KUSKUREN BAYA 1 TO 48
” a wasu shekaru da suka gabata anyi wani natsatsen yaro wanda ya taso cikin gata da kulawa, yana da mahaifi da mahaifiya da kane gudu hudu namiji daya mata uku , wahalar duniya tayi musu yawa naci ma da kyar suke samu sai da wannan azzalumin mijin naki yayi nasarar jefa rayuwarsa cikin gararin rayuwar da yasa ya dawo wannan mutumin dake tsaye agabanki , jaguwa ya sake tsuke muryarsa ya cigaba da magana “abinda yasa na dan baki labari ,mijinki ya cancaci na kashe shi bisa girman laifin da yayi min a shekarun da suka gabata sai dai na barshi da halinsa dan hukuncin Allah zai fi akan nawa hukunci ,sai abu na gaba ” idan mijinki yayi kuskuren ko gigin sako jami’an tsaro ciki aikina domin yunkurin tona min asiri ko bincike akaina zan…..
da sauri tace” he wont involved the police farinciki ya ziyarci zuciyar jaguwa saboda ya hango firgici da matsanancin tsoro attare daita, yana gama jin abinda tace yace “shiga muje kou ” Alh tanko gote yayi saurin waigowa gefensa inda Jaguwa ke tsaye fuskarsa da alamun tambaya “karka ɗauka bansan abinda nake ba ,nasan halin mutane azzalumai irinku masu bin mutane da bita da kulli ka shiga muje kawai ban gama da kai ba idan kuma mutsu zaka min yanzu na harbeka na harbe kaina muyi mutuwar kasko ,babu mutsu ya shiga gaba jaguwa na biye dashi har cikin mota ,Jaguwa ya zagaya ya shiga bangaren direba ya tayar ya nufi get ….
Suna karasowa bakin get securities suka tsaida shi warning glass din bangaren Alh tanko gote yayi suna ganinsa suka shiga rigerigen kawo gaisuwa cike da girmamawa, daya daga cikinsu ya bude tafkeken get din estate din jaguwa ya fita …….
Tafiya kaɗan jaguwa yayi ya soma motsa lip’s d’insa “nasan kana mamakin kwarewata kou? tanko gote yayi saurin gyada kanshi ” karka yi mamaki duk acikin rashin imanin daka dasawa zuciyata ne , idan har baka tuba bisa ayyukan da kake shukawa a doron duniya ba, ka zuba ido zaka haɗu da wanda zai daukeka daga doron duniya gabad’aya ..
ya k’arasa maganar yana murmushin gefen baki murmushin dake kashe zuciyar yammata dan duk sanda yayi irin wannan murmushin dole kaji ya shiga ranka sannan a take zaka rikice akanshi ,yayinda shi agurinsa duk sanda yayi irin murmushin to ya samu nasara ne akan aikinsa ,wayarsa ce ta soma babriting ya tura hannunsa d’aya cikin aljihun wandonsa ya ciro wayar sunan Anas ya gani yana yawo akan screen din wayar, maida wayar yayi ya ajiye batare daya ɗauka ba sai da suka fita daga area estate din sannan jaguwa ya tsaida mota a gefen titi “fitar min a mota har yanzu bazan hanaka kiran headquater na police ba ka kira ……..”
Kamar jira yake ya bashi umarni ya bude murfin motar jikinsa na rawa ya fita ya tsaya a gefen titi jaguwa ya fixgi motarsa a guje ya barshi tsaye yana bin bayan motarsa da kallo ….
Bangaren su Anas kuwa sun shiga tashin hankali mara misaltuwa saboda ganin jaguwa yaki ɗaukar kiransu dan babu wanda bai yi amfani da layinsa ba amman jaguwa yaki ɗauka shi ana shi so yake yayi surprise dinsu kusan fitowa suka yi daga cikin gidan suna shawagi a wajen unguwar kowane zuciyarsa cike da matsanancin tashin hankali jubi ne yace “kunga irin halin nasa ko? “Ban san me yasa yake mana haka ba ana kiranshi yana kin ɗauka “karkace haka bakasan halin da yake ci ba a irin tsoron dake estate din ya cancanci fiyye da haka mu dai mu dai ya dawo lafiya shine kwanciyar hankalinmu inji cewar Anas wanda yayi magana hawaye na gangaro masa ….
ita kanta tanweer haka ta kasance zuciyarta na bugawa da karfin gaske ga zazzafan zazzaɓi daya ziyarci jikinta haka nan ta dinga jin wani iri ajikinta idanunta ta lumshe tare da kamkame jikinta guri daya zuwa yanzu zuciyarta cike take da kewar gida ..
Haka ma can gidan minister of health Kuka sosai Hajiya zainab take Alh Abubakar shima kuka yake babu mai rarrashin wani ganin Alh Abubakar na goge hawaye yasa hajiya zainab ta saki wani gigitaccen kuka mai karfi tace “nashiga uku ni Zainab diyar tawa kwaya daya take hannu yan fashi da makami yau kusan kwana biyu Allah idan wani laifi nayi maka ka hukuntani ni kad’ai karka hukunta yarinyata dan batayi laifin komai ba ,saurin toshe bakinta Alh Abubakar yayi “haba zainab karkiyi sabo mana kaddara ce kuma tana kan kowa tanweer will be fine da yarda Allah lafiya zamu ganta ina iyakacin kokarina akan lamarin ta ko ina jami’an tsaron na kan bincike sannan nasa a tsananta addu’a bana jin tanweer na cikin damuwa kamar yadda muke ciki ,nasan killa suna bukatar wasu ƙarin kudade ne daga garemu yasa suka riketa a shirye nake da ko nawa zasu bukata zan mallaka musu komai dana mallaka akan tanweer dan Allah ki kwantar da hankalinki “wani kwantar da hankalinka zanyi ..”?
“Yan fashi da makami sun ɗauke min diyata kwaya daya tal yarinyata mafi soyuwa acikin raina ta yaya kake tunanin zan iya kwantar da hankalina ?
” waɗan nan yan sanda dake rike da case din basu san aikinsu ba basa komai kawai lamuran gabansu suke idan bazasu nemo min yarinyata ba ni na fita na nemota a duk inda take, gabad’aya ta gama fita haiyacinta sambatu kawai take zubawa hawaye na gangarowa daga cikin kwayar idanunta “wayyohlly tanweer ko a wani hali kike ciki” ?”Allah kasa tana cikin koshin lafiya , Allah kasa basu taba min lafiyarta ba ..”
Hajiya Zainab ta zabura daga zaunen da take ta mike tsaye kamar an mintsineta jikinta na wani irin rawa ,ta soma neman police headquater ganin take kamar basa komai akan bincike wasu abubuwa take kamar zarariya ko mahaukaciya sabuwar kamu ..
“Sp me ake ciki akan batun ‘batan yarinyata har yanzu shiru banga aikinku ba ?” idan har haka aikin police yake hakika bashi da wani amfani gareni yau tsawon kwana biyu har yanzu babu wani tsayayyen magana akan batan yarinyata “
“muna kan aiki ranki ya dade ya fadi haka yana cizan gefen lip’s dinsa da tsotsa geyarsa “dakata ni ba wannan na tambayeka ba Kawai inda yarinyata take nake son sani tayi maganar wasu zafafan hawaye na sake wanke mata fuska “ranki ya dade hakuri dai zaki sake yi, babu wata hanya da zamu samu damar gano inda waɗan yan fashi suke sai Kira daga yan fashi domin bukatar wani abu daga gareku ta haka ne kawai zamuyi saurin kamasu ” Alh Abubakar dake tsaye a bayanta a tun sanda ta soma magana yayi gyaran murya ya amshi wayar hannunta yayi disconneting din kiran “kiyi hakuri zainab tayi saurin zubewa ajikinsa tana kuka”yarinyata tanweer ” “inshallahu za’a kamasu nan kusa ,
Dole akamosu sannan dole a hukuntasu da hukunci mai tsanani domin laifinsu daidai yake da wadan da sukayi kisa..
Gudu jaguwa yake akan titi ya yaga wata mota baka kiran marcende C class na bin bayansa duk inda yabi sai motar tabi a karshe ya dauke bakin glass ya rufe kwayar idanunshi ya dauki hanyar da zata kai mutun aja ,gudu yake sosai har ya ‘bacewa motar ya bi wata hanya mai ciyayi ya ja numfashi ya fesar jikinsa na bashi Alh tanko gote ya kira mahaikata, yanzu kam a hankali yake murza stearing motar yana sakin murmushin cin nasara Idanunshi ya ɗan lumshe ya ci-gaba da driving dukkanin alamu ya nuna yana cikin jin dadi ya gama da Tanko gote bai yi tunanin abun zai zo masa cikin sauki ba sai gashi yayi nasara kara lumshe idanunshi yayi …..