare da maidowa da kud’inshi, tana d’auka kafin yace wani abu tace “Nagode da kula min amanata da kayi, da kasan ba zaka iya ba saika ce min na nemi wani.”
Cikin ladabi yace “Mama wani abun ne ya faru? Me tace miki na mata kuma?”
“Hum.” Kawai ta fad’a tare da kashe wayar, gabanshi ya shiga fad’uwa na tunanin abinda ta fad’a ma mama, da sauri ya baro inda yake tsaye kan gininshi wanda yanzun rashin kud’i ke naman kawo masa cikas ya taho gidan.
Ko da ya shigo d’akin ya samu Sarah na fad’in “Na rok’eki mama ki ce masa ya mayar dani gida, zan koma can nayi rayuwata duk yanda ta zo min.”
Shigowarshi ne tasa mama kallonshi tace “Uhum kaji ko? Gida take so dan haka ka mayar da ita kawai wajen mahaifinta.”
Kallon Mama yayi ya durk’usa yana fuskantar Sarah yace “Amma kuma Mama..”
Da sauri tace “Amma me? Dole ka mayar da ita tunda kai ma ba zaka iya kula da ita ba, ka dubi yarinyar nan yanzu misalin d’aya har da ashirin amma bata saka komai a cikinta ba, yunwar da kace bata sani bace kake son dole saika sanar da ita ta santa? Me yasa zaka mata horon yunwa Salahadeen?”
Saida ya d’an sunkuyar da kai tare da lumshe ido dan gaba d’aya mantawa yayi, cikin rarrashi ya d’ago ya kalli Mama yace “Kiyi hak’uri dan Allah Mama, wallahi mantawa nayi har na fita.”
Da sauri ya kalli Sarah dake ta k’ara matse k’afafunta duk tayi sanyi yace “Me kike so ki ci na siyo miki?”
Saida tasa hannaye biyu ta matse cikinta sosai tace “Ni ciki na ke ciwo, ka bani magani nasha.”
Da sauri ya kalli Mama yace “Wai cikinta ke ciwo.”
Kallonta mama tayi ta janye hannayenta tana d’an latsa cikin nata, kallonshi tayi tace “Ina tsoron yunwa ce take tunanin cikinta ne ke ciwo?”