KUSKUREN BAYA 1 TO 48
“yauwa haka nake so Ji abokina Ka bani mamaki ka rabu daita mu hutu tunda baka sonta banga amfanin zamanta damu ba dan kasancewarta damu matsala ne mu sallameta kawai anas ya fad’a yana cigaba da bashi shawara akan tanweer …”
Ita Kuwa tanweer tana shiga d’akin ta shiga har gitsa d’akin tamkar mahaukaciya a karshe ta fad’a kan gado hawaye na zubo mata sharrrrr akan quncinta tasan hawayenta nada halaka da bakaken maganganun daya fad’a mata , zuciyarta ta karye madadin soyayyarsa ta bar zuciyarta kamar yadda take buri sai ta dawo mata sabo fil tunda take baa ta’ba kallon idanunta aka furta ba’a sonta ba sai Adnan shine mutun na farko jikinta ya sake d’aukar zafi sosai wuni ranar bai shigo Inda take ba har dare ita Kuwa zazzabi da dacin maganarsa da ciwon gajiyar sex din jiya suka hade mata guri d’aya tayi kuka har hawayenta suka kafe bai shigo Inda take ba ya kama kanshi dan yasan koya shiga gurinta wani rashin mutunci zata masa shi Kuma bazai dauka ba .”
washegari tun karfe goma suka bar gidan batare daya lekata ba , dan har lokacin haushin abinda tayi masa bai bar zuciyarsa ba Kowani titi jami’an tsaro ne over fiyye da duk wani abun hawa, duk motar data zo wucewa sai an tsaresa an bincika ciki da wajenta tun daga nesa suka hango motar jaguwa tun kafin motar ya gama karasowa garesu suka daga ma eku hannu alamar ya tsaya a hankali motar ta rage gudu tare da k’okarin yin gefen titi ,a hankali eku yayi waning glass din motar yana mazurai ,daya daga cikin police officer ya dan leko cikin motar, cikinsa ne ya duri ruwa sakamakon ganin pesto a hannun jubi , ya ware Idanunsa sosai yaga ak 47 akan cinyar eku dake tuki ya Kai Idanunsa baya nan yaga sabon tashin hankali domin kuwa manya bindigu ya gani akan cinyar anas da jaguwa wanda ya kawar da fuskarsa gefe yana kallon titi da sauri Police office’s din da suke zagaye da motar suka yi baya jiki na rawa .
daya daga cikin police yace “sorry ban San ku bane you can be on your way ” a hankali glass din motar ya fara yin sama motar ta fara move police sukayi sauri suka tsaida wani me adaidaita suka duba cikin motarsa kana suka bashi hannu ya wuce direct to Ogun state suka nufa basu suka dawo gidan ba sai daf da sallar magriba wanka ya fad’a tare da alwala ya fito ya soma k’okarin gabatar da sallah byn ya idar da sallah magrib ya nufo d’akinta hannuwansa duka zube cikin aljihun wandonsa ya hangota kwance tayi ruf da ciki ko motsi kirki bata iyawa , ganin yanayinta yasa qirjinsa bugawa da sauri sai dai bai nuna hakan ba a fili tun kayan jiya ne sanye ajikinta, harara ya wurga mata sakamakon tuno abinda tayi masa a natse ya qaraso Inda take ya Kai hannunsa wuyanta nan yaji wani zafi ya ratsa tafin hannunsa kmr ta buge masa hannu sai dai bazata iya ba dan jikinta babu karfi “baki da lfy ne ?ya tambayeta banza tai masa taki motsa labbanta “raguwa banza kawai ya fad’a acikin zuciyarsa .”
“Kinyi sallah ma kuwa ?
Still shiru tayi masa bai damu ba ya cigaba da mgn “idan kinyi sallah ki canza kaya ki sameni a falon dan naga alamun tun kayan jiya ne ajikinki yana gama fad’ar hk ya juya har ya kai tsakiyar daki yaja ya tsaya yana cewa “na sanki da shegen d’aurin Kan tsiya ,minti goma kawai na baki ki sauya kaya ki fito dan Allah karkiyi abinda nace ya cigaba da tafiya ya fice daga daki .
Babu yadda ta iya ta mike ta shiga bayi alwala tayi ta fito ta tada sallah byn ta idar taki sauya kaya kmr yadda ya bukata ta fito , yana tsaye tare da friends dinsa ta fito duk suka tsura mata Ido suna kallonta maganar jaguwa ta jiya ce ta fad’o musu sosai suka qura mata Ido
suna yabawa da kyawunta .
yaji motsin fitowarta amman yaki juyawa “muje ko yace daita sannan ya fuskanci abokansa “zan dan fita amman bazan dade ba zan dawo ya karasa maganar ya nufi kofar fita ..”Tabi bayansa tana adduar Allah yasa gidansu zai kaita ta huta ..
suka bisu da kallo kowannensu na maganar zuci .yana gaba tana biye dashi abaya har suka ƙaraso inda motarsa ke fake eku na ganinsa ya taso da hannu jaguwa ya dakatar dashi ya buɗe murfin motar ya shiga itama ta shiga yayiwa motar key ya tada motar mai gadi na ganinsa yayi hanzarin tashi ya bud’e masa yana daga masa hannu ya fice ya hau kan titi tafiya kad’an yayi ya waigo gefen da take zaune cike da takaici”sai nace kisa seatbelt zaki sa kome ?” ya tambayeta cikin yanayi na ɗan jin haushi. Janyo belt tayi ta saka batare da tace umm ba bare Uhmmm sai qirjinta dake bugawa kamar zai fito waje.Sunyi tafiya me d’an nisa akan titi bata waigo ta kallesa ba, sai faman wasa take da yatsun hanunta tana addua acikin ranta .”
Kai tsaye 1829 plaza ya shiga har ya gama daidaita parking ɗin motar bata d’ago ba ya ciro wayarsa ya lalu’bo number aliyu yayi dealing ya manna a kunnensa maganar minti biyu yayi ya katse ya kira sadiq shima bai dade ba yayi disconnect din Kiran ya fito ya barta ya kulle motar gbdy, taja tsaki aranta ,shiru tayi tana zance zuci da dube dube da idanunta sai lokacin ta fahimci inda ya kawota, kallo d’aya tayiwa gurin ta fahimci gurin sun ta’ba zuwa da ib ta cigaba da zance zuci kmr ance ta Kalli kan kujerar daya tashi idanunta suka sauka akan wayarsa ta d’auka da sauri ta shiga daddana code din data ga ya danna jiya tana addaur Allah yasa haka ne 2020 ta danna sai ga wayar ta bud’e jikinta na rawa tashiga dealing number dad dinta kira biyu ya d’auka bakinta na rawa tace “dad …”!daga can bangarensa a zaune yake amman sai daya mike tsaye cikin firgice yace”tan !!! where are you ? dad ka zo 1829 plaza ….” ai bata Kai karshen maganrta ba taga yana tahowa da sauri ta sauke wayar a kunnenta tana kokarin goge number ta kashe waya gby da sauri ta ajiye wayar zuciyarta na bugawa da karfin gaske ta sunkuyar da kanta tana danne kukan dake kokarin fito mata “.
ya bude murfin bayan motar ya jefa ledar hannunsa sannan ya bude banagaren mazaunin direba ya shiga yaja Kai tsaye fmc hospital ya nufa a hankali ta d’ago idanunta nan ta fahimci asibiti ya kawota yayi parking Yana kokarin fitowa yace “fito muje” ya faɗa yana ciccin magani .jiki a sanyaye ta fito daga cikin motar ya rike tsintsiyar hannunta gam cikin nashi suka jera koina hasken fitilu ne kowa ya gansu sai ya sake kallonsu dan bakaramin dacewa sukayi da juna ba zaka d’auka su din mata da miji ne ,yayinda gabanta ya dinga faɗuwa aranta tace “Allah Ka bani iKon tserewa yau daga hannunsa “.
Tafiya kad’an sukayi taga sun tsaya a bakin wani ƙofa ya Kai hannu yana knocking din kofar daga ciki aka bashi izinin shigowa.” shiga muje “babu yadda ta iya ta shiga kmr zatayi kuka Sadiq na ganinsu ya miƙe yana fad’ad’a fuskarsa da murmushin jin dadi Dan bai taba ganin yayansa da wata mace ba sai yau shiyasa murnarsa a fili take da hannu ya nuna mata gurin zama ita Kuwa kallonsa take saboda tsananin kamaninsu zaka rantse tagwaye ne , babu shakka wannan mutumin dake gabanta dan’uwansa ne km na jini dan kamar ta baci a natse muryarsa ta fito tmkr ta dan’uwansa “father ya sunanta ne ?”ga tan a gabanka ta fad’a maka sunanta tunda shishigi kake son yi “.