Uncategorized

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE HAUSA NOVEL

Sallama namasa batare daya juyoba ya amsamun zama nayi a kujerar dake pacing dinsa nace, “yaya ya kannaka” “yayisauki sosai maryamaaaa” yaja karshen sunan yana kallonta. Nima shiru nayi ina kallonsa gabadaya duk ya canza yayi wani iri,kamar baya cikin nutsuwarsa, inajindai ko tafiyar dazeyice bayaso dole aka masa.ajiyar zuciya sadiq yasauke tare da dauke kansa daga kallon maryam, wayarsa yazaro daga aljihu ya lalubu number aliya ya danna mata kira. Alama yayimun da hannu alamun nazo na karba, tasowa nayi ahankali na karba na koma mazaunina tare da kara wayar akunnena. “Hello, yasadiq tadawo?” Murmushi nayi me sauti nace, “ehh nadawo” daga daya bangaren aliya cikin farin ciki tace, “mairota, ykk ya gida ya school ya samari?” “Komai da kowa lafiya kalau, samari kuma seku manya ai” nabata amsa fuskata dauke da murmushi har lokacin. “Hmmm zama kifadi gaskiya, nasan yanzu kinyi baby’s irin ten dinnan a school idannazo zaki bani labarine” “nikuma sekace wata ke,dazanyi samari har 10, ya aunty?” Nakawar da wancan zancen da tambayar aunty. Aunty tananan klu, dafazamuzo muyiwa daddy sannu da zuwa to kuma munfara exam ne, sedai wani lokacin” “ohk, Allah ya kaimu, nifa ince nayi mamaki dabaku zoba naga anata zuwa gaishesa” “zamuzo nan kusa insha Allah” “Allah yakawoku lafiya” “ameen maryam, se anjima, zanyi karatune dama kira nayi naji ykk” “toh aliya nagode sosai kigaidamun da aunty pls” “zataji insha Allah, nima kigaidamun da nakarfen kafin nazo mugaisa” “Allah yashiryeki” nafadi haka ina dariya tare da kashe wayar. Mikawa yaya sadiq wayar nayi, daya tsaya kawai yana kallon maryam, ita batamasan yanayiba. Shiko ya kura mata ido yanda take magana cikin siririyar muryarta bakaramin kyau take kara masaba. Hira mukadanyi da yaya sadiq kadan akan makaranta, sannan mukayi sallama ya tafi, bayan yayi_yayi nafada masa menakeso yakawomun a tsaraba naki. Yauma a part din daddy zasuyi dinner, secan anjima zasu dawo. dakina nakoma nacigaba da
al’amurana.

A part din daddy kuwa, bayan maryam ta fita daddy ya juyo yana kallon mommy yace, “wai ko atika a ina kika samo wannan yarinyar?” “Meyafaru dear kake tambaya?” “Naganta batayi kalar yaran da’ake kawowa aikatau bane, kuma ni yanayin kallonta yanamun kamar nasan me irin kallon, kuma namijine” shiru mommy tayi cikin faduwar gaba, tabbas itama tadade tana kallon hakan agurin maryam din tun randa tafara ganinta, kuma ita tagane me irin kallon maryam din,amma bazata tunawa daddy ba danbataso ya tuna, yanzu seya ballo mata wani ruwan. Kuma abunda yake bawa mommy mamaki, kwata_kwata maryam bata kama da Wanda kallonnasu yake daya, amma yanda take dago idonta tana dan lumsheshi shima haka yake, musammanma dayana yaro, idan maryam tayi kallon se mommy taga tamkar shine dayana yaro. Numfashi ta sauke tace, “haba dear har akwai wani kallo nadaban da wani yakeyi,kallodai ai duk kallone, kawai kaikake ganin haka” kafin daddy yabawa mommy amsar maganarta mustapha ya shigo falon da sallama. Cikin tsantsar kulawa da kauna. suka amsa masa, zama yayi atsakiyarsu yana musu sannu da gida. Hular kansa yacire ya ajiye, dukta takura masa ga gajiya sosai ajikinsa. Tsokanarsa daddy yahauyi ganin yanda yaketa faman yamutsa fuska. Mommy kuwa kwantar dakansa tayi akan kafadarta tare da shafa lallausar sumar kansa. Cikin tattausan lafazi tace, “son ya taro da gajiyar biki” lumshe idonsa kawai yayi tare da daga mata kai alamar amsawa. Wayarsa dake hannunsa aketa kira, kindagawa yayi danyasan abokansane suke Neman caza masa kai, sunga basu gansaba. dan yanzuma sulalowa yayi ya gudo, da’ana zancen kai amarya, shikam baze iya wani kai amaryaba, sabgar mata ai ciwon kai zasu kara masa akan Wanda yake damunsa. Fahimtar da mommy tayi da gajiya atattareshi seta mike ta dakko masa ruwa da lemo me sanyi ta bashi yasha. Yakwaji sanyi aransa dandama da kishirwar atattare dashi. Mommy dakanta tayi masa tausa, tanayi tana jera masa sannu. Daddy kuwa nagefe yana kallonsu cike da ban sha’awa da burgewa, yanajin dadin yanda mommy take kula da mustapha yanda yakamata……….

washegari yaya sadiq asubanci yayi yatafi,hakan yasa bamu haduba. Drivern dayake dakkoni shine yakaini school yau. Duk senaji kewar yaya sadiq ta lullubeni, dama shi sabo haka yake. Yau laraba kwanan yaya sadiq biyu da tafiya, gaskiya nayi kewarshi sosai gidan duk badadi. A kwana biyunnan haidar yasakarmun fuska sosai, wani lokacinma idan muna zaune yayita jana da hira. Abunna matukar bani mamaki,haidar daya tsaneni sosai yanzu kuma shikemun haka. Bankawo komai arainaba na canzamun din dayayi. Suhailat ce dai jiya i yau, tamkarma kara mata tsanata akeyi. Yanzu kullum bayan magriba senaje gaida daddy har part dinsa bisa umarnin mommy, anannema nake ganin mustapha nake samun nutsuwa. Nadage ina karatu sosai saboda banaso nabawa yaya sadiq kunya. Yau tunda nadawo daga school naketa faman solving di maths da zee ta kara koyamun, danyanzu yafi bani wahala akan duka sauran subjects din da mukeyi. Alhamdulillah yanzu ina fuskantar turanci ba lefi, dan malamin lesson dina yadagemun sosai, kuma a school kwata_kwata ba’a Hausa se turanci shiyasa. Satina na uku kenan a school din, amma munyi text yakai 7. Gobe zamuyi ta maths din shiyasa na dukufa akanshi.

Bayan magriba ina zaune a falo ina kallo nikadaice duk suna part din daddy, tunda yadawo ba kullum suke zaman part dinba. Nima banjima da dawowa daga gaisheshiba. Jinayi kawai ansa hannu an rufemun ido, a matukar tsorace nafara kokarin banbare hannun, amma na kasa. Sedayaga dama dankansa sannan ya sakarmun idon yana dariya. Dasauri na juyo ina kallonsa, haidar ne. Ajiyar zuciya nasauke na juyar dakaina bance masa komaiba. Zagayowa yayi yazauna akusa dani yana fadin, “matsoraciya jibi yadda duk kikabi kika wani firgice se sauke numfashi kike” nibesanma haushi najiba, dominni tsoratanin dayayi bedameniba kamar tabamun fuska dayayi, duk senaji raina ya baci. Danne bacin raina nayi nace. “Ai dole In tsorata yaya haidar, bansan da shigowarkabafa kawai jinka nayi.” “Tom shikenan Allah yabaki hakuri yar kanwata” yafadi haka yana hade hannunsa guri daya alamar roko.????gyada masa kai kawai nayi, namaida hankalina akan kallon danakeyi. Jana ya shigayi da hira, nikuma ina kakkaucewa danse naji zuciyata bataso kasancewa dashiba. Ko fahimtar hakan yayi daga baya daya gaji dan kansa yatashi ya tafi. Nina matsuma gobe tayi yaya sadiq yadawo. Yau a part dinmu sukayi dinner, amma banda daddy da mustapha. A gurin serving dinnasuma haidar se magana yakemun ina basarwa,harda cewa nima nazauna naci abincin tare dasu mana nace masa aini nakoshi. Dasuka gamama ina wanke_wanke a kitchen seda yakara shigowa ya takuramun. Besan banason wannan kusancinnamu dashiba, dan haka kawai naji zuciyata bata yarda da wannan canjinnasaba.

Misalin karfe biyu na dare na tashi domin yin sallar nafila, ina toilet ina alwala naji kamar motsi adakina, dif nayi domin natabbatarwa. amma se naji shiru,cikin tsananin tsorata naja kafata ina sanda nafito zuciyata na dukan uku_uku. Dama kofar toilet din abude nabarta saboda bankunnan hasken dakinba, na toilet dinne kawai a kunne. Cikin dan hasken dake dakin, naga kamar gilmawar mutum yafita tare da jan kofa. Jikina har rawa yakeyi saboda tsoro, dama gani sarkin tsoron. hannuna na karkarwa na kunnan light din dakin haske ya gauraye. Bin dakin nahauyi da kallo cikin faduwar gaba, tabbas anshigomun daki, saboda wani irin kamshin turare Mara dadi danaji yana tashi adakin,bugun zuciyatane ya karu,saboda razani. la’ilaha’illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin nashiga maimaitawa araina ina tunkarar kofar dakin, inajan kofar kuwa ta bude, alamun babu key ajikinta,kuma ni nasan akulle nabarta. Wani matsanancin tsorone ya kara lullubeni addu’a nashiga karantowa a fili, jinake kamar na leka falon naga kowaye amma kuma tsananin tsoro yahanani lekawar..ahankali namaida kofar na rufe tare dasanya mata key. Zama nayi abakin gado hawaye na zuba daga idona, abun yazo kaina kenan. afili na fara magana. ya Allah kakareni daga dukkan me nufina da sharri , ya Allah kada kabawa koma waye damar ketamun haddi, Allah narokeka, Allah kakawomun dauki, acikin wannan al’amari kuka nafashe dashi meban tausayi, bantaba tsorata da abunda baaba talatu tacemun irinna yauba, takurewa nayi akan gado, tsoro da razani duk sun baibayeni, gani nakeyi tamkar mutumin zedawo. gashi bani dame taimakona a wannan Daren, idan mutumin dayawo, mommy yanzu a part din daddy take kwana daga ni se suhailat asaman yanzu. Kalaman innata data taba fadamun sune suka dawomun arai. maryam, wani baya karewa wani abunda Allah yakaddara seya samesa, duk abunda yasameki na kunci kona damuwa, kada kinemi taimakon kowa se Allah, shikadaine ze iya kareki daga sharrin me sharri, kisawa ranki Allah yana tare dake aduk inda kike, kuma shine zekareki akan komai, kikasance memikawa ALLAH kukanki daneman taimakonsa akodayaushe. wasu hawaye masu dumine suka shiga kwaranyomun saboda tunawa da innata. nadade a dunkule nikadai ina faman rera kuka da addu’a araina. Dakyardai na rarrashi zuciyata na mike nakoma toilet nasake dauro alwala nafito nasaka hijabina na tada sallah domin kaiwa Allah kukana. har ketowar alfijir ina gaban ubangiji,seda aka kira sallah natsagaita. zama nayi tare da rafka uban tagumi ina tunane_tunane, tunanin hanyar kawai dazanbar gidannan nakeyi,tunda ankawomun hari nafarko gobema za’a iya kawomun na biyu gwara kawai nabar gidan na huta. sallar da’aka tayarne yasani mikewa nabi limamamin nima. Bayan an idar na dakko alkur’ani me girma nashiga karantawa, izu biyu nayi nadakko addu’ar da aunty tabani itama na karanta. Seda gari yayi haske tangararau sannan na mike daga kan dadduma nafita nafara ayyukana. Jikina asanyaye yau nakeyin komai tamkar wacca kwai yafashewa aciki, kuku naganina yafara tambayata meke damuna ko banda lafiyane, babu komai kawai nace masa,danni yau maganaba banaso nikadai nasan halin da zuciyata take ciki nafargabar zaman gidannan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button