A BAKIN WAWA COMPLETE HAUSA NOVEL
A BAKIN WAWA COMPLETE HAUSA NOVEL

Karasawa kofar gidan yayi tare da knocking,Jin shiru yasa ya karayin wani namma de shiru karawa yayi sannan yaji ance waye?
Shi besa ba da wani waye ba,hasalima yasaba kawai door bell zai Danna yazo a bude,
Amma wani waye? Shiru yayi don besan mezai ce ba,
Zuwa tayi ta bude masa, yace’ mai gidan nan?
Eh Yana nan,
Kice yayi bako,
To,
Ta koma bata jima ta dawo tace’ ance Ka shigo,ita ke masa jagora har cikin parlourn sannan taje ta kawo masa drinks da snacks, duda da safe ne.
Wani mutum yane ya fito kamili babba dashi, wuri ya samu ya zauna suka gaisa sai kuma sukayi shiru, mutumin yace’ ban shaida kaba,
Binaif yace’ ai baka sanni ba, amma wala’allah idan na Baka tambaya zaka iya tambaya hadina da komawa waye,
Mutumin yace’ wannan wacce irin tambaya ce haka?
Murmushi kawai Binaif yayi,
yace’ game da companyn ka, bayan Kai waye shugaban Ka?
Sosai mamaki ya bayyana a Saman fuskar mutumin nan, yace’ Kai waye din Muhammad ne?
Fadada murmushin sa yayi yace’ Sirikinsa ne, nasan daman tambayar Kenan,
Yace’ siriki? Kai yaro Muhammad daga har ‘ya’yan sa guda biyu da matar sa sun rasu, da dansa kace min ne ma Zan yarda,
Binaif kamar yarda na fada maka ni sirikin sane kuma Ka yarda dani, ‘yar sa nake aure Ummusalma koba ita bace?
Sosai mamaki ya lullubi mutumin yace’ ‘yarsa? Bata mutu ba? Tana ina? Ina take?
Yace’ bata mutuba,Abu daya nake so da Kai shine Ka fadamin Kai waye din shine? Aboki ? Dan uwa? Kode wani Abu haka?
Numfashi mutumin yace’ sunana Munir Yakubu, Dan asalin garin Gumel mahaifiya ta rasu tun ina yaro Babana Shi ya rikeni dukda mitar yayi aure da ake masa Amma yayi biris da zancen kuwa, Shi yaciga da Kula Dani har na Kaiga nagama Nce dina,Amma babu aikinyi a lokacin Babana ya fara ciwo kafa dayake Nika yake yi sai naciga dayi sabida aikin da za’a masa
Gashi kuma injin bayayi kullum Yana cikin gyara wayanci shike cinye mana kudin,kawai na saidashi na tafi Lagos don samu kudi,sai dai kuma kasan cewata sabon Shiga aka sa cemun kudi ga babu wurin kwana ga yunwa da wahala zafi komai ya hade min,nasami gafen titi na zauna kwatsam wata mota tazo ta bigeni tayi gaba Allah ya rufa asiri ma banji ciwo ba sai dai naji jiki,jiki ya kama ciwo Bansan meke damuna ba, idan nace zanyi dako kafin na dauka har andauke anyi gaba,ga ciwon kafa Ashe nayi tagade ruwan da zan shama aiki ne, ina kwance a gefen titi awannan lokacin mutuwa kawai nake bawa kaina,sai ga Ya Muhammad da Matar sa Sunzo sun taimaka min sun kaini asibiti bayan na warke suka tambayeni inda nake na fada masu na kuma Basu labari,shine ya biya kudin aikin sannan yace zai Samar min aiki a kusa da gida don nake zuwa ina Kula da mahaifina,banyi musu ba na yarda bayan anyiwa Babana aiki yazo da kanshi ya daukeni ya kawo ni nan garin ya nuna min komai da komai da shagunan sa da inda yake da Zama gidajen sa komai nashi wai gudun bacin Rana, koda na tambaya shi Baya tsoran na cuce Shi? Sai yace duk Wanda ya cuci wani kansa ya cuta ba Shi ba,da wannan Babana kullum yake Kara min nasiha Akan kar na yaudareshi na rike amana ko a zuciya ta Bani da buri cutar sa, a haka muka shafe shakara uku ina masa aiki duk wani Abu da yayi sai ya fada min, sai dai Mahmud Baya San haka ko kadan Amma be taba nunawa ba,ya daukeni tamkar kaninsa haka itama matarsa, lokacin da ta samu ciki ya sai wani fili yace duk Wanda aka haifa yazama nashi, ranar da ta haihu ranar amaida wannan fili sunan Dan da Umar don ni har na manta ma da anyi zancen, sai dai washegari da za’a sallame mu a asibiti aka nemi da aka rasa daga karshe aka gano sace Shi akayi kuma ya mutu, bayan anyi hakuri suka kuma samun wani ciki suka haifi twins mas’ud da mus’ab sannan suka dawo Abuja inda ya cigaba da kasuwancin sa,Iyayen matar sa sune suka rike Shi don Shi don Shi a hannun matar uba ya tashi mahaifinta ya daukeshi da suke unguwa daya a yarda ya ban labari Kenan, sai da twins suka shekara hudu Allah yasake a zurta su da Ummusalma suna Santa, tana da shekara biyu a duniya aka nemi yayunta aka rasa kosama ko kasa ba’a gani ba, anyi haka da sati daya gidan su ya kama da wuta, inajin labari washegari na tafi Abuja ganin gidan su ya kone kuma babu kowa da yake zaman makoki yasa na tafi kafancan Inda Iyayen su suke sai dai na iske babu kowa a gidan sun tashi, haka na dawo jikina ba dadi, ga kuma wani labari da ya riskeni cewan Mahmud ya mallake duk wata kadara ta Shi,banyi mamaki ba don nasan zai aikata hakan, sai dai bai san shagunan sa na nan ba da wani dake Paris shima besani ba Dani da Wanda yake Kula Dana Paris muka cigaba da Kula da komai dake hannun mu bayan na fada masa halin da ake ciki.
Shiru yayi na wani lokaci sannan yace’ gashi kazo Kace min Kai siriki sa ne taya?
Binaif da labarin ya Dan daure masa Kai Yana so ya bi komai a hankali ne, numfasawa yayi,
yace’ shine ya dauke ta ya so ya lalata Mata tarbiyar ta, sannan ya turata karatu don tarbiyar ta ta war gaje, sai dai Allah ba nufa ba hakan bata faru ba, sannan Yan uwanta Suma duk suna nan da ransu Umar ne bansan inda yake ba,Amma shima na tabbata Yana da rai,
Taya zakace Umar na Rai?
Sabida ta taba ganin wani, ba wannan ba ina so ayi wani abu ,ya saida min da company guda daya dake Kano ya kuma bani takardun karya a matsayin sune na gaskiya nikuma ina da na gaskiyar a hannu na ina so mu hada karfi da karfi mu yaki karfe,kayi wannan sadaukarwa ga abinda ya maka,
Koba baka fada ba yaro, zanyi komai Insha Allah indai komai Nasu zai dawo, bawan nan ba gidan marayun dake Lagos ya sayar dashi yanzu duk yaran da aka Kai can to idan suka taso kasar waje ake tura su, wasu suna aikin miyagun kwayoyi wasu kuma fashi, Mata kuma a tura su bauta gida Jen aikin reno wanke wanke da dw sauran aiki,sa’ar daya ce basa bata Mata masu rayuwa sai dai Basu San inda zasu tsinci kansu a ciki ba,ga kuma yunwa da suke fama da ita,
Ina so mu fara daga nan kafin muyi komai,
Binaif yace’ to shikenan Insha Allah daga nan zamu fara amma abinda nake so daki Ka fara nemo mana wanne percentage ake bashi,
Taya Zan iya Nemo percentage din da ake bashi? Baya ga haka ya sayar dashi,
Murmushi Binaif yayi yace’ koda ya sayar dashi bazai Bari haka kawai ba, dole za’a bashi wani Abu daga ciki, zaka iya nemowa tunda ka iya sannin an sayar dashi,
Zan duba na gani,
Cigaba da magana sukayi har biyu tayi masu sani ba, bayan sunyi sallah Binaif yace’ zai tafi
Dakyar ya tsaya yaci abinci sukayi exchanges numbers daga nan ya dau hanya Yana tafiya yaji Karan shigowar sako be Kula ba, wannan Karon yayi gudu a hanya don uku da rabi ma acikin kano tamasa kafin ya karasa gida anyi la’asar Yana zuwa bakowa a parlour jakarsa ya dauka ya Shiga ciki sai da yayi wanka yasa kayan shan iska yayi sallah sannan ya kwanta ya janyo wayar sa ganin message din ta yasa Shi budewa,
Nayi tafiya zuwa Adamawa, take care.
Besan abinda yaji ba don bazai iya fada ba, take care Shi yafi bashi haushi ma, ba gaisuwa bakomai sai take care juyi kawai yake Yana maimata take care din nan ina laifin ma ta Dan masa message din na morning ko yaji sanyi a ransa,Amma sai take care da ce masa,tsaki yaja a Karo na ba adadi wayar ma ajje tayayi Yana tunanin su Mus’ab ne suka shigo banza yayi masu ya cigaba da abinda yake,