A BAKIN WAWA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

A BAKIN WAWA COMPLETE HAUSA NOVEL

A BAKIN WAWA COMPLETE HAUSA NOVEL

tace’ sannunkin fa da aiki irin wannan aiki haka?

Gaisawa sukayi sannan Antu tace’ fito muje muci abinci to,
suna tafiya Anty tace’ Ai da weekend Bama tashi da wuri sai mu Kai shabiyu muna bacci abinmu muna tashi kawai abincin Rana za’a daura kuma har yaran,

Karasawa sukayi suka zauna a wurin dining sai dai ba’asa dining ba a kitchen ta ga ansa Shi, Ummi ma ta tashi har an Mata wanka,Basu jima ba sai ga Nafisa tace’ Ina kwana tana kallan Ummusalma,amsawa tayi, tace’ Mommy ina kwana,

Anty safiya ta kalleta tacet yau kuma kece da gaidani Haka?

Tace’ Kai Mommy kema de kinsa ai mantawa nake shiyasa ai,

Anty safiya tace’ Ai bakya manta da gaida babanki ko?

Ai wannan special ne ina zan manta dashi?

Ohh nikuma ba special ba ko?

A,ah kefa ta dabance,

Kinga zuba mana abinci ba wannan surutun zamuci ba,

Tana kokarin zuba abinci, tace’ Anty yau mun tashi da wuri ko Dan muna da bakuwa kar tace mana makararru shiyasa tana tashina na tashi,

Anty safiya tace’ yanzu ma hakanne don ba abinda kikayi ai du ita tayi wannan aikin har abincin da kike zubawa, wani ana tashin ki da bansan hali ba de,

Shiru tana cuno baki irin haba din nan agaban bakuwa kuma?

Ummusalma kallansu kawai tun jiya idan suna dramar su, ta lura akwa shakuwa sosai a tsakaninsu ko ajiyan sai da ta tuna Mama a lokacin da take taken shagwa arta sai dai kuma a yanzu tasan tayi bankwana da wannan abu, sai dai ina a lahira idan anayi, suna cikin ci wani yaro ya shigo ya girmi ummi sosai don zaiyi shekara goma,ummi tana ganinshi ta hade Rai karasowa yayi,,
yace’ mommy ina kwana,

Anty safiya tace’ lafiya qalau Ka tashi lafiya,

Yace’ laaa Momy ina zanci ,

Tace’ Baka gaid a bakuwa ba,

Juyawa wurinta yace’ ina kwana, da lafiya ta amsa,

Ummi tace’ Kai kullum kullum sai kazo ko ba makaranta ko?

Yace’ eh din sai nazo din wurinki akace nake zuwa kome? Ko gaida ni bakiyi zaki fara ko? Sai na mauje maki Baki marar kunya kawai,

Shiru tayi tasan yanzu tsab sai Anty safiya tasa yamata duka don babu reni a tsakanin yara gidan batasan dalilin dayasa reni ya Shiga tsakinta da Yaron ba,
Babu Wanda ya Kara magana har suka Gama sai da suka Gama Nafisa ta kwashe kayan ta Kai kitchen ta wanke su tas, tace’ Bari taje ta gaida mutanen gidan, da to kawai ta masa mata, parlour suka dawo suka zauna suka kunna kallo suna yi, Ummusalma ta kalli Anty safiya

tace’ Anty safiya maman Shi fah,
Kallan Anty safiya tayi

tace’ laa wai Ahmad, Ahmad Cousin din Ummi ne gidan Suma ba a jikin gidan nan yake kuma akwai kofar da ta shigo tana shiyasa kullum Yana nan idan banfita aiki ba shiyasa,

Ummusalma tace’ Anty safiya shifa,

Wakenan?

Ehhm Bi…bi…bi…na..nai…f

Numfashi taja tace’ nagane,
Hannunta taja suka je daki hotuna ta dauko ta ajje mata Akan cinyarta,Zama tayi a kusa da ita cikin nuna halin nadamuwa,

tace’ Binaif be taba tambayar mahaifiyar shiba, Bansani ba ko ya tambayi Rukayya wacce ya tashi a wurinta,
Shiru tayi sannan tace’ ki bude hotan mahaifiyar sane,

Bude hoton tayi wata budurwa tagani fara da ita kyakykyawan kallo daya zakayi Mata Ka gane hakan,idan Ka kalli idan ta kuma zakace Mata bafilatana,suna kama da Binaif sai dai idanshi ba irin ta bane nata kana ne na Fulani shikuma idansa ba madaidaici ne,bakinta yafi nashi pink shape dinne irin daya,kallon take sosai tana kare matar kallo hannunta kuma rike da jariri kallanta ta dawo kan Anty safiya wacce take kallanta,

tace’ to tana ina?

Kwallace ta taru a idanta ta share,
tace’ babu Wanda yasani,ko ta mutu? Ko tana da Rai? Bamu sani ba Sai Allah,

Da’alamar tambaya ta juya kallan kallonta,

tace’ bangane ba?

Anty safiya tace’ bazaki gane ba idan ba bayani aka maki ba,

Tace’ zaki iya Bani labarin ?

Ganin tayi shiru alamar tunanin yasa Ummusalma kamo hannunta, tace’ don Allah,
Asalin mu mu ‘yan kauyen Alkaleri karamar hukumar Bauchi, mu hudu iyayen mu suka haifa Dan Lami shine Mahaifimu Amma asalin sunasa Ahmad Bansan dalilin da yasa ake fada masa haka ba, Ada can ma Shi Dan kasuwa ne kuma Yana tafiye tafiye da ada tafiyar tana daukan lokaci kafin aje inda za’aje a kuma dawo, mahaifiyar mu Zainab wacce ake Kira da Hajja Abu wasu kuma suce Mata mai tagwayen suna, Hajja Abu tun tana karamar ta take da masifa rashin hakuri,rashin gani ta kyale komai ta hada ba ruwanta da Kai ko waye, dayake a da ne kuma ana yiwa Mata auren wuri shiyasa aka Rasa me aurenta sai Dan Lami Wanda yake Dan uwa a gareta,kwata kwata halinsu bezo daya ba,Amma da yake Shi mutum ne mai karamci iya Zama da mutane yasa Shi Jan ra’ayinta suke zaune, Dansu na farko Usman sai da aka shafe kusan shekaru hudu Allah yabasu Adam, Usman da Adam kusan tare Baba yasa su a makaranta dake cikin garin Alkaleri,Shi beyi ba shiyasa yasa ‘ya’yansa, dukda za’a iya cewa usman kusan halin Baban Shi ya dauko sai dai Sam Shi magan a baya dame Shi gashi kuma da dankaren zuciya, shikuma Adam tun Yana yaro yake da Jan magana shiyasa basa jituwa shida Umma, sai kace ba halinta ya biyo ba, har sun fitar da ran Kara haihuwa bayan shekaru goma aka haifeni a lokacin suna Usman Yana da shekara sha biyar Adam nada goma Usman Yana makarantar secondary sannan kuma Yana koyar da primary dayake da haka akeyi idan Ka gama Zama koyar kafin Ka tafi jami’a, Nima koda na taso sai ya kasance halina dana Adam ba daya ba,nafi sabawa da Usman a haka muka taso sai nayi shekara uku aka haifi Ruqayya itakuma sai ya kasance Adam ke dawainiya da ita komai shike Mata sai da shekara shida aka sani a makaranta lokacin tana Shekara uku itama sai da tayi shida aka sata, mun taso cikin so da kaunar junanmu tare da tarbiyar iyaye sai de kuma bamu da wani lokaci Wanda ya wuce na karatu,muna tasowa daga boko zamu tafi ta Allo dayake da duk shi akeyi, har gwara mu muna da Dan lokaci Amma su Basu da wani lokaci idan ba dare ba shima sai can dare suke dawowa saboda sana’ar dasukeyi don su taimakea kansu su ragewa Baba wani abu, bayan wani lokaci Yayinda Usman yasamu wani aiki a Ilorin na man fetur kawo lokacin akwai mota jefi jefi,shima kuma Adam yasamu aiki a Kano na koyarwa dayake Shi fanin education ya karanta,yayin da nikuma bami cigaba ba, Aikin da suka samu Baba beso ba sai dai kuma Jin Adam a Kano yake yasa Shi Jin damadama,Yayinda Umma tayi tsalle ta diri tace Adam bazaije Shi ba yayi nesa da gida a gida ma tana fama inga ya fita wani wuri, duk yarda akayi da ita ki tayi kawai sai Baba yace mu tafi tare tunda Yana zuwa acan yayi ya cigaba da sana’ar Shi, wannan shine dalilin tasowar mu daga cikin dangi muka dawo nan kano Yana aikin Shi koyar a gidan da aka bashi Wanda akwai komi da komi aciki ba bukata daga nane Baba ya fara sana’ar Shi kuma ta karbe Shi don har gidan kansa yayi,muna cikin haka mane ma suka fara fitowa inda Baba yace Yana so ne mu karanci bangaren lafiya, Adam ne ya samu mana nursing a BUK anan muka fara karatu, a Yayinda aka yiwa Adam transfer ya koma Alkaleri kuma aka Kara masa matsayi, ba yarda Umma ta iya ta hakura ta barshi bewani jima ba aka kuma maido Shi,Yana dawowa kuwa ya yace’ ya Sami matar aure Amma yaran Giwo ce,ba haka Umma taso haka de ta hakura tayi shiru Amma ba tasan auren nan Allah Yana ya gani bayan anyi aure ta jima bata haihu ba, sannan kuma bata zuwa gaida Umma ita kuwa Umma daman can basanta take ba shiyasa ko bi takanta batayi, Sai da ta shekara uku ta haifo ‘yarta mace,a haihuwa ta biyu ma mace ta haifa, anan kuma aka masa transfer ya koma Adamawa aka kuma Kara masa matsayi saboda haza karsa a wurin aiki zuwansa Adamawa a inda yake aiki ya hadu da wata zulai
Ihat, dayake mutanen da akwai rike amana ganin sa mutum kamili da Shi yasa suka bashi aurenta sannan kuma aka taho da iayenta, a tunanin sa umma zatayi wani Abu sai dai kuma ganin ta nuna bakomai yasa Shi Jin dadin haka satinsu guda anan gidan su sukace zasu koma Suma su Umma suka biso don ganin wuri, Babu ta inda yasamu matsala sai a wurin matar Shi Hajiya Kenan tayi borin ta kada ta Raya Amma a banza, zulaihat yarinya ce mai hankali da girmama na gaba sa’ar Ruqayya ce shiyasa komai nasu yafi zuwa daya ba ta da matsala ko kadan kowa Yana santa, sai alokacin Usman yace’ zaiyi aure,dayake Baba bame matsawa haka ma Umma ita dai kawai barta a fada kosa ya shaida da wannan musamman idan kayi Abu baka nemi shawarta ba, a lokaci ne kuma mutuwar Baban Umma ya riske mu gabadaya muka tafi a motar Usman bayan wani lokaci aka daura auren Usaman da matar da ya gani acan kauye a kauyen aka daura ya dau matarsa suka tafi Ilorin,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button