KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

“Assalamu alaikum yan’uwa barkanmu da wannan lokacin Dan Allah ku taimakawa wannan baiwar Allah Mai suna rukayya wacce ta kasance budurwa ce tana fama da ciwon no-no tsawon shekara daya Kenna saboda iyayenta basu da halin da zasu dauki nauyinta yasa brest dinta daya ya lalace har ta kai ga tsutsa , rukayya tana zaune ne a garin Kaduna a unguwar kanawa tare da iyayenta dan Allah ku taimaka mata saboda Allah da darajan fiyayyen halitta annabi Muhammadu sallallahu alaihi wa sallam ga masu bukatar taimakawa ga account number nan 1438775094 Aishat Abdullahi access bank .Domin Jin qarin bayani a tuntubi wadan nan numbobin
07039569430
07037450698
08059623096
Allah ya bada iKon taimakawa .
????????????????????????
KUSKUREN BAYA
     ????????????????
????????????????????????

PAID BOOK

 WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
  

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin na kudi ne  mai bukata karanta shi  ya tura 500 ta wannan  account number din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert  domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu  a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.

????️23

Ta kusan minti shabiyar tana kwance tana maida numfashi tana furta “wayyo Allah zan mutu ” da kyar ta Samu ta yunkura ta tashi zaune amman ta kasa mikewa tsaye saboda jirin da take jin har lokacin . da Jan jiki ta k’arasa Inda ta jona karamar wayarta ta kunna sakonnin dayawa sunyita shigowa ,tayi shiru had’e tsurawa wayar Ido zuciyarta na beating very fast har sanda sakon data tura da layin jaguwa ya shigo . naunayen ajiyar zuciya ta sauke kana ta soma k’okarin neman layinsa , Kiran na shiga sai dai ba’a d’auka , ta kira yafi sau goma bai d’auka dan haka ta hakura ba dan ranta yaso ba .
a dudduke ta k’arasa inda wordrobe din kayanta suke jikinta na rawa ta bud’e ta d’auki doguwar riga mara nauyi ta sakawa jikinta ta fito zuwa falo a lokacin har mutanen gidan sun hallara suna zaune akan kujera na alfarma , rukayya na ganinta ta saki fuska tana sakar mata murmushin jin dadin ganinta murmushin karfin hali tanwer ta mayar mata sannan tace “rukayya yaushe kikazo garin”?
“Ai na kwana biyu a garin nan tunda muka zo dasu Alhaji jaje Ina nan ban Koma ba “.
“Ai ko kin kyauta da kika zauna tare dasu mumy . ” qaraso ki zauna mana, yanzu nake shirin na shigo d’akinki nayi miki ya gajiya saboda yanzu mumy take fad’a min ashe ma tun shekaranjiya dady yaje ya d’aukoki “?sannu Allah ya kiyaye gaba, Allah ya kare yan gaba .
“ameen rukky na gode tanwer ta fad’a tare da k’okarin zama kusa da mumy tana sauke numfashi da kyar ,jiki a sanyaye ta d’aura Kanta akafad’an mumy tana cewa “wash Allah nah wallahi gabadaya jikina kamar ba nawa ba sai ina jin yana min nauyi ” .sannu ai dole kiji haka wa yasan irin wahalar da kika sha a hannun wadan nan tsinannun yan ta’adan ai tsakanina da wadan nan mutanen sai dai Allah ya Isa bazan taba yafe musu ba “.
ita dai tanwer bata ce komai ba kawai ta cigaba da sauke numfashi ko cikaken minti biyar batayi da zama ba yan aikin gidan suka fito daga kitchen domin shirya dining nan sukayi turus suna kallonta dan sam basu san da dawowarta ba ,cike da murna suka hau gaisheta suna yi mata allah kiyaye ita kuma ta dinga amsa musu da kyar sannan suka nufi hanyar dining mumy ta tsaidasu suka dawo suka tsaya tare da tattara dukkanin natsuwarsu zuwa gareta ,ta kallesu d’aya bayan daya tare da kiran sunansu” zulai, ussaina suka amasa da “na’am hajiya “. “to ga tanwer ta dawo gida sai dai ba’a ce ku fad’awa Kowa ta dawo ba muddin naji maganar dawowarta ta fito abakacin aikinku bayan na had’aku da hukunci mai tsanani Kenan” jikinsu na rawa suka had’a baki gurin cewa “inshaallahu babu mai ji abakin mu, mumy tace “da kun huta .
tanwer ta d’ago idanunta da suke a galabaice ta kalli mai aikinsu zulai tace “zulai kije d’akina ki gyara min toile dina ki kwashe duk sabulun dake d’akin da toilet din Ku raba da ussaina ,Zulai ta amsa da “to! sannan ta juya da sauri ta nufi d’akin .
Rukayya ta dube tanwer cike da mamaki tace “Ikon Allah daman bada sabulun kike amfani ba “? “dashi nake amfani amman yanzu ban san dalilin ba gabadaya Ina shiga d’akin naji bana son kamshinsa .
zulai da ussaina suka share mata d’akin fes da bayi kana suka tattara duk sabulan dake d’akin sukayo waje dashi suna nan zaune suka fito suna cewa sun gama sannan suka koma kitchen bakin aikinsu .”

dady ya fito daga d’akinsa sanye da jallabiya blue colour yar maroco ya samu guri ya zauna akan d’aya daga cikin kujerun dake zagaye da dining table yana ya fito tanwer da hannunsa d’aya alamun tazo garesa yayinda dayan hannunsa Ke rike da waya ta mike da kyar tana ciza lips dinta ta k’araso inda yake zaune ta samu guri ta zauna kusa dashi a lokacin har ya fara waya da dan’uwansa yana fad’a masa batun dawowar tanweer dan Ko zai boyewa Kowa dawowar tanwer gida bazai iya boyewa dan’uwansa ba sun dade suna tautaunawa kafin daga bisani sukayi sallama mumy da kanta tayi saving din tanweer ta tura mata plet din abinci gabanta “maza ga abincin nan kici ki koshi ga maganin ciwon jiki sai ki sha “da Ido kawai tanwer ta bita dashi sannan mumy ta juya kan dady tayi saving dinsa , tanweer ta kalli abincin kawai tana yatsina fuska ba dan bai mata ba sai dan yanayin da take ji ,dan gbdy ilahirin jikinta tamkar ba ajikinta yake ba, ita Kanta abun yana bata mamaki daga dawowarta gida komai ya sauya mata sai dai kawai ta danganta hakan da rabuwarta da adnan ne yasa jikinta ya canza .
Mumy tace “rukayya taimaka kije d’akina ki d’auko min wayata nima na Kira kannena na fad’a musu dawowar tanwer . rukayya tace” to tare da mikewa da sauri ta nufi d’akin mumy ,tanwer ta shagwabe fuska”kai mumy bana ce Kar kowa yasan na dawo ba sai na gama bincikena ,mumy tayi mata wani irin kallo “yanzu fa dad dinki ya Kira dan’uwansa baki ce masa komai sai ni?” “amman mumy ..”amman mumy din me kinga bani da wad’an da suka fisu kuma bamu saba boyewa juna komai ba haka zalika bana zargin yan’uwana, dan sunfini qaunar kaina , ta k’arasa maganar a daidai lokacin da rukayya ta dawo hannunnta rike da waya ta mika mata “yauwa rukayya sannu da k’okari na gode ,nan ta kira kannenta d’aya bayan daya ta sheida musu , aiko sunyi fariciki sosai da jin labarin dawowar tanwer har ma sukayi mata alkwarin zasuyi kokarin su shigo cikin sati su duba tanwer din sukayi sallama dasu cikin tsananin farinciki har kusan karfe goma na dare tan tana tare dasu dady da mumy suna hira har da rukayya sannan kowa ya tashi ya koma d’akinsa .”
tanweer koda ta koma d’akinta sai data sake Kiran number jaguwa still yana shiga baya d’auka dan haka ta aika masa da text message .

slm adnan fatan kana lafiya ya kake tanwer ce please ka kirani ina son naji muryarka

Ta tura sakon sannan ta cigaba da kiran layinsa still bai kira ba kuma bai d’auka ba , kwanciya tayi lamo akan katifa zuciyata ta kasa samun natsuwa, zuciyarta cike da ciwon abubuwa barkatai “Adnan yaki d’auka wayarta Koda bai san layin ba ai ya kamata ya biyo Kiran yaji mai Kiransa, tunaninsa ya hanata runtsawa , bata ta’ba son abu Kamar yadda take jin son Adnan ba faffad’an qirjinsa ya shiga yawo acikin kwayar idanunta da kwakwaluwarta kallon qirjinsa kad’ai ya Isa ya tunzura zuciyar mace ta kamo da matsanancin qaunarsa , nmj duniya ne Ko daga qirjinsa .
ta lumshe tsumammu idanunta lokacin data tuno Kan nipples dinsa baki makale da qirjinsa suna wani irin sheki mai d’aga hankali haka ta dinga tuno abubuwansa , kallon qirjinsa kad’ai yana sakata jin natsuwa , “wayyolhhly Allah Adnan ka kirani mana Ko zuciyata zata Samu natsuwa ta furta hakan a fili tana kallon saman d’akin . sake lumshe idanunta tai sai ga wasu hawaye sharrrr masu zafi suka gangaro ta gefen idanunta nan take yanayin fitar numfashinta ya sauya ya dawo yana fita da kyar .”
“Allah ka jarabi Adnan da matsanancin qaunata Kamar yadda ka jarabeni da qaunarsa , Allah ka hana zuciyarsa kwancinyar hankali da samun natsuwa Allah ,ka hanashi sukuni da walwala da kwanciyar hankali har sai ya nemi inda nake Allah Allah ….”sai kawai ta kasa karasa maganarta ta fashe da kuka tana Kankame jikinta guri daya tana jin wani felling dinsa na yawo a sansar jikinta.
a lokacin da shi kuwa jaguwa yana can yana sharar baccinsa hankali kwance dan tun da suka dawo daga operation ya kwanta yake bacci bai farka ba sai karfe goma shadaya na dare a hankali ya bud’e kyawawan idanunshi sannan yayi mika a hankali tare da karaton adduar tashi daga bacci “alhamdulillahil ahyana badama amatana wa ilaihin nushur ” ya kai hannu ya lalubo wayoyinsa guda biyu da suke a kashe ya kunna sai d’aya wacce ta kasance a kunne amman kuma a silect take, missed calls dayawa ya gani ciki har dana sadiq kaninsa dana amminsa daga sama yaga sakon text message ta screen din wayarsa ya bud’e nan ya fahimci Ko sakon wacece ,ajiyar zuciya mai sanyi ya sauke tare da tsurawa wayar Ido yana kallon sakonta qirjinsa da jijiyarsa na harbawa da sauri sauri .
cikin sanyin murya yace “kai tanwer kina son damun kanki dayawa ,ban d’auka da wuri haka zaki nemeni ba ,to ma meye abun nema agurina “? ya tambayi kansa yana shafa goshinsa ” ina tausayawa rayuwarki Amman Ke bakya tausayawa kanki, baki san illar soyayya da mutun Irina bane shiyasa kike son kai kanki ga halaka goge text din yayi ,da Kamar yayi blooking dinta dan Karta kara nemansa sai Kuma ya barshi .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button