KUSKUREN BAYA 1 TO 48
Alhj tahir dake zaune yana jiran zuwn nazifi yace “ya’akayi son Kai nake jira anyi nasarar samun alluran kuwa da kwayoyin ?”kayi hakuri karka ga kamar Ina cutar da abokinka wallahi rashin tashinsa shine zaman Lafiya da kwanciyar hankalina sai da nazifi ya zauna akan kujera sannan yace “karka ji komai dady an samu da yarda Allah Kuma zai yi aiki ajikinsa sosai fiyye dana baya dan wannan maganin bincike ya nuna idan anyiwa mutun sau goma zai iya mutuwa dady ya matso gabansa “kar dai ya mutu amman Kuma idan mutuwar zata zame min hutu Allah ya bada ikon tafiya “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun nazifi ya furta a ransa qirjinsa na bugawa da matsanacin karfi a sukwane nazifi ya jingina bayansa da abun kujera “dady nifa Ina ganin daga wannan maganin da zan kaiwa mumy bazan sake kawo komai ba nagaji da wannan aiki zuciyata ta kasa samun natsuwa kullum zuciyata na fad’a min Ina cutar da aminina, ruhina yaki samun salama wallahi bana iya runtsawa dama nasan dalilin da yasa kake son kassara rayuwar Ib Kuma nasan cewar ba cutarwa bace a rayuwarsa wallahi zan tsaya sai Inda karfina ya kare sannan zan tsaya naga komai ya tafi daidai .”
“kai dan Allah gafara can Sha Sha dady yayi hanzarin katseshi ta hanyar fad’ar haka “Ashe baka da hankali Taya kake tunanin zan fada maka dalilina ? karfi da matsayin da Ibrahim yake dashi acikin garin nan ne farkon jegon komai , muddin na bari ya tashi bisa kafafunsa komai zai iya faruwa dani, kasani Kai ma ko ka manta matsayinsa ne?bama haka ba Ibrahim nada karfin da zai iya komai akan cikar nawa burin dan haka
nazifi bazan barshi ya tashi ba Kuma bazan fada maka dalilina ba dan ko na fad’a maka bazaka fahimta ba ka dai qara min lokaci ka cigaba da aikin nan karshensa ma yazo “.
nazifi ya furza da wani huci Yana tsinewa alhj Tahir a zuciyarsa ya mike tare da yi masa sallama har ya kusan Kaiwa bakin kofa yaji muryar alhj Tahir “karka kuskura ka fadawa kowa wannan shiri dan bazan fad’a maka abinda zai biyo baya ba sai dai kawai ka tsinci kanka cikin tsaka me wuya abinda bazan so faruwarsa ba kenan dan har yanzu kana nan a matsayin d’ana” . gyada Kai kawai nazifi yayi ya fice .
Hajiya baseera zaune akan kujera me zaman mutun uku sai ga nazifi ya shigo hannunsa rike da leda wanda da gani kasan na asibiti ne dan a zahiri ake iya ganin abinda ke ciki ,hjy baseera na ganinsa ta saki fuska duk da zuciyarta cunkushe take da damuwar rashina lfyr Ibrahim ,
sosai tayi farincikin ganinsa tana qaunarsa tamkar yadda take qaunar Ib .ya dan rusuna cike da girmamawa ya gaisheta “Ina yi mumy ?”lafiya lau son ya fama da jama’a da kokari Kuma ?
“alhamdulillah mun godewa Allah ya Ib da jiki ? alhamdulillah Lafiya na ta samuwa ta nuna masa gurin zama da hannunta “ka zauna son “ya samu guri ya zauna yana cewa daga bangaren dady nake gbdy lamarinsa babu sauki a yadda yake kokarin son kassara rayuwar Ib,wallahi mumy abun na matukar bani mamaki haka nan sai na zauna Ina tunanin Anya kuwa mahaifinsa ne da yayi silar zuwansa duniya ?”mahaifinsa ne nazifi kama daina tantama shi mutun da son abun duniya ke sama da farincikin iyalinsa “.
runtse idanuwanshi yayi “dady na bukatar rayuwar Ib domin kuwa wadan nan magungunan da yake bukata a dinga bashi da allurai daidai suke da mutuwarsa dan watan wata rana za’a wayi gari babu shi .”
“Da naji wannan mummunar labari zanfi bukatar na bar gidan nan dashi sai dai ban san yadda zan bar gidan dashi ba batare da sanin mahaifinsa ba”. ta k’arasa maganar cike da damuwa .
shiru suka yi na second biyar sannan nazifi ya cigaba da magana a tsanake “karki damu mumy daga yau kisa a ranki Ibrahim zai dawo rayuwa kamar yadda sauran mutanen suke yi “zan d’auki nauyin ib bama garin nan ba kasar ma zan bari dashi gabad’aya Cikin dakiyar zuciya hjy baseera tace “wannan hukuncin naka yayi daidai Kuma na gamsu dari bisa dari dashi wallahi , dan haka babu abinda zance maka sai godiya ,yadda kake son ka nisanta tsakanin Ibrahim da mahaifinsa ta k’arasa maganar tana Kuka sosai tmkr wacce aka Aiko mata da sakon mutuwar ta ko akace mutuwa Ibrahim zaiyi “.
“lamarin alhj Tahir akwai ban tsoro da rashin tausayi da Imani “sosai kuwa yanzu dai a sirrance zamuyi komai ta yadda bazai fargaba “Allah ya d’aura mu akansa Allah ya kawar da tunaninsa akanmu “Ameen mumy ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraki a waya. “To na gode na gode sosai Allah yayiwa rayuwa albarka ya mike ya fice .”yana jinina girman alamrin dady ,gbdy ya gama ganosa Kuma yana tare da kwararrun hujojin da zai sa jami’an tsaro su tunhumeshi dashi idan bukatar haka ya taso , idan ta kama ya tsaya gaban alqali zai tsaya ya bada sheida domin kuwa mutumi kirki ake karewa da rufawa asiri irinsu dady kuwa sai dai a fallasasu duniya tayi Allah wadai dashi .”
***””
Da misalin karfe goma na daren ranar litini jaguwa ya shigo d’akin jikinsa sanye da kayan shan iska farare sol yayinda hannunsa ke rike da farar leda dake d’auke da roban takeway guda biyu wayam ya ga d’akin babu ita babu alamun ta jiki a sanyaye ya ajiye ledar hannunsa ya karasa ya zauna abakin gado a tunaninsa wanka take shiru har minti biyar ta wuce bata fito ba ya kira sunanta yana duba agogon dake d’aure da tsintsiyar hannunsa still shiru ya Kara five minute bai ji motsin saukar ruwa ba ya mike tsam ya Isa bakin kofar bayi yayi knowking still babu respond Kara knowking yayi no answer a hankali yaji zuciyarsa ta buga da sauri ya d’aura hannunsa kan handle din kofar ya murd’a yaji murfin a bud’e ya sanya kanshi cikin ya leka wayam ya gani nan ma babu ita yayi mamaki Inda taje ya fito a rud’e yana duba sauran dakunan gidan nan ma shiru babu ita ..
Wata uwar ashar ya saki ya wuce su anas ya fito zuwa haraban gidan da sauri da mugun sauri yanzu kam jikinsa ya fara bashi akwai matsala yana tafiya anas ,jubi,jabir ,har ma da kamil dake dingisa kafarsa suka biyosa suna Kiran sunansa amman bai juyo ba sai faman dube dube yake yana Kiran me gadinsa da sauri ya k’araso ya rusuna cike da girmamawa “ka budewa yarinyar nan kofa ne ?me gadi ya girgiza masa Kai alamun a’a , cikin fushi ya d’auke shi da mari “ka bud’e baki kamin magana zaka wani girgiza min Kai kamar kadangare “a’a sir ban budewa kowa get ba tun safe ma babu wanda ya fita daga gidan nan bayan Kai “.
ya Salam ya furta yana rike kugunsa da hannu d’aya ya shiga sintiri a haraban gidan ya bar me gadi dafe
da quncinsa “gidan ubanwa ta shiga ?wallahi idan banganta ba sai naci ubanka ya fad’a a fusace yana juyowa tare da nuna me gadi da yatsansa gbdy abokansa suka k’araso garesa alokacin d’aya anas ya dafa shi “wai meke damunka ne “ban sani ba duk banga amfaninku ba ace Kuna zaune tanweer ta fito baku sheida min ba “
“ta fito taje Ina ?”tun byn sallahr isha’i muke zaune a falo bana tunanin ta fito zo muje mu sake dubata tana ciki may be ko tana bathroom ne ya kamo hannun jaguwa ,ya fixge a fusace “bata nan na duba koina bata nan bata cikin gidan nan wallahi idan banganta ba duk sai na kasheku d’aya bayan d’aya cikin kankanin lokaci gabad’ayansu suka shiga tashin hankali anas ya basu umarnin nemota duk suka raba kansu suna nemanta shi kuwa jaguwa tuni ya dawo tamkar wani zarare shi kad’ai yasan irin tashin hankali dayake ciki “Ina tabi tunda me gadi yace bai bud’ewa kowa get ba ?ya d’aga Idanunsa da suka rikid’e suka canza kala zuwa katangar gidan da sauri ya girgiza Kanshi “muddin ta tsallaka katangar nan lallai zata mutu idan Bata mutu ba zata nakkasa gashi bayan gidan babu wasu gidaje sai kango .
ya fito a gigice anas da jubi suka biyosa suna cewa “Ina zaka ? “dan Allah ka natsu bazata iya tsallaka katangar nan ba , bai tsaya sauraronsu ba dan kwata kwata hankalinsa bai jikinsa Kai tsaye bayan gidan ya nufa yana haska gurin da wayarsa yana Kiran sunanta babu ita babu alamunta ya juyo
a harzuke yana masu wani irin kallo mai d’auke da rashin mutunci suna kallo ya dungule hannunsa, gbdynsu suka yi matukar tsorata shi kuwa anas byn tsoro har da kallon mamaki yake masa sai dai ya kasa ce masa komai wani irin kallo jaguwa ya cigaba da yi musu da jajayen idanunshi ..”
????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????