KUSKUREN BAYA 1 TO 48
Tanweer zaune a bakin gado tayi shiru ta zuba uban tagumi tana tunanin shikenan ta sadaukar ita da iyayenta sai alahira idan da rabon zasu had’u dan bata ga al’amun zata koma garesu ba ta barwa Allah komai komai yayi zafi maganinsa Allah
a tsakanin wannan lokacin ta lura Kullum gidan cike yake da mutane da yammata kala dabam dabam , wasu masu fasali wasu marasa fali ga shaye shaye baka jin kamshi komai a gidan sai na wiwi da ta’ba da sauran kayan shaye shaye, wannan Abu na matukar daga mata hankali idan ta tuna da irin qaunar da take wa Adnan kullum kokari take taga ta yakicesa a rayuwata dan ingata nata rayuwar amman abun ya cutura kullum soyyarsa sake nunkuwa yake amman hakan bai hanata son komawa gida ba .
ganin yadda gidan ya rikice yasa take kulle kofar d’akinta dan bazata zauna akaita a baro ba .tun da jaguwa ya lura tana kulle kofar ya tsareta yayi mata gud warning “karki sake kulle kofar nan ko da kudin ubanki na gina gidan ?”
ranta a matukar bace tace ” ba da kudin ubana ka gina ba hakazalika Kai ma bada kudin ubanka ka gina ba da kudin ubannen mutane ka gi… “bata k’arasa ba taji saukar mari akan quncinta “zaki sha wahala matuka a hannuna muddin zan dinga fada kina fad’a Kuma na rantse na sake ganin kin kulle kofar d’akin nan zaki ga yadda zanyi dake .”
Ya sake d’aukar fushi me tsanani daita bata damu ba duk sanda ya fad’a sai ta fad’a masa haka rayuwar tanweer ta cigaba a gidan jaguwa cikin rashin Jin dadi da kwanciyar hankali domin kuwa a maimakon abubuwansa yayi sauki sai yayi gaba tayi fushin tayi zagin tayi rashin kunya duk abanza dan bai canza ba sannan bai sauko daga fushin da yake daita ba dan haka ta sauko daga nata fushin tayi k’okarin shawo kansa amman ya faskara ta bishi har d’akinsa ta bashi hakuri amman yaki nan itama ta fita hanyarsa ko kallon kofar d’akinsa ta daina kullum cikin addua take Allah ya kawo mata d’auki ,adduar da batayi ada shi ya zamo abokin hirarta a yanzu .”
Hajiya Zainab zaune cikin halin damuwar da take kawarta hjy saratu ta kawo mata ziyara tare da diyarta mardiyya wacce ta kasance Kawa ga tanweer byn sun gaisa suka samu guri suka zauna nan ta fara bawa hjy zainab hakuri” addau zamu cigaba dayi komai zai daidata inshallahu karki sa tunani a ranki ,Allah bazai ta’ba had’a mana dadi gbdy ba idan Kuma ya had’a to wallahi mu tambayi kanmu “.hjy zainab ta kalleta cike da rauni ta girgiza Kai kawai bazan iya daina tunanin tanweer ba Allah na gode maka ban ta’ba tsammanin zan shiga tashin hankali irin haka ba a she haka iyayen da suka rasa yayansu suke ji idan akayi kidnapping dinsu ? Allah ka juyo da hankalin yan fashin nan suji tausayina dan zuciyata bazata juri rashin tan ba “hjy saratu tace” Ameen inshallahu zasu dawo daita cikin koshin lfy hjy zainab tayi shiru ta ma rasa mai zatace lamarin yan fashin Nan ya isheta hjy saratu ta Kalli hjy zainab tace “ki Kara hakuri .”
bayan sati d’aya taga alamun jaguwa ya dan fara saukowa dan har d’akin da take yake shigowa , bata kallonsa haka zalika bata ce masa komai har yayi abinda zai yi ya fita.
da yammacin ranar juma’a a bakin kofa suka yi karo dashi zata fita shi Kuma zai shigo d’akin garin ta matsa masa tayi baya zata fad’i da sauri ya Kai hannunsa ya taro bayanta , ita dake jiran ta ji bayanta ya daki kasan tayis taji saukar hannunsa ya tare ta sauke wahalalle numfashi suka tsurawa junansu Ido suna kallon kwayar idanun juna cike da shauki ko kifta idanunsu basa son yi yayi mata kyau matuka cikin shigarsa ta kullum yake wando da riga sai kamshi turare yake.
sun kusan minti biyar a haka sannan yayi k’okari janye kwayar idanunshi acikin nata
ya tsaidaita bisa kafafunta yana cewa”kin dinga kula ki daina wannan haukan tafiyan “
“haka zalika kaima ka dinga lura da naka haukan shigowan tana gama fad’ar haka ta wuce ta barshi nan yana kallon bayanta tsaki yaja ya gyara zaman rigarsa sannan ya shiga d’akin ya d’auki abinda zai dauka ya zauna zaman jiran dawowarta d’akin ya samu damar cin ubanta la’ada waje amman taki dawowa mikewa yayi ya biyota Kai tsaye falo ya nufa har zai wuce yaji motsin ta a kitchen ya k’araso ya tsaya a bakin kofa ya rike kugunsa da hanun daya wani irin kallo yayi mata na rainin wayo fuskarsa babu alamun wasa ya had’e girar sama data kasa tunda ta waigo taga irin kallon da yake mata Tasha jinin jikinta tare da rikicewa ta d’auke idanunta ta juya masa baya muryarsa a harzuke yace . “ni kike cewa mahaukaci ?
“to menene kake mamaki ?tayi mgnr a dake tana kokarin cire tsoro yayi taku d’aya yana ƙoƙarin damkota ta juyo da sauri qirjinsa ya hade danata atare suka sauke numfashi wani irin abu sukaji ya bakuncin zuciya da gangar jikinsu sakamakon haduwar da jikinsu yayi ,kasa yayi da sexy eye’s dinsa suka sauka akan qirjinta tsurawa qirjin Ido yayi yana kallon tudun dukiyar fulaninta duk da cikin riga suke amman a zahiri yake kallonsu .
wani zirrr yaji lokacin daya tuno yadda yayita murzasu a wancan ranar Ina ma zai sake samun dama irinta ranar ? iya murzasu ma kawai ya ishesa ba sai ya Kai ga saduwa daita ba .
a hankali ta soma k’okarin juyawa ganin yadda yake ma qirjinta kallon kurrilla, yasa hannu ya juyo daita ta sake fuskantarsa ya hade fuskarsa tamau “har Kin isa ki juya min baya ?batace umm ba bare Uhm uhmm illa qirjinta dake dokawa fiyye da kaida “ba’a min back to back sai dai nayiwa mutun ya Bude Baki zai sake yin mgn kira ya shigo wayarsa ya janye jikinsa ya soma received call yana mata gargardi da hannunsa alamun zai ka mata sannan ya fara amsa wayar “okay to shikenan gani nan just give me 10 minit yanzu zaka gani ya juya da sauri ya fita wani naunayen ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da abinda take ..”
Mmn sudais????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
????️19
Da misalin karfe tara na daren ranar laraba tanweer tana bathroom tana wanka jaguwa ya shigo d’akin hannunsa rike da tabar wiwi yana zuga a hankali cikin kwarewa ,warin bai tsaya iya d’akin ba har sai daya iskota bayi , abinda tafi tsana kenan ta gansa yana shan wiwi Kuma ta lura ya fahimci bata son hakan shi yasa cikin kwanakin dan iskanci idan zai shigo sai ya shigo mata daita yana sha ,Idan ta kulle kofar d’akin ya zama balai . “
cikin fushi ta fito sanye da doguwar riga hannunta rike da towel tana cewa “dan darajan Allah ka daina shigo min kana Shan wannan abar bana son warinta “kana da ilimi amman kullum kamar dabba kake abubuwanka, tsabar shagala kullum cikin aikata abinda Allah ya haramta kake , wallahi Koni da bani da wani sani akan naka ba zanyi lalacewa irin taka ba, Kaine Zina , Kaine sata , Kai ne sha…….”