KUSKUREN BAYA 1 TO 48
yayinda sp yusif ke tsaye a cikin wani kango sanye da bakin suit tare da wasu daga cikin yaransa da suka biyosa aiki daman kuma ya rabasu kashi kashi ne kowanensu da bangaren daya ɗauka ,wayarsa ce tayi ƙara ya ciro wayar daga aljihunsa cikin sauri yana duba screen din wayar sunan wanda ya gani yasa ya dauki kiran da sauri tare da mannawa a kunneshi “hello “
“Yes noted “
Inspector hasan dake fuskantar shi yace “how far ?
“We have to move immediatly “boss there won’t be a problem there be danger today let us move ,let’s move suka faɗa gaba-daya a hankali motar Jaguwa ke gudu ganin hanyar so silet ga duwatsu kaca kaca dole ko yana son yin gudu yabi a hankali yayinda yan-sanda ke la’be hagu da dama domin ƙoƙarin cafkarsa ..
A tsanake sp yusif ya fito daga maboyarsa ya sha gaban motar Jaguwa hade da tsaita bakin bindigarsa ga glass din motar Jaguwa slow motar Jaguwa ta koma tafiya a hankali har yayi kusa da sp cikin haka yaran sp dake boye hagu da dama suka bayyana suka saita bakin bindigarsu pistor “crack and shut basu tsaya wata wata ba suka budewa motar wuta bisa umarnin da’aka basu harbi motar suke da iyakacin kwarewarsu har sai da suka tabbatar da sun yiwa glass din motar ratsatsa…
DARLING’S????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
WRITING BY
BAGUDO& MIMI’S QUEEN
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
????️10
…A hankali sp yusif ya sauke bakin bindigarsa yana haki yana takowa a hankali har ya karaso jikin murfin motar jaguwa ya ja ya tsaya tare da d’aura hannunsa ɗaya a saman mota “the wages of sin is death …….”
ya furta haka yana duban inda yaransa ke tsaye rike da bindiga “yau dai munyi nasara kashe tantirin ɗan fashin daya addabi kasa da kasa ,Allah na gode maka daka bani dama da ikon kawar dashi daga doron duniya , isar da gawarsa headquater ma wani matakin d’aukaka ne garemu ,na dade ina addu’a akan zuwan wannan rana sai gashi tazo mana cikin sauki dole mu samu double promotion…… ” ya karasa maganar yana kallon sararin samaniya zuciyarsa fes cike da matsanancin farincikin samun nasara .
“ya sake buɗe bakinsa da niyyar sake yin magana yaji an daki murfin kofar motar da karfin gaske kofar ta buɗe wanda hakan yayi sanadiyyar da hannun jaguwa ya bugu da murfin kofar dashi kanshi sp yusif dake tsaye yayi taga taga ya koma baya sannan ya tsaya bisa kafafunsa yana kallon motar .
Mutuwar tsaye suka yi gabad’aya suna kallonsa take bindigar hannun sp yusif ta subuce yayi saurin sake ja da baya idanunshi na kan jaguwa dake ƙoƙarin fitowa daga cikin motar, duk ilahirin jikinsu rawa yake har sp yusif wanda hankalinsa kusan yafi na sauran tashi dan yanayin bugawar zuciyarsa da yanayin tsoronsa sai ya baka mamaki tamkar ba jami’in tsaro ba “
cikin isa da izza jaguwa yake takowa zuwa inda sp yusif yake tsaye , ya tsaya nisa kaɗan dashi wanda bai fi taku biyu su fuskanci juna ba , idanunshi dake a lumshe ya ware su fesss akan sp yusif yana ciza gefen lip’s d’insa na kasa,sp yusif ya kalli jaguwa kamar zai yi kuka saboda gigita da ganinsa a raye da yayi , tunda yake bai taɓa ganin abinda ya d’aga masa hankali irin wannan ba , “bai taɓa ganin dan adam din da aka yiwa harbi irin wanda suka yiwa motar jaguwa ba amman ya rayu har ya samu damar fitowa daga cikin motar cikin isa da izza ,tabbas yasan akwai wata a kasa ,wannan abu akwai tsarkakkiya acikinta “
Jaguwa ya had’iye dariyar sp yusif dake neman kufce masa saboda gabad’aya ya gama karantar yadda sp yusif da yaransa suka tsorata dashi ,dan gabadaya fuskokinsu ya sauya daga farinciki zuwa matsanancin tsoro da firgici kallo ɗaya zaka musu kasan suna cikin tashin hankali mai tsanani …
“waye kai sp yusif karaye ? mutumin da cin hanci da rashawa ya aura tun kana ƙaramin mataki har zuwa yanzu daka taka wannan matsayin , har kake godiya ga Allah bisa samun nasara akaina “wani mataki ka taka tukunan ma a rayuwarka da zaka so kama mutun irina “?yayi masa tambayar yana kafeshi da kyawawan idanushi hade da sauke numfashi .
“Ya kamata kusan ko waye ni kafin ku dinga bibiyar rayuwata kana min kallon mamakin ko ? “Kana mamakin yadda na rayu ko ? Zan so bude maka hanyar da zaka fahimci ko wanene ni da kai da sauran tawagar dake bibiyar rayuwata amman bazan yi ba zan barku cikin duhu da wasi wasi da kai da waɗan nan yaran naka daka taso gaba ” babu abinda zaku iya akan jaguwa sp yusif karaye , ba ku ba hatta shugaban tawagarku gaba-daya wato commition of police yayi kankatar da zai iya gaba da gaba dani bare kai da yaranka ya karasa maganar a fusace yana nuna sp yusif da yatsansa “
“a kasar nan kowa abinda ranshi yake so yake tare da aiwatar da son zuciya akan kaskantattu marasa galihu , “to bari kaji wani labari da baku isa ba dubunku ma basu isa suja da yaran jaguwa ba bare shi kanshi jaguwa , ni nan nafi karfinku nafi karfin hukuma kuma yanzu na sama addabar rayuwar manyan kasar nan ya karasa maganar yana dukan qirjinshi yana murmushi ……
“Anyway nasan daga inda shiriku yake kowanen daga cikinku ƙoƙarin raya kanshi da ahlinsa yake ba domin kare kasa da kasa kuke yin komai ba domin raya kanku kuke ,dana soma wannan aikin domin ɗaukar ran wani to da ina tabbatar maka kai ne mutun na biyu bayan wancan tantarin tanko gote ….”
duk wannan Maganar da yake yana yi yana jujjuya jikinsa ne kafin daga baya ya shafa fuskarsa ya cire fuskar dake manne da fuskarsa wata fuskar ta bayyana da tsananin kyau da sage zagaye daita “ka kalleni da kyau sp yusif muddin akaina zaka samu double promotion ina tabbatar maka bazaka taba samu ba har duniya ta nade saboda jaguwa mutun ɗaya ne mai fuska daban daban yana gama maganar ya zaro bindiga daga kugunsa ya saita daidai gwiwar sp yusif ya sakar masa bullet biyu a jere wata irin razananniyar qara ya saki tare da durkushewa a gurin “jaguwa ya nuna sa da bakin bindiga “bance ku daina farautata ba , sai dai ku shirya iya shiryawa kafin ku tunkareni yana gama fadar haka ya juya a fusace tamkar mayunwacin zaki yana taku kamar baya son taka kasa ya buɗe motarsa ya shiga yayi mata key a hankali motar ke motsawa tana moving gbdy suka bi bayan motar da kallon mamaki har sanda motar tayi musu nisa …..