KUSKUREN BAYA 1 TO 48
“Matsalar Kenan Duk kwanakin da zarar ana magana zaka fara Kawo batun mutuwa ,zamu mutu amman ba yanzu ba anas ya bud’e baki zai yi mgn jaguwa yace “kaga malam karka ce komai ga sauran kazar da nacan na rage maka kaci kaji dadinka ya juya zai shige bedroom dinsa Anas ya rikoshi ya marairaice.
” dan Allah Adnan kayi hakuri ka lallaba yarinyar nan ta zubar da cikin ta dadin rai ,yadda kake mata din nan zai bugar mata da zuciya tana bukatar rarrashi da kulawa , jaguwa yay masa wani irin kallo mai hargitsa kayan ciki “dan Allah ba dan ita ba .”
Ya numfasa kana yace” naji zan kiranta “yauwa to Ko kai fa dan Allah ka lallaba ta kaji abokina. Baice komai ba ya wuce zuwa uwar dakansa ya hau kan katifa ya kwanta ya janyo blanket ya rufe rabin jikinsa sannan ya lalubo wayarsa ya ya fara neman layinta kira d’aya ta d’auka qirjinta na buga da sauri sauri tsayawa tayi batare da tace komai ba shima shiru yayi na kusan minti goma yana sauke mata numfashinsa a kunne kafin daga bisani yace “hello ..!
Shiru tayi tare da kasa kunne tana jin zazzakar muryarya mai kashe jiki ,a hankali ta dinga jin wasu abubuwa na yawo ajikinta cikin zazzakar muryarsa yace “ya kike ?”a hankali ta bud’e bakinta “yanzu Adnan ka kyauta min Kenan ? lafiya muka rabu da kai fa,a tunanina kira d’aya idan kagani da kowacce number zaka biyo Kiran a tunaninka ko nice amman sai kayi watsi dani.
cikin murmushin yace “kiyi hakuri yanzu ya kike jin jikinki “.
gumin dake tsatsafo mata a bisa goshinta ta goge tana sauke numfashi hade da cewa “gani nan dai sai hankali wahala nake sha gashi kace a zubar da cikin saboda baka qaunata sai dai ni bazan zubar ba ina son abuna ..”
Naunayyen ajiyar zuciya ya sauke da karfi ya kamo lips dinsa na Kasa yana cizawa a hankali yana yabi yatsun hannunsa da kallo dan tunanin Kalmar da zai mata amfani daita gurin lallabata “kace Baka bukatar cikin Ko”?
Shiru yayi na tsawon minti goma kana a hankali ya fesar da numfashi ya kwantar da murya “ba wai bana son cikin bane matsala zai zame mana arayuwa bare ke da kike matsayin mace “ni dai gsky Ina son kayana “a hankali ya d’aura tafin hannunsa a goshinsa ya dafe tare da lumshe idanunshi cike da kulawa yace “nima Ina son abuna amman kiyi hakuri acire zamu samu wasu nan gaba.
“Da gaske kake ?”
Yayi shiru yana cigaba da cizan lips dinsa .
A hankali ta Kira sunansa “Adnan !”a hankali ya motsa lips dinsa “na’am tan .”ka tabbatar zamu samu wasu ? da kyar ya fixgo mgn “eh idan kika bi umarnina kika cire ba ya k’arasa maganar yana shafa sumar kanshi “tunda muka rabu ban kara samu sukuni ko walwala ba har mamakin kaina nake kullum cikin damuwar soyayyarka nake da zazzabin cikin nan bana wani cin abincin kirki gashi Kowa ya gane halin da nake ciki a gida “.
“oh my god tanwer me yasa kikayi haka me yasa kika bari suka sani ?
“saboda ina qaunarka ta k’arasa maganar kmr zatayi kuka ..
Qirjinsa yayi masa nauyi tausayinta ya lullubesa duk da bai son yawon surutu amman haka yayi shiru yana biye mata “gsky banso kika sanar dasu ba “to yazanyi da rayuwata dole ce . ya dunkule hannunsa sosai yaji ya Shiga damuwa” ina sonka Adnan Allah idan bakayi wani abu ba tunanika zai kasheni “
ki daina yawon tunanina .
tace “bazai Yiwu ba yanzu ma Na fara idan kaga na rage tunaninka to ina gidanka ne “
“Ki rage yawon tunsni yana kisa ,dan Allah kiyi kokari kije asibiti gobe acire cikin nan sannan su rubuta miki magani. “nifa bazan zubar ba .
Ki yi abinda nace shine kwanciyar hankalina sun dade suna magana akan ciki duk yadda yayi daita taki amince masa da zata cire cikin, wanda ita a zuciyarta tuni ma ta yarda kuma ta amince ma zuciyarta zata cire ta hutawa ranta tunda shima bai so amman bazata yarda ta bari yasan zata cire ba sai ta d’aga masa hankali.
“ki kwanta ki huta zan Kiraki zuwa gobe amman ki tabbatar kin amincewa ranki zaki cire “
Tace “to !
“karkiyi tunani komai kinji “
ta sake cewa ” to ! ta fad’a tana jin zafi aranta saboda gbdy ta gano rashin sonta da bai mata sai tana jinshi ya katse Kira .”
zuciyarta ta kasa samu natsuwar tunanin daya gargade shi ta cigaba da yi, bata da burin da wuce ta mallakesa a matsayin mijin aurenta , tunani kala kala tayi ta saka wancan ta kwance har ta shigo tunanin rayuwar da sukayi agidansa a farkon zuwanta suna lullube dashi cikin bargo d’aya babu kaya ajikinsu tana makale a gefensa yayinda hannunta d’aya Ke Saman faffadan qirjinsa shi kuma yana shafa sansar jikinta tare da sarrafa albarkatun qirjinta nan take tsigar jikinta suka tai mikewa ,ta dinga jinsa ajikinta a hankali jikinta ya kama kyarma ta kankame jikinta guri daya tana jin kamar jijiyarsa na shiga jikinta ,yayinda taji tafukan hannunsa na yawo sansar jikinta da wannan tunanin bacci barawo ya dauketa .”
Washegari da misalin karfe biyar da rabi ta farka had’e da yin mika , jiki a sanyaye ta sauko daga kan gadonta tashiga bathroom tayi alwala ta fito ta gabatar da Sallah byn ta Idar bata tashi ba ta kwanta akan sallaya tana azkar tana kuka har ta gama ta kama addua “rabbi Inni Lima Anzalta Ilaiya min khairin faqeer ta dade kwance tana tunani da fargaban zafin cire ciki ahankali baci ya dauketa sai gurin karfe goma ta farka ta mike tare da nade dadduma Sallah ta shiga bathroom tayi wanka ta fito ta shirya ta nufi d’akin mumy anan ta samu mumy har dasu uncle bashir byn ta gaishesu ta gaishe da mumy sannan ta roketa tare da bata hakurin damuwar da ta sakata jiya, sannan Kuma ta tabbatar mata Da ta amince a cire cikin .
nan take mumy taji ta warke daga ciwonta ta ji jikinta ya dawo normal damuwa ta bar gangar jikinta sai faman saka mata albarka take “inshaallah sai Allah ya yaye Miki abinda kike ji akan dan iskan mutumin nan ,
Allah ya yaye miki gbdy suka amsa da” ameen”.
cike da farinciki suka dauketa zuwa babba asibitin kudi batare da bata lokaci ba suka Samu ganin likita suka fad’a masa taimakon da zai musu ,dake yasan minister bai tsaya bata musu lokaci ba yayi mata gwaje gwaje dan ya gano cikin Ko na wata Nawa ne dan yasan me za’a mata ganin karamin ne yace “za’a Iya bata kwaya tasha amman fur dady yace a’a ayi mata abortion Kawai zaifi samun natsuwa , dan haka batare da bata lokaci ba aka Shiga daita Wani d’aki .
ta sha wahala sosai Kamar zata mutu har aka gama kuka take tana Kiran “wayyo Allah zan mutu nurse ta d’auki sama da minti talatin tana aikinta bayan an gama nurse ta fito ta barta ta dan huta .
byn kmr awa d’aya ta fito tana d’aga kafa da kyar tana jin jikinta kmr ba nata ba sai dai ta daina jin nauyin da jikinta yayi mata amman kallo d’aya zaka mata ka tausaya mata dan taji jiki sosai , duk tayi wuri wuri Kamar wacce tayi shekara tana ciwo.
sai dai ciwon bai kai zafin rashin son da jaguwa yake mata ba office din doctor ta shiga inda ta iske su dady zaman jiranta doctor ya rubuta mata magugunan da zasu taimaka mata sannan suka dawo gida .
Kai tsaye d’akinta suka nufa daita suka kwantar daita akan gado suka zagayeta suna mata Sannu “doctor yace abata ruwan zafi ta sha kafin ta sha magani inji cewar uncle Jamil.
mumy najin haka ta mike da sauri ta fita ta shiga kitchen da Kanta ta dafa mata ruwan zafi ta juyo a cup ta dawo d’akin “Tashi ki sha kinji tanwer dina ,tan ta soma k’okarin mikewa uncle bashir ya taimaka mata ta zauna tana fidda zazzafan numfashi ya janyo pillow ya saka mata abayanta ya jinginata yana mata “Sannu!”
Mumy ta mika mata cup din ruwan zafi tana sake mata “Sannu”! tanweer ta gyada mata kai Kawai dan ita kad’ai tasan ciwon da zuciyarta ke mata .
a hankali ta dinga kurban ruwan zafin ,kadan ta sha tana k’okarin mikawa mumy cup, ta miko mata magani ta karba ta sha da kyar ta mika mata cup ta koma ta kwanta lamo had’e da kunna wayarta dan tun safe a kashe take ta tura karkashin pillow .
Ko minti biyar batayi da kunna wayar ba,ta soma babriting alamun ana Kira ta lalubo tana duba screen din wayar number jaguwa ne dan haka ta maida wayar inda ta dauko batare data dauka ba ta runtse idanunta sai ga hawaye masu zafin gaske wanda take jin zafinsu har cikin jikinta .
“ya kiranta yanzu saboda yana bukatar ta zubar da ciki amman ita kira nawa tayi masa bai d’auka ba ?”tana jin Kira na sake shigowa wayar amman taki d’auka “ciwon abun taji sosai bata san meye matsala arayuwarta ba sai da qaddara ta hadasu ,wani Kiran ne ya shigo aranta tace “duk ka gama kiranka bazan dauka ba sai na ganar da kai kuskurenka .
Ahankali duk suka watse suka barta a d’aki ranar yini sukai cikin farinciki bini bini sun shigo dakin dubata har dady yayinda wuni jaguwa yayi yana Kiran number tanwer amman taki d’auka a karshe ma ta kashe wayar gbdy.”
Haka yayita damunta da kira acikin kwanan biyu ya hanata sakat da batun zubar da ciki ita kuma taki yarda ta fad’a masa ta zubar tun su mumy basu fahimci mai Kiran ba har suka zo suka fahimta haushi kamar ya kashesu ganin tana sauraronsa.