NOVELSYAR BANGAR SIYASA COMPLETE

YAR BANGAR SIYASA COMPLETE

Misalin ‘karfe takwas sun shirya tsaf! sun fito da jakkunansu, da duk abinda suka san nasu ne a cikin gidan, suka fito tare Uwani da Rashida suke jan akwatinan kayansu yayin da Wasila ke bin bayansu cikin sanyin jikinta, wani irin yanayi mara dad’i takeji a cikin zuciyarta…..Bakin gate suka nufa, Wasila ta fito da keys din gidan ta mi’kawa d’aya daga cikin masu gadi tace”Idan As yazo su bashi. masu gadin gidan kamar zasuyi magana sai kuma sukaja bakinsu sukayi shiru suna kallonsu suka fice daga gidan da akwatinan kayansu…….A jigaje ta ‘karisa bakin babban titi dan wannan tafiyar da sukayi ya sanya ta haki! dan har sai da suka samu guri suka zauna ta huta tukkuna kafin su cigaba da tafiya…….Babur din a dai-dai sahu suka samu ya daukeshi zuwa tashar kabuga.

“Wai wannan wane irin wulakanci ne ? na shigo gidanka tun safe ka shanya ni a palo sai kace yaronka ina ta fama zaman jiranka kai kana can kanayin abinda ya dameka, idan ba zaka fito ba zanyi tafiyata ba wai ban san gidan bane.”!!! Ahamdu yake waya da khalifa lokacin da yake kai komo a tsakiyar palon nashi……Khalifa ya fito daga bedroom d’insu kunnanshi ma’kale da waya yayin da Hafsa ke biye da bayansa hannunta rike da turare da kuma hularshi tana gyarawa.

Ahamadu ya dinga watsa musu harara kamar idonsa zai fad’o ‘kas! Yace.” Ga d’an iska kun bari yana muku jiran gida kun shigo ciki wai me yasa bakwa gajiya da abu guda ne.”!! A zafafe yake maganar……Hafaa ta gumtse dariya kanta a ‘kas tana sanyawa mijin nata links din hannunshi tace”Allah ya huce zuciyar governor ba wai abinda kake tunani muke ba, lokacin da kazo gidan bamu dad’e da tashi ba shiyasa.”

Ya maka mata harara yace.”Ke kika san wannan ni a gurina karfe shida na safe ba safiya bace lokacin duk wani me himma yake tashi domin gudanar da harkokinsa na yau da gobe ke kuma a lokacin kike sake ma’kalewa wai ke gaki wacce ta iya soyayya.”

Khalifa yace.”Wai meye laifina nan ne? tayi fa ‘kokari sosai kawai kazo mata gida da asuba kuma kace sai kaga yanda kake so ba zai yuwu ba lokacin da kazo ma ni ko tashi banyi ba wayarka ce ta tasheni.” Yace.” Dan Allah ni muje dubi time kun ‘batawa mutane lokaci mtsss!. Duk suka bishi da kallo cikin mamaki masifa yake musu sai kace sune suka sashi ya aikata abinda ya aikata shine kuma zai zo ya d’aga musu hankali basuji ba basu gani ba…

A mota ma sai mita yakewa Khalifa, wanda tun baya ramawa har ya shiga ramawa ya dinga yi masa shagu’be duk domin ya fahimci cewar shifa d’an taimako dan haka ba zai zo ya dinga d’aga mishi hankali ba idan yana so ya cigaba da samun nutsuwa da kwanciyar hankali to yayi gaggawar dawo da iyalinshi gabansa, To
wannan magana da khalifa yayi itace ta kashe masa baki yayi shiru sai dai jefe jefi yakan ja tsaki ya duba agogon dake daure a hannunsa.

Dai-dai gate din gidan khalifa yay parking ya shiga horn da sauri daya da sauri mai gadi ya bude gate din dan duk sun dauka As ne sai bayan motar ta shiga cikin gidan ne suka gane cewar bashi bane……….Shine ya fara fitowa kafin Khalifan ya fito…….Dake masu gadin biyu ne daya sai ya tsaya bakin gate din daya kuma ya nufi in da suke….Gaishesu ya shiga yi yana so yayi magana amma be san me zaice ba yaso dai ya shaida fuskokinsu mussaman Khalifa da shine yayi zuwan karshe cikin gidan…….Shine ya fara yin gaba da nufin shiga cikin gidan sosai Kafin Khalifa yace.”Ka d’an dakata na kira wayarsu naji ko.” Dan tsayawa yayi yana ya mutsa fuska, Khalifa ya kira numbar wayar Rashida dan itace me waya kuma numbar ta ya kar’ba, Wayar na hannunta tayi saurin d’agawa tana kara wayar a kunnanta lokacin suna tsakiyar tasha suna ciku cikun hawa mota……..Tayi ta fadin “hello ” hello “hello network da hayaniya sun hanata jin muryar Khalifa inda shi kuma nashi ‘bangaran yana jin muryar ta rad’au! sai dai dik inda take tana cikin hayaniyar jama’a da ababen hawa! Fad’i yake ” Rashida kina jina? kina jina.” Da karshe ma sai wayar ta tsinke yay gaggwar cirota daga kunnanshi yana dubawa…..Mai gadin dake tsaye yace.”Yallabai mutanan gidan fa basa nan dan tun sassafe suka fita da akwatinan kayansu da alama sunyi balaguro ne.”! Ya wani juyo a sukwane! yana kallon gate man d’in bakinsa na motsi……Mai gadin yace.”Amma dai ina kyautata zaton yanzu basu isa tasha ba ko sun isa baici ace sun tashi ba tunda kasan dole kafin mota ta tashi sai tayi lodi sai dai kuma muma bamu san inda suka nufa ba.”

Jikinsa ya soma wani irin rawa! yana kyarma! kafafunsa suka shiga kyarma Cikin tsawa da d’aga mirya Yace .”Wane irin wawanta ne wannan!? Wane irin sakarci da hauka ne yasa zaku barsu su fita! meye amfaninku a gidan!? waye ya basu izinin fita da jakkunan kayansu!? ina kuma suka tafi? Ina zasuje! min da gudan jinana? sai muryarshi ta shiga rawa yana wa tsawa masu gadin mugun kallo babu marasa tunani da kwakwalwa kamarsu da har suka barsu suka fita daga gidan sun riga sun cutar dashi mutukar sukayi sanadiyar zubewar cikinsa dama tun jiya yake ji ajikinsa akwai abinda zai faru, Ya kalli khalifa yana tsuma!!! Yace.” Ko ina suka nufa sai na lalubosu! dan basu isa su yanke min
wannan hukuncin ba, kawai ka shiga mota muje.” Yana maganar ne a sanda yake nufar motar tasu cikin gaggawa da kuma saurin gaske ya bude motar ya shiga
khalifan dake tsaye cikin mamaki! ya rasa ma tunanin da zaiyi ashe wasila bata da hankali dama? tanajin abinda likita tace dangane da lafiyarta da babynta amma zata dauki jiki suyi tafiya mai nisa cikin mota mai kwajab kwagab! babu sakarkaru sai masu gadin gidan da suka barsu suka fita daga gidan……..Da saurin gaske yabi bayan abokin nashi ya shiga motar da gaggawa ya mayar da murfin ya rufe Ahamdun yaja motar da karfin gaske, ya nufi kofar fita daga gidan cikin sauri wanda yake bakin gate din ya matsa gefe guda yana zazzare idonsa.

Littafin na kudi ne……!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap Numbar
07084653262[14/08, 12:04 pm] Farida Books: ‘Yr Bngr Sys
57
Zaman motar ne ya isheta ta dinga ya mutse fuskarta tana dan tsartar da yawu ta tagar motar kanta ne ke sarawa tana jin wani irin amai na taso mata, hayaniya ta mutane duk ta cika mata kunne ga warin fetur da tsamin hammatar wata mata dake kusa da ita d’aga rigarta ta fito da nono ko kunya ba taji tana shayar da yaronta alhalin motar da akwai maza a cikinta, haushin matar ya sanya ta dinga dauke kanta tana jan tsaki wasu matan sam babu kintsi da kamun kai cikin motar haya mai dauke da mazan da ba muharraman ta ta fito da nono kowa nagani gashi da ta motsa warin hammatar ta zai buga……Mutum biyu kacal ake jira motar ta tashi Wasila duk ta kosa su tafi ko ta sha’ki iska mai dad’i bayan warin hammatar matar ma mazan dake ciki wasun sy wari sukeyi abinka da wanda rana ta daka….Uwani da rashida kam hira sukeyi suna cin awara da suka siya kafin su shiga motar…Kira ya shigo wayar rashida dake kan cinyarta. Da sauri ta kalli Wasila dake zura kanta tagar motar tana shakar iska tace”Anti Wasila kinga Khalifanan ya sake kira.” Tace”Ki daga mana to.” Rashida ta d’aga wayar tare da fad’in “Hello.” Khalifa dake driving yay sauri mika mishi wayar ya kar’ba da sauri yana kokarin kara wayar a kunnensa ta fad’i ‘kasan site sakamakon rawar da hannunsa yake yi….Kasancewar wayar ta bugu da karfi yasa ta mutu ya dauko da sauri ya kunna ta bude, ya lalubi numbar yana sake kira, A dai-dai lokacin ne kuma wasu matasa suka shigo motar direban motar ya Umarci rashida ta gyara sosai domin su samu gurin zama garin gyarawa wayar dake cinyarta ta fad’i kasan motar ba tare da ta sani ba….Aikuwa shi wanda zai zauna kusa da ita ya sanya hannunsa ya dafe ta, a take yay dubarar cire sim din lokacin da Rashidan ta juya suna magana da Wasila ya jefa wayar karkashin kayanshi, Rashida matsatsi da xafin mota ya sanya ta manta da wayarta burinta kawai su tashi saboda zafin ya isa…..Aikuwa sai da direba ya cika motarsa tsaf sannan ya shiga ya zauna maxauninsa ya tashi motar suka fita daga cikin tashar suka dauki hanya

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button