Uncategorized

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE

ABUNDA KA SHUKA COMPLETE HAUSA NOVEL

Daren yau gabadaya a wani irin yanayi nayishi, tunanin abunda yaya sadiq yafadamun yamun tsaye a zuciya. Ga kuma tsananin tsoro na abunda yafaru jiya, I najin tsoron karyauma a kara shigomun. Addu’a makamin mumini ita nakama inatayi afili da cikin zuciyata. Abunda yakara tadamun da hankali danazo serving dinsu na dinner babu yaya sadiq, da mommy ta tambayi su haidar sesukace yace bayajin dadine. Shiru naga mommy tayi bata kara cewa komaiba. Senaji duk babu dadi, yanzu akaina yaya sadiq ko abinci yakici, akaina ze shiga damuwa irin haka, gaskiya yakamata nayi tunani kada nazama me saka alkhairi da sharri. Nima kasa cin abincinnayi se sakawa da kwancewa nakeyi, idannayi tunanin amincewa yaya sadiq se kuma intuno badakalar daza’asha alokacin dazancen yafito. Karshedai na yanke shawarar zanyi shawara da zee gobe idan Allah yakaimu naje school. Baccina nayau rabi da rabine ga tsoro ga damuwa, danaga abun bana kare bane sena tashi na nahauyin sallar nafila………..

Washegari, kamar kodayaushe 7/30 nagama shirina, nasaba yaya sadiq kafin wannan time din yazo falo yana jirana, amma yau dana fito senaga wayam babushi. fita nayi koyana mota yana jirana amma nanma se driver nagani, yacemun tundazu yake jirana oga yace shize kaini. Hankalinafa idan yayi dubu yakara tashi, me yaya sadiq yake nufi, jikinnasane kokuma me? bani dame bani wadannan amsoshin seshi.

Da’aka fita break yau banfitaba, dama ni ba kullum nake fitaba, balle yau danake cikin damuwa. Su zee dai sun fita. bata jimaba ta dawo ita kadai. Zama tayi agefena tace, “maryam Ahmad lafiya, yau naganki sukuku dake, kodai jikinnakine.?” Girgiza mata kai nayi alamun a’a sannan nace, “zee yau wata matsalace dani nake Neman shawararki amma dan Allah inaso abun yazama sirri tsakanina dake.” Cikin mamaki zee take duban maryam, tace. “Matsala kuma maryam wacce iri” numfashi nasauke. “nabawa zee labarin abunda yake faruwa atakaice.” Cike da tsantsar mamaki zee take kallon maryam, domin bata taba tunanin maryam aiki takeyi agidan alh menasaraba. dan batayi kala da masu aikiba. Gyara zama zee tayi tare da dafa kafadar maryam tace, “kamar yadda kikafadamun sadiq ya miki abubuwa arayuwa na alkhairi yakamata kema kisaka masa da alkhairi. Kicire tunanin wai mahaifiayarsa ko yan’uwansa baza susokiba, wannan duk ba matsala bace, domin badasu zaki zaunaba, kuma babu wanda ya isa yahana abunda Allah yarubuta faruwa, duk bala’i da masifar mutum kuwa,idan Allah yayi ke matarsace babu Wanda ya isa ya hana. Maryam zanbaki shawara wadda nasan zakiji dadinta, bazan taba fada miki abunda ze cutar dakeba, danko nice bakebama haka zanyi. Ki amshi soyayyar yaya sadiq hannu, bibbiyu natabbata bazakiyi danasaniba nangaba. Yaya sadiq yakai asoshi, gashi kyakkyawa, ga kirki ga saukin hali, gadai abubuwa na qualities dayawa yana dashi wanda kowacce mace zataso mijinta yakasance haka. Kuma koda yanzu bakyajin sonsa azuciyarki nangaba zaki sosa. Yarinya kisaki jiki kawai Ku kwashi romon soyayya, gashi kun bala’in dacewa dashi kuwa” takarashe zancen da murmushi a fuskarta. Shiru nayi ina juya maganganunta araina, tabbas duk abunda zee tafada gaskiyane, kuma insha Allah zanyi amfani da shawararta duk da haryanzu wani bari na zuciyata cike yake da tsoron yau nice da soyayya, nida banmasan menene sonba, balle harna iya wata soyayya. Ajiyar zuciya nasauke nace, “nagode sosai kawata, Allah yabarmu tare insha Allahu zanyi amfani da shawararki.” “Yawwa tawan kokefa, Allah ya kade muku fitina da sharrin shedan atsakaninku yakuma tabbatar mana da alkhairi musha biki” ta fadi haka tana rungumoni ajikinta. “Ameen” nafada cikin jin kunya. “Inyeee, yanmata masoya harna hangoki kinawa yaya sadiq kallon luv, dan wannan idanunnaki masu kyau nasan zasu bada wuta wajen kara hargitsashi.” Zee tafadi haka cikin shakiyanci. Dariya namata kawai cikin jin dadi, senaji tamkar ansauken wani katon dutse daga kirjina, duk senaji na matsu a tashi injewa yaya sadiq dina da daddadan albishir. Amma duk wannan abun dake faruwa daga jiya zuwa yau, tunanin yaya mustapha nanan daram araina kamar kodayaushe, amaimakon idanuna su dinga haskomun hoton yaya sadiq senashi kawai nake gani. “Wannan bawan Allah, bansan sanda zandena tunaninshiba, tare dajin faduwar gaba idan na tunoshi” nafadi haka araina ina lumshe ido????????……….

Yau din senajita wata tadaban arayuwata inajin tamkar ancanzani. Ina dawowa gida natarar da yaya sadiq shikadai a falon mommy, da alama beje office ba. Wata sassanyar ajiyar zuciya nasauke na shiga falon da sallama. Sadiq dake kwance akan kujera 3 star tunanin maryam yahanashi sukuni, daga yammacin jiya zuwa yanzu dabe gantaba gaba daya yakasa samun nutsuwa. Amsa mata yayi yana binta da kallo, duk yanda yaso dauke idonsa daga ganta amma yakasa,wani garin ciki yaji sanda yaganta ajiyar zuciyarsa yahausaukewa akai akai dama dawowar tata yake jira. Nikuwa ganin yaya sadiq yana kallonta senayi kasa da kaina cikin jin kunya, zuciyata na bugawa. Ahankali nakarasa garesa naxauna aka can carpet nace, “yaya sadiq sannu da gida yajikinnaka” “dasauki maryam ya makarantar?” Yafadi haka yana tashi zaune, cikin sanyin murya me tattare da damuwa. “Alhamdulillah” daganan nayi shiru ina wasa da yanyatsun hannuna, nama rasa ta ina zanfara masa maganar, kalmomun bakina duk sun gudu. Fahimtar hakan sadiq yayi yace, “maryam kamar da magana abakinki ina fatandai lafiya ko” tattaro duk wata nutsuwata da juriyata nayi na daure nace, “yaya sadiq na’amince da soyayyarka.” Nafadi haka cikin rawar murya. farincikin da sadiq yaji alokacin da maryam tafadi haka baze misaltuba, hannu yadaga sama yace, “Alhamdulillah” har sau uku. Fuskarsa dauke da fara’a bakinsa yaki rufuwa,betaba tunanin zata amince masa haka da wuriba,tsareta yayi da idanunsa cikin tsananin farin ciki,yakasa dauke idonsa daga ganta. Mikewa nayi da sauri nafara tafiya cikin sassarfa saboda matsananciyar kunyarsa data lullubeni. “Kije ki shirya, kifito zamuyi magana” natsinkayi muryar yayasadiq yana fadar haka, banjuyoba nidai nashige daki. Tsayawa nayi ajikin kofa ina sauke numfashi tamkar wadda tayi tseren gudu, gani nakeyi kamar nayi gaggawar amincewa yaya sadiq, amma idannatuna kalaman zee se inji hankalina ya kwanta.nadade atsaye ina jimantawa kaina, dakyar naja jiki nashiga toilet na watsa ruwa tare da dauro alwala nafito natada sallah. Ina sallah tunanin tsarabar yaya sadiq ta fadomum arai, aiko ina idarwa na dakko ledar na bude danganin menene aciki. Waro idona nayi waje duka saboda abunda nafara tozali dashi, wayar hannuce kirar android yar madaidaiciya. Bansan takan wayaba balle nasan matsayinta kawaidai tun a jikin kwalin naga anrubuta Samsung ajikin wayarma haka. Ajiyeta nayi agefe, domin gaskiya mayar masa da wayar zanyi, abun yayi yawa dawainiyar tayi yawa gaskiya. Se abu nabiyu dana gani agoguna guda 6 na karfe masu matukar kyau da daukar ido. Gaskiya na jinjinawa yaya sadiq a wajen kyauta, shiko gajiya bayayi nihar kunyar amsar abu nakeyi ahannunsa. Wata takardace ta karshe anannade, se tashin kamshi takeyi. warwarewa nayi naga rubutune amma typed akayi. Gyara zama nayi nafara karantawa kamar haka:

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button