Uncategorized

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE HAUSA NOVEL

washegari, inayin sallar asuba nafara gyaran dakina,yau sonake nagama aikina da wuri domin inason zuwa unguwarmu. Harna gyara falo na koma dakina na kwanta, babu Wanda yafito,har kuku kuwa. Tunawa nayi yau Saturday, may be weekend basa tashi da wuri. Se wurin karfe goma da wasu mintuna suka fito,nima fitowa nayi danyin aikina. Serving dinsu nayi ina gaishesu,wasu suna amsawa wasu kuwa ko kallo ban ishesuba, ninama Riga nasaba da hakan,kamar kullum yauma duk sun hallara amma babu oga. Harna juya zantafi mommy ta tsaidani da fadin na shiga kitchen madauki breakfast dinsa nakai masa. Seda zuciyata ta buga sosai, saboda tsoro. Amsa mata nayi nakoma dakina nadakko rigartasa na boyota acikin hijabi. Basket din kayan Karin kumallonnasa na dauka, zuciyata na dukan tara_tara, ina tafe Inayin addu’a. Da sallama nashiga falon kasa, babu kowa se mayen kamshin turarensa,sama na haura, yana zaune akan kujera 2siter yanata fama aiki a computer. Dukda bugun da zuciyata takemun haka nadaure nashiga da sallama, labbensane kawai ya motsa alamar ya amsa. Tsugunnawa nayi cikin girmamawa nace, “ina kwana” batare daya dagoba yadagamun hannunsa, karasa wa nayi najere kayan akan dinning, gabansa na dawo na durkusa akaro na biyu, cikin matukar tsoro na mika masa rigarsa. Dagowa yayi yakalleni na wasu y’an sakanni sannan yadauke kansa karbar rigar yayi ya budata. Kallona yakeyi yana kallon rigar, nandanan jikina yafara rawa, saboda babu wasa kokadan a fuskarsa. “Dan Allah kayi hakuri, wlh bada sanina na konaba,tsautsayine” nafadi haka cikin rawar murya inashirin fashewa da kuka. “Meyasa kika konamun Riga?” Yajehomun wannan tambayar cikin tsawa,fuskarsa a hade. Cikin in’ina nace, “ba….ba.ko..mai.” Daradaran idanunsa yazubamun, kasa nayi dakaina hawaye yafara zuba a idona,saboda tsoro. Cillomun rigar yayi becemun komaiba,yamaida hankalinsa akan abunda yakeyi. Ahankali nadago kaina na kura masa ido, duk yanda naso dauke idona daga kallonsa amma nakasa, yana sanyene cikin farar jallabiya. Gaskiya ada gaba daya kallon tsoro nake masa, seyanzu nakara ganin tsantsar kyawunsa, ada inaganin kamarsa da mommy, amma yaunagane yafita kyau nesa bakusaba, babuma hadi, kuma ba mommy kadaiba dukama mutanen gidan duk ya fisu kyau,farar fatarsuce kawai daya. Mintuna goma, suka shude, amma beko kara kallonaba, nikuma aikin kallonsa kawai nakeyi ina tasbihi ga ubangijin dayayishi,wani Abu naji yana shigata akansa, Wanda bansan yazan fasalta mukuba, domin bantaba Jinhakan akan waniba. Kafata ta sagemun saboda tsugunnon danayi, gyarata nayi ina sauke doguwar ajiyar zuciya. Kallona yayi ya nunamun hanyar kofa, tare da fadin, “kisan yanda zakiyi kikawomun wata rigar,bakonanniyaba, tunda ke bakyajin magana,kokuma na babballaki agidannan” waro idona nayi waje cikin tsorata nace, “dan All…..” “Go out!” Yakatseni cikin tsawa. mikewa nayi ina kara sauke nannauyar ajiyar zuciya, ajiye rigartasa nayi ina satar kallonsa, wata uwar harara ya wurgamun dasauri na dauki rigar nafara tafiya, Ina tafe ina waiwayensa harna fice. Tsaki yaja bayan ta fice, yalura yarinyar akwai yarinta sosai atattare da ita, ga kuma abunda yatsana wato saurin kuka,ga kuma rashin ji. Yarasa meyasa mommy takeson irin wadannan yaran a matsayin y’an aiki,wadanda babu abunda suka iya banda shirme, dasawa mutum ciwon kai. tabe bakinsa yayi yacigaba da aikinsa….. (Kaikadai dai????)

Ina tafe ina gulmarsa araina, hoton fuskarsa yaki bacememun daga idona,gadai tsoronsa daya cikamun zuciya,amma jinakeyi dama bekoreniba inzauna inta kallon fuskarsa me kyau,niyau fadannasama burgeni yayi. Seda nafara ajiye rigar adakina, sannan nafara gyaran dakunan su mommy. Abun mamaki mommy bata tambayeni mena tsaya yiba harna dade. Se suhailat cema naji tana magana tana hararata, nibanmaji metaceba, hankalina yana wani gurin daban. Bayan nagamane na tambayeni mommy, inason zuwa gida, tace nabari senakara kwanaki yanzu yayi kusa, dududu satina dayafa. Haka na hakura na koma dakina, bayan na dibi abincin Karin kumallona, inagama ci na kwanta, Inata tunanin yanda zan iya biyansa rigarsa, niba kudiba idanma inada kudin inazansamu rigar insai masa, Allah ka sassauta zuciyar bawannanka ya hakura, dan tun jiya danakaimasa lemo na fuskanci ransa abace yake. bansan sanda bacci yayi awongaba daniba Inata tunane_tunanena……….

Suhailat ce tashiga falon mustapha da sallama, duk da sallama ba dabi’arta bace, amma shi tana masa dantasan idan batayiba casata zeyi. Bedago ya kalletaba ya’amsa mata akan labbansa. Zama tayi agefensa tana fadin, “yayana ina kwana?” Dagowa yayi yajefeta da wani kallo be amsa mataba,yamaida kansa, yacigaba aikinsa. Marairaicewa suhailat tayi ta fara magana cikin shagwaba. “Haba yaya ina maka magana kaki kulani, meyafarune jiyama da daddare nakiraka da yawa amma bakayi picking ba, pls yaya I’m sorry idan na maka lefi” Wata uwar harara yadago ya zabga mata, wadda tasa yayan cikinta hautsinawa. “Waye Wanda yazo gurinki jiya?” Yajefo mata wannan tambayar cikin kakkausar murya. Rasss! Gabanta yayanke yafadi, dama yasan kamal yazo, nashiga uku ni suhailat, Ashe duk boyon danakeyi yasan da zuwannansa. Cikin alamun rashin gaskiya tace, “am… Cla..ss ma..te dinane” “kifadamun gaskiya, kinsan banason karya ko?” Yafadi haka yana tsareta da idanunsa, kasa tayi da kanta cikin matukar tsoro, batason fushinsa ko bacin ransa, saboda be iya fushiba. “Dagaske nake yaya” bekara cemata komaiba yacigaba da aikinsa. Gajiya tayi da zama ta mike jiki asabule ta fice, dankarta kara wani lefin. mommy ce kawai zata iya shawo mata kansa, yanda taga tsananin bacin rai atattare dashi…….

Seda akayi sallar azhar na tashi wanka nayi tare da dauro alwala. Ina idar da sallah nafita falo domin yin kallo, dannagaji da zaman da kwanciya kuma nasan yanzu babu kowa a falon. Ina shiga falon naga yaya sadiq, shikadai azaune. Da mamaki nake kallonsa. “Yaya sadiq, ina wuni?” Nagaisheshi bayan nazauna. “Lafiya kalau, maryama ya gidan?” “Alhamdulillah yau lafiya naga baka fita aikiba?” Murmushi yayi yace, “kinmanta yau weekend ne” “eh hakanefa bamanta” tasowa yayi yadawo kusa dani yazauna. “Meke damunkine maryam, naga kamar da damuwa akan fuskarki?” “Bakomai yaya, amma meyasa kullum.kake tambayata haka.” Murmusawa yayi yace, “saboda inaganin hakan atattare dakene, amma senaji kinje bakomai, ko bakyajin dadin zaman gidannamune?” “A’a kokadan bahaka bane kawaidai kai kake ganin haka” bebani amsaba yazira hannunsa acikin aljihun wandonsa, wani zobe na azurfa me kyau ya mikomun yana fadin, “saka wannan ahannunki, naga hannunki ko ring daya babu” cike da mamaki nake kallonsa, “kaii yaya sadiq, amma yayi kyau sosai, nagode Allah yasaka da alkhairi.” “Babu komai kanwata ni dake da suhailat duk daya nadaukeku agurina,duk abunda zangani insai mata kema zansiya miki” murmushi nayi inasaka azurfan a danyatsana na tsakiya,naji dadin kalamansa sosai, kaf gidannan bayan baaba talatu babu Wanda nakejin dadin kasancewa dashi tamkar yaya sadiq, yanada kirki sosai bakamar yan’uwansaba,shiyasa nasaki jikina dashi. Azurfar tamun kyau ahannuna kuma tamun dadidai tamkara angwadani. Godiya namasa sosai, harseda yacemun godiyar ta isa haka. labari ya shiga bani na’abun bandariya, daga baya muka koma hira. gaskiya yadebemun kewa sosai, wadda harta mantar dani rikicinmu da oga. Muna cikin hirarne mommy tashigo falon. Tunda tashigo namata sannu, naja bakina nayi gum. Hira suka farayi da danta, nikuma na maida hankalina akan kallo.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button