KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

tashi yayi ya mike tsaye tare da fad’in “me ?!
Hawaye suka Kara zubo mata a hankali ya koma ya zauna saboda juyan dake dibansa bakinsa na karanta salatin manzon Allah gbdynsu tsit sukayi na tsawon lokaci sai mumy dake zubar da hawaye bai yi auni ba yaga numfashinta na fita da kyar da sauri ya tarairayota zuwa jikinsa Yana Kiran sunanta “Zainab !Zainab !!Dan girman Allah karki Kara min tashin hankali akan Wanda nake ciki ya jawo Goran ruwa ya zuba a hannunsa ya yarfa mata ya cigaba da shafa mata ruw a fuskarta a hankali har ta dawo haiyacinta ta bude idanunta tana kallonsa sannan ta sake fashewa da wani sabon kuka da take Jin radadinsu har cikin zuciyarta Nan take tausayinta yasa hawayen minister suka zubo bakinciki kamar ya Kai mumy lahira “kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki Zainab wannan jarabawa ce daga Allah Babu Wanda ya Isa ya Hana Hakan faruwa ,ban son ki cigaba da tsananta damuwa domin zata jefaki cikin mummunar matsayi ki dogara da Allah shine zai magance komai mu ma godewa Allah da qaddara ce ta fad’awa tanweer ba bin Maza take ba.

” Aranshi yace Ina ma zan iya goge kuskuren baya dana aikata hakika na tafka kuskuren gashi ya shafi yaruwar dilon diyata .Ta goge hawayenta tayi iya yinta ta tashi zaune ta kasa yace karki damu da sai kin tashi yanzu kiyi kwanciyarki ki huta bari na kwaso magunhunaki naga Wanda ya dace ki Sha .
Ya mike da sauri wani duhu ya rufe idanunshi baya ganin komai sai wasu taurari dole tasa ya dawo ya zauna Yana furta hasbinallahu wa ni’imal wakil yayi ta maza ya sake mikewa mumy tace “ka zauna karkaje ka fadi ka nakasa bai kulata ba ya fice dan yafi bukatar rayuwarta akan tashi .
bai dade ba ya dawo d’akin da kwadon magungunanta ya zauna yana bincikawa jikinsa na rawa
Saboda bacin rai Amman haka ya daure ya d’auki kanta ya d’aura saman cinyarsa yana mata sannu ya goge mata kwalla sai daya kwantar mata da hankalin sannan ya mike ya nufi dakin tanweer cikin tsananin tashin hankali.
tana kwance tayi ruf da ciki ya tsurawa bayanta Ido daman wannan shine karshen masu halin munafurci irin nasa, karshen mai son zuciya kenan, Kuma duk Wanda yaci bashin Allah sai ga karshensa tun anan gidan duniya ,sannan karshen mai irin halinsa kenan dansani.
a yanzu ya gane kuskurensa da yayi tsawon shekaru yana aikatawa a boye ,ya goge kwallan data zubo masa ya kirasa sunanta “tan!
Ta juyo a natse tana fuskantashin “Tashi ki shirya muje hospital a cire miki cikin ” da sauri ta shiga girgiza masa kai alamun bazata zubar .Wani irin juya ne ya soma dibarsa nan kuma ya shiga furta Kalmar Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun yana maimaitawa cikin haka mumy ta rarrafo ta shigo d’akin adaidaita lokacin da dady yake sake bawa tan umarni “ni dady Abar min abuna ina so …”
“Kina son me dan ubanki ?”me zakiyi dashi ? kina hauka ne Ko kin fara Shaye shaye ne ?”tayi mata tmbyr ajere juya na sake dibarta kafin kace me tuni ta soma yin kasa da sauri tanwer ta sauko daga kan gado suka hadu da dady a lokacin da take kokarin kaiwa Kasa da kyar take fidda numfashi bakinta na rawa tace “tan..! tan !! ki amince a cire cikin ….”

Assalamu alaikum yan’uwa barkanmu da wannan lokacin jama’a , ku taimakawa wannan baiwar Allah Mai suna rukayya wacce ta kasance budurwa ce tana fama da ciwon no-no tsawon shekara daya Kenna saboda iyayenta basu da halin da zasu dauki nauyinta yasa brest dinta d’aya fara lalacewa , rukayya tana zaune ne a garin Kaduna a unguwar kanawa tare da iyayenta dan Allah ku taimaka mata saboda Allah da darajan fiyayyen halitta annabi Muhammadu sallallahu alaihi wa sallam ga masu bukatar taimakawa ga account number nan 1438775094 Aishat Abdullahi access bank .Domin Jin qarin bayani a tuntubi wadan nan numbobin
07039569430
07037450698
08059623096
Allah ya bada iKon taimakawa .
????????????????????????
KUSKUREN BAYA
     ????????????????
????????????????????????

PAID BOOK

 WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
          

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

“Wannan  littafin na kudi ne  mai bukata karanta shi  ya tura 500 ta wannan  account number din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert  domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu  a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.

????️24

Mumy   bata  qarasa maganarta   ba numfashinta  ya  sake tsarkewa   idanunta na faman  zubar  da  hawayen   tashin hankali ,” Ina  ta  ta’ba ganin   balai   irin  wannan  , Allah  ya rufa  maka  asiri  ka  nemi ka  tonawa  kanka, dady  kuwa duk ya  rud’e  ya gigice   sai  zufa  yake   fitarwa  da  kyar  ya bud’e bakinsa   yace  “zainab  ki rufa min   asiri  dan  girman  Allah   karki  d’aga min  hankalinki  da  sannu   zata  fahimcemu  ta janye kudirinta. mumy  taja numfashi  da kyar  ta  sauke  ta sake fashewa  da  kukan  bakinciki
ita abinda ya d’aure  mata kai mai  yasa  tanwer  zata ce abar mata  cikin “?
“To  tayi  meye  dashi ?”  cikin muryar  kuka  tace “da kunnenka kaji  abinda ta  fad’a  wai  tana son  abunta “. ta k’arasa maganar tana  zubar  da hawaye.
nan take tausayin  mumy  ya kama tanwer  bisa kuncin data jefa  mahaifiyarta muryarta na rawa tace “mumy  kiyi hakuri ” ta k’arasa maganar tana zubar  da ruwan hawaye mumy ta sake matso  ruwan hawaye “tayi hakuri  akan me Kenan” ? ” akan zata yarda a zubar da cikin Ko kuma  bazata yarda ba ?”
“Sannu zainab komai zai daidaita inshaallahu tanwer yarinyar ce har yanzu batasan ciwon Kanta ba ,batasan rayuwa ba  sai mun zaunar daita  mun fahimtar  daita  illar abinda take son  jefa  rayuwata “.mumy  ta sake   runtse idanunta   gam jikinta na  wani  irin rawa saboda bacin rai .”

Sallama  suka  jiyo daga  parlour  babu tantama muryoyin yan’uwanta  ne  take  jiyowa bashir da Jamil da sauri  dady ya jinginar   da mumy  ya nufi waje yana  fad’in ” gamu anan  ku shigo ya fad’a tare da  juya ya Koma  d’akin  ,suka biyo  bayansa  jugun  suka ga yayartasu ta rasa  kuzarinta. “yaya  dai  aunty  meke faruwa dake ba  dai jikin bane ya tashi ?sun  fadi  haka ne saboda zuciyarta  data  soma ciwo adalilin  dauke tanwer .
dady  yace  “shine dai yake  k’okarin  tashi  bashir , nan take suka  zube  gabanta kamar zasuyi  mata  kuka  uncle  Jamil ya  d’auki  Kanta ya d’aura akan  cinyoyinsa yana cewa  “sannu  auntynmu !shima bashir sannu yake  mata faman jera mata
sam  hankalinsu bai  ga tanwer ba ta matso kwalla ta dubesu  d’aya bayan daya “kunzo lafiya ?”ya mantaku da yaranku suke “? suka  had’a baki suka amsa mata da “lafiya suke   sunce  agaisheki “ina amsawa  ta k’arasa maganar  da kyar wasu sabbin  hawaye na gangaro mata ta gefen Ido  bashir ya goge mata kwalla ,Kannenta uwa d’aya uba d’aya itace babbarsu su hudu ne agurin  iyayensu  kuma sun mutu sun barsu maza uku ita kad’ai  ce mace  acikinsu shiyasa ma ta d’auki soyayyar duniya ta d’aurawa tanwer duk da bata rasa kulawa da gata da komai ba  daga gurinsu dan  sun maye mata gurbin komai duk abinda tace shi sukeyi kafin ma tace sunyi mata suna tsananin qaunar junasu .”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button