KUSKUREN BAYA 1 TO 48
Jaguwa ya gyara tsayuwa yana shafa qirjinsa da hannu d’aya sannan yana jin bayani amminsa daki daki akan matar data samo masa ,”ammi ki bar maganar wata hasera a yanzu , zanyi k’okari na kawo miki wacce zan aura “.ya fadi hakan ne ba dan zai Kai mata din ba sai dan ta rabashi da batun wata hasera .
a bangaren ammi ta katse shi da sauri “lokaci ya kure maka bazan sake baka wata dama ba dan naga alamun zuciyarka bata shirya amsar soyayyar kowace mace ba ,gara ni na shirya maka ga hasera nan ita zuciyata ta zaba maka Kuma ita zaka aura muddin Ina raye idan Kuma bujirewa zabina zakayi to sai ka sanar min ? “. Shiru yayi
tare da lumshe idanunshi a tsayen da yake dan amminsa ta rigada ta gama d’aure shi da maganarta “kayi shiru ko bazaka bi zabina bane nasani ? “
“Ban Isa ba ammi ,ban Isa naki bin zabinki ba amman ki canza min da wata ban da hasera” ya fad’a yana Jin wani sabon tashin hankali ya kusanto rayuwarsa “Amman Kaine kace duk wacce na zaba maka baka da ja ?sun d’auki tsawon lokaci suna tautaunawa a karshe yace ta bar maganar idan ya shigo karshen sati zasu sake tautaunawa akai “.
Bayan ya gama waya da ammi ya boye number ya kira mahaifin tanweer magana biyu yayi masa ya katse Kiran sannan ya kira number baba yana sheida masa zai maida tanweer gobe “bana ce maka karka kuskura ka maida yarinyar nan ba ?
“wannan yarinyar da kake tare daita a gidanka karka yarda ka rabu daita ko ka yarda ta matsa a kusa da Kai kmr yadda na fad’a maka a watanni da suka gabata ,
abinda bakasani ba ajikinta akwai taurari masu haske da karfin da zasuyi maka amfani akan aikinka ka barta a karkashika karka yarda ta bar karkashinka “.
“shiru jaguwa yayi yana tunanin abinda yake ta fad’a masa kenan kafin daga baya ya soma magana a sanyaye “bazan iya cutar daita ba sannan bazan iya amfani da taurarinta ba, idan da hali na zauna a yadda nake.
na samu duk abinda nake nema batare danayi amfani da taurarin kowa ba..”.
“Wannan yarinyar dabam ce km ko ba yanzu ba dole zaka bukaci me irin taurarinta sai dai ba lallai ka samu ba dan haka ka barta kayi amfani da taurarinta .” bazan iya cigaba da zama da…..”
“to ka aureta domin ta kasance a karkashin ikonka abinda ake so dai ta zauna tare da Kai “.
“Aure Kuma baba ?”
Mmn sudais
Mmn sudais????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN domin sauraron littafaina a tuntubi channel dina ta hausa bakwai .
????️ 21
“Eh ! abinda nake nufi Kenan kuma nake bukata ka aikata, muddin wannan yarinyar bazata kasance karuwarka ba to ya zama lallai ka aureta Kuma acikin tsakankanin wannan lokacin “.
Cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya jaguwa yace ” me yasa baba ? “mai yasa baza’a bar wannan maganar ba dan Allah ? ” ni dai gsky a biyo wata hanyar banda wannan, tanwer tasan koni waye , tasan sana’ata fashi ne , nayi Imani Koda na fada mata zan aurenta bazata aureni da wannan sana’ar ba ya k’arasa maganar tare da yin shiru yana tunanin zuci “shi dai gaskiya komai za’a yi bazai taba auren tanwer da wata manufar ba ko cutar daita ba domin yana jinta ajikinsa tamkar jininsa .”
Shiru ne ya biyo baya na wasu mintuna kafin daga bisani baba ya numfasa kana ya soma magana a dake “Hanya daya ce zata maye maka wannan gurbin , ka nemi mace mai irin taurarinta ka ajiyeta akarkashin ikonka Koda bazaka aureta ba ka dinga saduwa daita saduwa irin ta aure idan kayi haka shikenan komai zai cigaba da tafiyar mana yadda muke so batare da wata matsala ba .”
“shiru jaguwa yayi yana kallon zara zaran yatsun kafafunsa masu tsananin kyau da sheki yana nazarin maganar baba, nan take gumi ya shiga tsatsafo masa a dukkanin ilahirin jikinsa, kwakwaluwarsa ta toshe zuciyarsa ta cunkushe guri daya , tunanin da yake ya tsaya cak ya Kasa cigaba da tunanin komai . sai daya dauki minti biyar tsaye batare da yasan madafar dafawa ba “amincewa auren tanwer Ko nemo mai irin taurarinta ya ajiyeta akarkashin ya dinga aikata zina daita “shi da yake neman yakice zina arayuwarsa sai ga baba na kokarin maidashi ruwa tsundum.
“Ya amince ne ko kuma ya fada masa a sake nemo wata mufutar ? sautin muryar baba ne ya dawo dashi cikin hankalinsa ta Inda ya cigaba da zayyano masa hujojinsa akan bukatar auren tanwer da yake son yayi Ko kuma ya shiga gari ya nemo mace me irin taurarinta idan ba haka ba nan gaba kadan za’a yi galaba akansa ” .
duk abinda baba ya fada yasan yana da huja akan hakan kuma yasan ya fada ne domin ingata rayuwarsa daga sana’ar fashin da yake but shi baya jin zai iya ajiye tanwer a matsayin karuwarsa Ko aurenta domin samun wani biyan bukata daga gareta “. ya runtse idanunshi yana mai sake gyara tsayuwarsa yana jujuya maganganun baba yana sake fadadasu yana masu filla filla , gbdy komai ya tsaya masa.
ya sake neman natsuwarsa ya rasa , ji yake Kamar zuciyarsa zata buga tsabar shiga rud’ani tunanin matsalar dcp ,tanwer ,
Amminsa , yanzu Kuma ga matsalar baba da me zai ji?
“me ya kamata yayi ya samar ma zuciyarsa salama ? yana jin kamar yace babu abinda zai yi acikin umarnin baba wanda wannan shine Karo na farko da zai sabawa umarninsa a tun tsawon lokacin da suka dauka tare dan bai taba cewa ga abinda zaiyi ya mutsanta masa ba sai dai ya aiwatar . “
“tun yanzu ka fara tunanin shiga gari domin nemo me irin taurarin yarinyar nan ka ajiyeyata a matsayin karuwarka dan nasan bazaka taba aurenta ba tunda baka amince da auren yarinyar nan ba .”
Juya maganar baba yaketa faman yi acikin kwa kwaluwarsa , zuciyarsa ta dunkule guri daya yana jin Kamar ya daura hannu akanshi ya saka ihu ko yaji saukin zafin da zuciyarsa ke masa sai daya sanyawa jikinsa jarumta sannan yace “wacce irin alama ce zatasa na gane me irin taurarin tanwer ?
“Kenan kafin bukatar wata akan wannan yarinyar ?
“bazan iya cutar daita bane ” ya fada yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa, shiru baba yayi kafin daga bisani ya numfasa sannan ya cigaba da mgn “alamar da zaka gane me irin taurarinta , kana ganinta duk wata kafa ta gashi dake kwance ajikinka zata mike, take wannan zoben dake hannunka zai yi baki, abu na gaba tsuntsun dake ajiye a gidanka zai bayyana akanta wannan shine alamar me irin taurarinta amman fa bai zama lallai ka samu ba.”
“zan samu …..” ina samun nasara akan komai dana saka gaba wannan Karon ma nasan zanyi nasara da yarda Allah “Ina maka fatan alkhairi da fatan samun nasara yana gama fadar haka yayi disconnecting din Kiran , jaguwa ya cigaba da tsayuwa agurun tare da lulu duniyar tunanin .”