KUSKUREN BAYA 1 TO 48
Jaguwa ya dade tsaye a lambun gidansa byn ya gama waya da mahaifiyar tanweer yana shawagi agurin tare da tunani kala dabam dabam cikin haka wayarsa ta soma ringing ya d’auka ya manna a kunne ya tura hannunsa cikin aljihun wandonsa maganar minti biyar kacal sukayi ya katse Kiran ya cigaba da shawagi sai gasu anas kowannensu hannunsa rike da tabar wiwi yayinda anas ke rike da biyu ya mikawa jaguwa d’aya, ya amsa ya kai bakinsa ya fara zuka sannan gabad’ayansu suka samu guri suka zauna suna magana akan mata “ya kamata mu dan fita yau ko Kuma muyi invent dinsu zuwa gidan nan ?”ai rayuwa babu mace quntatawa ne kasamu mace lafiyiyayya Kuma me shaye shaye ka sauke gajiyarka akanta inji cewar jubi murmushi jabir yayi “wallahi kamar kuwa kasani mace me shaye shaye tafi dadin muamula ga juriya saboda bata haiyacinta haka dai sukayita hirarsu akan mata
yayinda jaguwa ya lula duniyar tunanin wanda tunanin kusan duk na tanweer ne .yana jin kamar ya shareta amman zuciyarsa ya kasa aiwatar da hakan ko babu komai tana bukatar kulawarsa tunda bata da lafiya kuma idan bata ci abinci ba taya za’a yi ta sha magungunanta ?
wannan tunanin yasa ya kira aliyu ya aika siyo mata abinci bayan kamar awa d’aya aliyu ya dawo hannunsa rike da farar leda ya amsa ya ajiye ya cigaba da zugar wiwi , sai da yayi mankas sannan ya mike ya nufi d’akinta bakinsa d’auke da sallama hannunsa rike da farar leda yayinda gbdy jikinsa ke warin wiwi hade da turaren jikinsa .
shigowarsa ke da wuya d’akin ma ya kaure da warin wiwi dana turarensa wani irin haushi ya kamata idan akwai abinda ta tsana shine warin wiwi ko ta’ba , kallo d’aya tayi masa ta d’auke kanta ta mayar wani gefe tana wasa da yatsun hannunta .
Ya ajiye ledar hannunsa yana cewa “ga abinci nan kice ki sha magani kin ma kuwa yi sallah isha’i ? “ban yi ba Kuma bazan yi ba, wallahi idan ka sake min magana akan sallah sai na kashe kaina “Allah ya bada sa’ar tafiya dadin abun idan kin kashe kanki bazaki rataya a wuyan Adnan ba kice zaki mutu kafura “.
“Kai ne dai kafuri Kuma Kaine zaka mutu a wannan rayuwar da kake. “are you out of your sense ? ya fad’a a fusace ” ni kike fad’awa haka ?” shiru tayi tana dubansa kafin idanunta ya kawo ruwa “amman Kai me yasa kullum sai kayi min magana akan sallah kamar wata kafura ? “Alama na gani na bakin son yinta ” .
shiru ta sake yi kamar me nazari numfashi ya fesar ya juya zai fita
yaji sautin muryarta a raunane “kazo ka d’auke banzar abincinka dan ba zanci ba” kad’a kafad’unsa yayi yace “daidai kenan Ina son haka ,Kinga rashin cin abincinki ko rashin walwarki bazata dameni ba saboda bana sonki bakya cikin rayuwata kisan Allah ko nemanki nayi na rasa bazan damu ba dan bayan mahaifiyata da kannena ban san ciwo kowa ba, bayan darajan kannena dana sani ban San darajan kowace mace ba Kinga Kenan Kema kina cikin matan da bana ganin darajansu ,yana gama fad’ar haka ya fice daga daki .”Kuka ta rushe dashi tana Kiran tashi uku sai da tayi me isarta sannan ta janyo ledar daya ajiye mata dan yunwa take ji sosai , taci kad’an ta bar sauran ta shiga bayi tayi wanka ta fito ta sha magani tayi sallah ta kwanta lamo akan bed tana tunanin iyayenta, “Allah sarki dadynta muryarsa ta nuna yana cikin damuwa ” dad dinta da bai iya cikakken awa d’aya ba tare daita ba ,ko zuwanta turai karatu baya jimawa batare daya ganta ba, kullum Kuma cikin video call suke ,ko ya dad dinta zai ji idan ya ga ta dawo garesa ? tasan rungumeta zai yi a karshe ya d’auketa sama yayita juyi daita yana cewa “my tan ta dawo I really miss you my tanweer wasu hawaye masu zafi ne suka biyo gefe da gefen idanunta.
“Ko waye wanda ya tura musu yan fashi ?waye wannan ? ta tambayi kanta “waye cikin family dinmu ?dangin mumcy dina ne ko dangin dad dina ne ?”dangin dad dina basa zaune a lagos tunda shi din haifafen garin Kaduna ne, mumcy dina Kuma yar d’aura ce “,ai daga koina mugu zai iya idar da nufinsa ya farmaki rayuwarka,Allah sarki mugu bashi da kama suna tare dashi Amman basu san cewar shi din makiyinsu bane “shiru tayi tana sake zurfafa tunaninta ,babu abinda ya shiga
yawo acikin kwakwaluwarta kamar hirarsu jaguwa a wacan ranar data san dan fashi ne “tabbas taji sun ambaci sunan Alhj tahir a hirarsu .
a lokacin ta zurfafa tunanin domin sanin me sunan a karshe zuciyarta ta tsayu akan mahaifin Ib shi kad’ai tasani me wannan sunan, tashi tayi zaune ta zauna “tabbas shine me sunan Ibrahim Tahir ta furta a fili “Kai ba dai shi ba bazai ta’ba aikatawa mahaifinta haka ba sai dai idan suna ne ya zamo daya , to Kuma ai maganar Adnan ta nuna Wanda ya turasu na tare dasu to meye gaskiyar lamari ? take zuciyarta ta shiga wasi wasi wata zuciyar tace shine wata zuciyarta ta karyata hakan .
wasu hawaye ne masu zafi suka
zubo akan kuncinta ” tana bukatar ganin iyayenta tana son ganin dad dinta da mum dinta tana bukatar Jin dumin jikinsu kamar yadda ta saba dan girmanta bai hanata kwanciya ajikinsu ba she really miss them .”.
Daren ranar kasa runtsawa tayi jikinta yayi zafi rau kamar garwashin wuta sai faman juyi kawai take akan mamaken bed din da take kwance tana tunanin mafuta kwakwaluwarta ta sake lula kogin tunani mai zurfi akan yadda zata bar gidan ta kowani hali dan dole tasan yadda zatayi ta bar gidan tun bai canza ra’ayinsa akanta ba ya fara kusantarta.
da kyar bacci barawo ya saceta washegari da safe bai shigo yaga halin da take ciki ba yayita lamuran gabansa ita Kuma hakan ya bata damar tsara yadda zata bar gidan kota halin balai, ta fito sanye da doguwar riga baka har kasa tayi rolling kanta da mayafin rigar Kai tsaye ta wucesu a falo zaune tare da abokansa har ta fito haraban gidan
ya fito ya biyota yana cewa ” ke Ina zaki kika wani wuce mutane dan iskanci ?
“Bansani ba Kuma karka sake tambayata Inda zani dan ni ba diyarka bace sannan ba abar ikonka bace da zaka wani tsareni da banzar ta…..” shiiiii wuce ki koma ciki” “bazan koma ba gidan nan zan bari Kuma a yanzu ta fad’a tana cigaba da tafiya taku uku yayi ya riko tsintsiyar hannunta “muje babu Inda zaki sai wadin zamanki a gidan nan ya Kai .
ta juyo a fusace ta sanya kwayar idanunta cikin nashi cike da balai tace “Kai waye da zaka hanani tafiya?.
“ni Adnan amad “.ya bata amsa yana kallon cikin idanunta fuskarsa a had’e babu alamun wasa .
“wallahi baka Isa ba who the hell are you? duk da me gadi gidan nan abun ikonka ne zanyi duk yadda zanyi na bar gidan nan Kuma a yau .
jaguwa bai saurarata ba ya jingina jikinsa ajikin motarsa ya tsura mata Ido yaga iya gudun ruwanta . tanweer ta Isa Inda taga makulan motoci rataye ajikin bangon rufar motaci ta d’auki ta camery ta rike gam zata bude moto tuni yaransa suka tareta bisa umarnin jaguwa da yayi musu umarni da Ido sai dai hannunsu bai ka ga jikinta ba suka hanata ta’ba kowacce mota a daidai lokacin su anas suka fito suka tsaya suna dubanta .