KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Dady zaune a d’akinsa byn yayi wanka ya sauya kaya zuwa jallabiya ya jima zaune yana tunanin rayuwa kawai yana Jin ciwon abinda tanweer take aganinsa hakuri ya dace tayi .
ya mike da kyar ya goya hannuwansa duka abaya yasan babu tantana wannan yaron da take zuwa gurinsa yana ta’bata .
mace akan jijiya babu abinda bazata iya yi ba tunda taji dadinsa da matukar wahala ta iya rabuwa dashi sai ya tashi tsaye yayi amfani da karfnsa da kudinsa da matsayin kujerar mulkinsa .
ya runtse idanunshi “duk fa zunubinsa ne ya kare akan tilon yarsa haka rayuwa take shine wanda yake cin mata a office ,Shine yaci a hotel hotel ,shine yaci a mota Kuma duk yara kanana brain dinsa ta hasko masa fuskar Hibbat yarinyar yar kimani shekara sha takwas a duniya a mota yayi yayin cinta a car park yawon zuwan da yake gurinta Kuma duk sanda yaje sai ya ci yake komawa gida mutane dake gurin suka fahimci haka wata rana Yana tsaka da yi suka zo suka tsaya ajikin motarsa suna buga kofa.
yayi saurin tashi akan hibbat Yana Maida wondonsa ai kuwa suka taru ajikin motarsa har sai daya fito gashi babban mutun ga hibbat yarinya karama siririya doguwa kyakkyawa jinin saurata .
nan fa suka haushi da fad’a taya kamarsa zai dinga irin wannan rayuwar da yar cikinsa case har gurin sarkin agege , ganin shi din babban mutun ne ga Kuma yarinyar diyarsu ce idan ma suka ce zasu daga maganr cikinsu zatayo kamar sun tonawa kansu da sarautarsu asiri ne yasa aka bar maganar Amman fa duk da hakan bai sa ya rabu daita ba suna haduwa daita akan titi depomu express ya d’auketa suje hotel yayi yadda yake so daita idan kuwa yayi tafiya zuwa Abuja ko Kaduna shikenan kofar sikanci ya bud’e sai a hada masa yammata uku alokaci daya yaci wannan ya gama yaci wannan haka yayi ta rayuwarsa sai gashi sanadiyyar iskancinsa ya janyowa yarsa ” .
“me yasa nayita zina da ya’yan mutane gashin abun ya dawo kaina ..?”
Yana cikin zagaye d’akin wayarsa ta soma ringing naunayen ajiyar zuciya ya sauke yaje ya d’auka yana dubawa ,number ne kawai babu suna har zai ajiye wayar sbd bai daukar number da babu suna sai kuma ya fasa ya dauka tare da yin shiru “hello aka fada daga daukar wayarsa shima hello yace “alhaji ili ne.
“okay ili ya kake ?”Lafiya alhj kwana biyu banga kiranka ba shine nace na kiraka muyi bakin mata daga kano gasky akwai daya dana tana da maka zaka ji dadinta “ili ai tunda kaga bana kiranka ai kasan akwai damuwa yanzu dai magana ta kare dan a yanzu bana cikin kwanciyar hankali sakamakon abinda na dade Ina yi a boye ya shafi dilon diyata dan haka zina ta fita araina daga yau karka Kara kirana akan mata yana gama fad’ar haka ya katse Kiran tare da juyowa bayansa Ido hud’u sukayi da mumy ..”
Kallon mamaki ta dinga binsa dashi tamkar bata san shi ba bancin da kunuwanta taji yana maganar da tace karya ne idan wani ne ya fad’a mata .
Hawaye suka shiga zubo mata shi Kuwa gabansa ne ya dinga faduwa ,ya dinga Karanto Kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun wani irin zufa ke tsatsafo masa bisa goshinsa kamar an watsa masa ruwa .
gbdy sukayi sit na tsawon mintoci daga shi har ita shi tashin hankali ya hanashi magana ita Kuma mamaki ne ,mumy dake zubar da hawaye bai yi auni ba yaga ta zube kasa ta zauna dabas tana cigaba da kallonsa yayi saurin yayo kanta zai ta’ba tayi saurin dakatar dashi da hannunta “karka tabani Allah sarki tanweer ashe ubanki ne yayi silar jefa rayuwarki cikin kunci hakika ka cutar da tilon diyarka, ni Kuma ka yaudareni ta fad’a tana goge hawayenta kana ta numfasa ta cigaba da mgn ” na kan zauna ina tunani me yasa abubuwa suke faruwa damu haka ashe da walakin kuskurenka ne ya shafita bata ji bata gani ba kaga rayuwa ko ?”Kai din ba barowa ba ,ba mahainci ba duk wanda yaganka yaga responsible man amman Kalli ta inda Allah yayiwa ya’yan mutane sakayya dan fashi yazo har gidanka ya saci kudinka sannan ya tafi da diyarka ya kwana daita ta kamu da mutuwar sonshi saboda ba’a cin bashin Allah akwana Lafiya ,wallahi da wani ya fad’a min cewar kana neman mata bazan yarda ba sai gashi da bakinka wallahi abban tanweer kabani mamaki kullum yabonka nake ashe kai din ba kowa bane sai fasa gurbi acikin mutane nayi danasanin aurenka.
” ka taba fad’a min zaka kara aure na hanaka bare kace shine hujjar bata ya’yan mutane?”
“wallahi a yanzu na daina ganin laifin tanweer dan haka ni zan goyawa tanweer baya ta auri wanda take so ,ta fad’a yaron ya fito suyi aure a wuce gurin kowa ya huta, haka Allah ya so da rayuwarta nata qaddarar kenan.
dady ya sauke numfashi sukayi zugun kafin a hankali yace “bazan yarda ba, bazan bawa dan fashin da kasa ke nemansa Ido rufe diyata ba , bazan iya wnnan kwamacalar ba .”
ta mike tsaye da kyar ta karaso gabansa ta buga table dake d’akin wanda takardunsa da system dinsa ne Akai tace “haka nan zaka hakura da abinda take so , zan fada mata da kaina cewar kace ya turo iyayensa idan Kuma kaki bakaki gani ba domin masu irin halinka suna nan cike a agarin nan.”
zuwa yanzu gbdy jikin dady tsuma yake kanshi yaji yana jujjuyawa dashi saboda tashin hankali “wallahi ka cuceni ban taba hanaka aure ba amman kake neman mata tana gama fadar haka ta fice daga d’akin ya biyota da sauri yana kiran sunanta “zainab karki soma wannan dayen aiki “zan yi domin wannan shine hukuncin dayafi dace wa da kai ,data dinga binsa yaje ya sake yi mata wani cikin gara ta auresa tunda taji ta gani tana sonshi “karki min haka zainab arayuwa kinsan Ina matukar sonki fiyye da kowa da komai a duniya ban taba tunanin idan kinji abinda na aikata zaki yanke wannan hukuncin akaina ba.
na duara burin duniya akan diyta zata auri mijin da zatai alfahari koda bata auri Ibrahim ba dan haka kar muyi haka dake….”
” zamuyi koma nace muyi data zubar mana da mutunci kmr yadda kake yi a waje Allah gara ta aureshi ai shiriya ta Allah ce sai kaga ya shiryu a sanadiyyarta “bafa zan yarda ba, tanweer diyata ce “please ka fitar min a daki kana damuna da surutun banza,kai bana ma son ganinka kuma kasan allah babu wanda ya isa ya hana aure nan “.
da misalin karfe shida na yammacin rana
Suka fito cikin shiga iri daya sai dai kalar kowannensu dabam sannan kowannensu goye da school bag kawai jaguwa ne kawai mai akwati wanda yake dauke da kayan aiki da school bag idan ka gansu zaka dauka yan wasan kwalo ne saboda irin shigarsu sukayi suka shiga mota daya scopio yajasu suka bar gidan .
kai tsaye airport suka nufa koda suka isa jirgi ya kusan tasshi daman kuma suna sane suka fito late dan su samu damar wucewa da makamansu
da dan sauri suka isa reciption suka Mika body fast dinsu nan maiakatan wajen sukace sunyi lattin jirgi ya kusan tashi .
daya daga cikin maakatan gurin ya tashi kasancewar yasan jaguwa adalilin tafiye tafiyen da yake ,ya karbi akwatin jaguwa suka nufin filin jirgi cikin sauri ya karbi lebet a hannu wani ya manna a akwatin aka sakashi acikin kagon jirgi sannan suka shiga kowannensu ya nemi set dinsa .