KUSKUREN BAYA 1 TO 48
Ahankali suka dubi dady suka gaisa kafin su sake wata magana dady ya fad’a musu komai dake faruwa duk sukayi shiru tare maida hankalinsu inda tanwer ke durkushe tana kukan zuci .
Idanunsu na Kanta na tsawon lokaci kafin uncle Jamil ya dube uncle bashir sannan ya cire kan mumy ya d’aura a jikin dady ya k’arasa inda take cikin hanzari yasa hannu ya fizgota ba karamin tsoro ya bata ba ta kwalla qara tana rike cikinta
tare da furta “wayyo Allah cikina “. wani bakinciki ya qara turnukesu bai san lokacin daya buge mata baki ba yace “maza ki rufe mana baki shasha banza shashar wofi Kawai ” .
da sauri tasa hannu ta dafe bakinta wanda take kyautata zaton hakoranta zasu iya ficewa su bar bakinta Idan bata dafe bakin ba “jawota yayi kiiiiiii bai direta akoina ba sai a gaban mumy ta zube har tana cin karo da gwiwar mumy ya zaro mata Ido kamar zasu fad’o waje mumy tace ” matsa kusa dani dan zan iya shake miki wuya ki mutu na huta”.
da sauri ta janye jikinta dan wani irin tsoron mahaifiyarta ne ya shigeta, a hankali hawaye ke ambaliya a fuskarta sun fi minti biyar jugun jugun babu wanda ya sake cewa komai saboda takaicinta.. “gbdy kina son ki rusa rayuwarki, ki lalata asalinki, me zakiyi da wannan ciki ?”bari kiji idan ma kin barshi babu abinda zai janyo miki sai bakin fanti da cila rayuwarki cikin garari , sannan babu mai aurenki da dan shegen ‘yanta’ada dan haka wannan cikin dole a zubardashi tana jin haka ta sake fashewa da wani sabo kuka .
gbdy suka nemi natsuwarsu suka rasa ji suke Kamar zuciyarsu zata buga wallahi sun san da soja yana kasar to da sai ya balbalata yayi gudunwa gunduwa daita dan ya tsani ganin mumy cikin damuwa bare kukanta uncle Jamil jikinsa sai tsuma yake yana faman jan tsaki .”
A natse uncle bashir ya mike ya riko hannunn tanwer ya nufi waje daita , ta gaban abokan dady suka wuce dan suna zaune har lokacin a matukar firgice suka bisu da kallo “Kamar tanwer nake gani Ko kuwa idanuna ne?” inji cewar alhj Lawan Shuaib “ba idanunka bane itace “a’a to yaushe aka dawo daita da bamu sani ba ?” wa zai baka wannan amsar tunda duk yanzu muka ganta .?alhj rufa’i ya fad’a yana kwabe baki.
Kai tsaye part din mumy uncle bashir ya nufa daita ya murda handle din kofar suka shiga ya zaunar daita abakin gado shi kuma ya janyo karamar stood ya zauna ya fuskance na tsawon lokaci sannan ya fara magana jiki a sanyaye “tan….!
Ta d’ago runannun idanunta da suka kode tsabar kuka ta zuba masa tana jiran taji mai zaice “mai yasa baki son a zubar da cikin nan ? “tayi shiru tare da sunkuyar da kainta kasa wasu hawaye na sake gangaro mata suna diga a tafukan hannunta.
” kiyi hakuri my daughter a zubar da cikin nan babu abinda zakiyi dashi barinsa bai da wani amfani ,wannan cikin matsala ne a rayuwarmu gbdy”.
on-expecting yaji sautin muryarta cikin dodon kunnensa “yanzu uncle bashir zaka jagoranci kisan kai ?” take zufa ya shiga tsatsafo masa hankalinsa yayi mugun mugun tashi”, wannan cikin dole na haifesa domin yunkurin zubar dashi yafi samunsa barna da ta’addanci da tarin zunubi .
“Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ya dinga furtawa had’e da mikewa tsaye cikin tsananin tashin hankali ya shiga zagaye d’akin yana maimaitawa abinda ta fad’a gumi na sake karyo masa duk da gudun ac dake aiki a d’akin amman hakan gumi ke tarara ajikinsa kamar ruwa kwakwaluwarsa ta hargitse
tana hautsinewa cike da buguwar zuciya ya tsaya cak a tsakiyar d’akin yana kallonta tare da nazarinta a matsayinsa na barrister take ya hango wasu abubuwa a tattare daita a hankali ya lumshe idanunshi tare da sanya hannunsa a daidai saitin zuciyarsa ya dafe dan wani irin bugawa take saboda abinda ya zowa zuciyarsa ,still idanunta basu daina zubar da hawaye ba cikin kasa da murya ya kira sunanta “tanwer !
Idanunta ta sake da d’agowa wadan da suke cike da ruwan hawaye ta kalli uncle bashir murmushin takaici ya sakar mata wanda yafi kuka ciwo.
“ba cikin kike so ba wanda yayi cikin so Ko idan na kintata daidai ?”shiru tayi tana tunanin amsar da zata bayar kafin idanunta su sake Kawo wasu ruwan hawaye .
Ya numfasa ni kadai ne anan ki fad’a min gaskiya zan fahimceki. “wannan gaskiya ne uncle ina son shi sosai ,ina masa son da bazan iya zubar da gudan jinsa ba “. ware idanunshi yayi sosai akanta yana cewa “are you out of your sense dan fashin kike so tanwer? shiru tayi tana nazari cikin zazzafa murya yace “why tanwer ?”me yasa zaki mana hk ?mai yasa zuciyarki zata kamu da sonshi ?”a Ina ma kika san zaki qara ganinsa ?”mutane da ba guri d’aya suke zama ba Ke yanzu kina tuninin zamu yarda dashi ne ?”
Da sauri ta rike masa hannu tana cewa” dan Allah uncle ka taimakeni Adnan mutumin kirki ne qaddara ce take yawo a rayuwarsa, wallahi idan kagansa bazakace dan fashi bane,yana da kirki da kamala da tausayi ….”
“Tausayin banza da wofi yana tausayi ya kwana dake ?yayi maganar yana k’okarin cire hannunsa cikin nata ta sake rikewa gam”wayyolhhly Allah ka taimakeni uncle ta fad’a jikinta na rawa Ina son shi wallahi zan iya mutuwa akanshi, zaku rasani akanshi, ni dai ina sonshi ..” da sauri ya runtse idanunshi kafin ya fizge hannunsa cikin nata, kuka take sosai tana rokonsa amman Ina a fusace ya juya ya bar d’akin zuciyarsa na bugawa da karfin gaske . “
A falo sukai cikibis dasu dady sun kamo mumy da sauri ya karasa ya sa hannu suka nufi d’akin dady daita, nan fa hankalin mutane dake zaune falon yayi kansu atare suka mike tsaye suna kallon juna “Ku da alamun gidan nan babu lafiya ,nima abinda na gani Kenan mu wuce Ko mu tsaya neman qarin bayani ?”gasky gara mu tsaya muji Ko meke faruwa suna cikin tautaunawa sai ga dady ya fito daman niyyarsa ya sallamesu kowa ya kama gabansa ,cike da damuwa suka matsoshi suna tambayarsa “fatan dai lafiya zainab take Ko jikin ne ?”eh jikin ne amman da sauki yanzu likinta nake shirin Kira “okay to Allah ya kara sauki inji cewar alhj rufa’i dady na gama magana ya nufi kofar fita dole tasa suka biyosa alhj hamisu yace”Ashe kuma tanwer ta dawo ?”eh! Kawai yace ya kara gaba ya nufi inda motarsa take fake ya shiga ya zauna tare da kunnata kamar zai fita hakan yasa kowanensu ya sha jinin jikinsa ya nufi inda motarsa take dan ga dukkanin alamun yana bukatar su bar masa gidansa dan haka suka soma k’okarin barin gidan zuciyarsu cike da sake sake Kala Kala .