KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

  mik’ewa yai ya  bar da’kin ya fito haraban gidan yana taku tamkar wani zaki ,  jiki a sanyaye ya shiga motarsa  kai tsaye m.s  fast food ya nufa , yai order abinci da abun sha  mintuna  kaɗan  aka  haɗa masa komai daya bukata aka mika masa farar laida  ya dawo  gida  ya zaro key  ya bude d’akin  ya tura kofa a natse   ya  shiga  ,tana ganin  a buɗe kofar ta zabura  ta mike jikinta na karkarwa  ganinsa yasa ta sauke wani wahalallen numfashi .

  ya maida kofar ya rufe ya k’arasa shigowa d’akin sosai , bai kalli inda take ba ya ajiye laidar   hannunsa akan table ya  soma balle mabalin  tigarsa  ya zare, whit singlet d’insa ya bayyana da gajeren wando iya cinya   duk da bata ga kwantaccen sumar gashin  dake kwance a qirjinsa ba tana iya  hango kan nipple’s dinsa dake tsaye ga  santala santalan cinyoyinsa a bayyane  gabad’aya jikinsa kwance yake da laulausan gashi mai tsuma zuciya wani irin shaukin sonsa ke fixgarta , kallon inda take yayi take  idanunsu suka tsarke cikin juna, wani irin abu suka  dinga fitowa daga kwayar idanunshi suna shiga nata masu wuyar misaltuwa ,
kusan minti uku suna kallon juna batare da sunyi magana ba , sai itace tayi karfin halin yin  mgn “ina ka baro matarka ? banza yayi mata ya soma takowa   zuwa  inda take rigingine tana binsa da idanunta, ganin yadda yayi mata banza yasa ta juya  ta kwanta haɗe da  juya masa baya  tana matso ruwan  hawaye.

A hankali ya k’araso idanunshi na kanta yana karewa halittar jikinta kallo   “Ki tashi kici abinci girgiza masa kanta tai alamar bata ci ,saman gadon ya hau yasa hannunsa ya taɓa wuyanta zafi ne ya ziyarci tafin hannunsa  “oh my god your body is hot are you still sick ? ya tambayeta   girgiza masa kai ta sake yi  , matsota yayi sosai  tashi muje  hospital  ina son sani meke damunki ya fadi haka batare daya tashi faɗa ba   “karka damu idan na koma gida i will be alright   “okay tashi kici abinci  ya sake kai hannunsa jikinta yana  shafa wuyanta taushi da dumin hannunsa kaɗai ya isa  ya siye zuciyar mace ya mallaki duk wani abinda mace zata so ga cikakken namiji  shiru ya  ratsa dakin bai sake cewa komai ba  haka itama bata sake cewa komai ba  tana kwance lamo “har ga Allah ba wai bata son komawa gidansu bane tana tsoron nisan da zai sake yiwa rayuwarta tunda ya tabbatar mata bazata sake ganin ko mai kama dashi bane ,  yayinda shi hankalinsa ya kashi gida biyu wani  na wajen ahlinsa wani na gurin aikin da zai tafi gobe bata ankara ba taji ya dauke cak ya sauko daita  ya zaunar daita a bakin gado ya kai hannu ya dauko laidar takeway din daya shigo dashi ya bude ya fito da take way ya bude “bisimilla ……

  Yatsina fuska tayi “banason taurin kai ko mutsu akan duk abinda nake so eat ya k’arasa maganar yana nuna mata abinci ,kin ci tayi kamar yadda ya umarceta a ranshi yace “ta fiyye shagwa’ba ni da nake dan oya oya  yaushe zan iya jurar wannan shirmen nata , spoon ya d’auka ya dubo abincin ya kai bakinta  “me yasa kike da taurin kai ? “bazaki taɓa shiryawa  dani ba matukar kina da taurin kai ,  bai tsaya jin abinda zatace ba ya sake  kai spoon karamin bakinta babu mutsu ta bude bakinta ta amshi abincin idanunta na kanshi sai dai cike suke da ruwan hawaye shi kanshi sai daya lumshe idanunshi saboda abinda yaji yana bin jikinsa wanda ya rasa ko menene, spoon biyar ta amsa ta kawar da fuskarta alamun takoshi ya bude kwalin   freshyo ya mika mata sannan  ya mike ya shiga bayi …

Shiru tayi tare da bin bayansa “iya haka ma tasan ta samu wata daraja ta musamman daga gareshi  mikewa tayi ta shiga tsintiri a d’akin da tunani “anya kuwa muryar data ji d’azu na matarsa ne ….? “Idan bana matarsa bace to na wacece ?”meye matsayinta garesa ? a natse ta koma kan gadonta ta kwanta tana sake zurfafa tunaninta gbdy hankalinta a tashe yake jin sautin matar sai dai hakan  bai sa son da take masa ya kau ba hasalima ji tayi zata iya rayuwa dashi da kowacecce  ,a natse ya tura kofar bayi ya fito sam bata ji motsin fitowarsa ba tana can duniyar tunani  sai hucin  numfashinsa taji a daidai saitin wuyanta  ta matsa  kafin ta ankare  ya haɗeta da jikinsa ya soma  rabata da kayan jikinta ,gabanta ya tsananta fad’uwa  da sauri “karfa soyayya ta rufe mata ido ta biyewa mutumin daya tabbatar daya baya sonta,  tana jin yadda hannunsa ke yawo a sansar  jikinta ta fashe da wani irin kuka yayinda qirjinta ke dokawa da matsanancin karfi kamar zai tsage.

gaba-daya  hucin numfashinta da kamshin jikinta ya cika masa hanci ,  jin sautin kukanta yasa ya  juyo daita bai tsaya wata wata ba ya  haɗe bakinsu guri daya  tare da kafe hannunsa daya  akan nipple d’inta yana murzawa a hankali wani irin tsotsa yakewa  bakinta yana murza kan nipple d’inta wanda take jinsa har cikin kwakwaluwarta ,take kukanta ya soma raguwa  saboda hannunsa dake yawo a jikinta, take  fitar numfashinta ya sauya ,shi kasan baya son yadda yake zakewa da jikinta tunda yasan bai dace ya mallaketa ba , sai dai ya rasa dalili   sake  manneta yai  tsam ajikinsa yana sake  shegewa jikinta tare da taɓa duk inda hannunsa yaci karo dashi a sansar jikinta musamman dukiyar fulaninta kusan minti talatin yana romancing d’inta wayarsa ta soma ringin a hankali ta zame jikinta daga nashi ta  kwanta tana sauke numfashi ,  figota yayi  ta faɗa saman faffad’an qirjinsa yana sauke numfashi da kyar batare daya ɗauki wayar ba , duk yadda take jin karfin soyayyarsa a matukar tsorace take dashi cikin sanyi jiki ya dinga shafata yana  sauke numfashi “ana kiran wayarka fa tayi maganar kamar zatayi kuka   ..

  hannu ya kai ya ɗauki wayar ya manna a kunnenshi batare da yayi magana ba daga can bangaren anas ya kira sunansa ” Jaguwa …
Shiru yayi yaki furta komai yana wasa da gashin tanweer  “nasan kana jina ka maida yarinyar nan kuwa ? shiru ya sake yi yana sauke numfashi da ajiyar zuciya “da alamun baka maidaita ba ?  lumshe idanunshi yayi yana yin kasa da hannunsa tare  zagaye kan nipple’s dinta, shi   kaɗai yasan yadda yake ji ajikinsa a duk sanda suke tare.. ..

“Ni ka yiwa gargadi  sai gashi  kai ne ka aikata hakan, jin haka yasa Jaguwa   mikewa ya sauko  yana gyara zaman gajeren wandonsa  dinsa daya dan zamo  daga kugunsa ya nufi kofar fita “bai dace ba gaskiya ,abinda mukeyi ne fa  kana  mana faɗa   me yasa zaka yi  …?saurin dakatar dashi yayi   “ni din ma ba da wata manufa na d’aukota ba ,na d’aukota ne da niyyar  azabtar daita, na gana mata  azaba na nuna mata kuskurenta akan  abinda ta min sai….
Yayi shiru ya kasa karasa maganar  “sai kuma ka bige da  …….

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button