KUSKUREN BAYA 1 TO 48
“Nazifi haka mukayi da Kai ?a she baka da amana ban sani ba ? ya rufe shi da fad’a ta Inda yake shiga ba ta nan yake fita ba cike da matsanacin firgici nazifi yace “dady me nayi Maka ? bangane me kayi min ba ? ya tambayesa yana maxurai “,ni zakawa tambayar rainin hakali ? to yau duk a zaune naga Ibrahim alhalin na fad’a maka bana son ganinsa a zaune sai akwance dan lokacin tashinsa bai yi ba tukun “sai lokacin nazifi ya fahimci rashin amanar da yayi masa . ya shafa sumar Kansa yana cewa “Allah dady Ina iyakacin k’okarina Ina yin komai yadda ya kamata alluran da na saba yi masa shi nake masa haka zalika maganin da yake sha shi nake kawo wa ban canza ba “.
“wannan karya ne nazifi “da gaske dady baza yi maka haka ba ,ai duk abinda kace shi zanyi tunda ka zabi abarshi cikin wannan yanayin ni me zaisa naki?” ai ya zama dole nabi
duk wani umarninka bayan haka ma duk sati sakokan na shigowa account dina ,nafi tunanin yawon magani da allurar da ake masa ne yasa suka daina aiki ajikinsa Ina ganin me zai hana a canza masa ? “. ya fad’a yana tsine masa acikin zuciyarsa domin kuwa mutane masu hali irin na alhj Tahir sam basu ya kamata su haifi d’a irin Ibrahim ba. “to shikenan na d’auka kana cin amanata ne ?Ina ai bazan ta’ba cin amanarka ba wannan ai sirri ne a tsakaninmu ” alhj Tahir yayi murmushin jin dadi yana cewa “to yanzu kana ganin idan an canza masa za’a samu me karfin na farko ?”sosai kuwa za’a samu zan duba me karfi wanda yafi na farko zuwa gobe sai nazo dashi “to shikenan na gode son Allah yayi maka albarka ya Kai hannu ya zagaye kafad’an nazifi yana tafiya dashi acikin falonsa” ka cigaba da bin umarninna ni Kuma bazan gaji da tura maka sakona ba “nazifi ya gyada masa Kai tare cewa “babu komai dady ai ko baka biyani ba ya zama dole nabi duk wani umarninka nasan kana da wata munafa me kyau akan ib shiyasa kake bukatar ganinsa akwance ?”.
“yauwa nazifi a she kana da fahimta ?” shi yasa kullum kake kara burgeni saboda kaifin baseerarka” cike da girmamawa nazifi yayi sallama da alhj Tahir ya fito zuwa babban falon gidan Inda ya iske hajiya baseera zaune kusa da Ibrahim dake zaune akan wheelchair tana bashi abinci a baki tausayinta dana Ibrahim ya kamashi ,mace har mace me tausayi da biyayya amman batayi sa’ar miji ba “har ka fito nazifi ? “eh mumy na fito “to sannu da kokari Allah yayi muku albarka gbdy , yadda kake kula da abokinka baka gajiya Allah ya kula da lamarinka “Ameen mumy ai kula da ib ya zama dole , Ibrahim ya dubesa wuyansa a karye magana yake son yiwa amininsa amman ya kasa furta Komai so yake ya sheida masa Kiran daya samu daga bakin alqali a kwanakin da suka gabata .
sai da nazifi ya sake duba jikin Ibrahim sannan ya fito zuwa haraban gidan ya shiga motarsa ya zauna ya bata wuta, tafiya kad’an yayi ya gangara gefen titi yayi parking ya Kasa cire hannunwansa akan stearing motar ya shiga kogin tunani ta yarda alhj Tahir yake wa dan lelensa wanda shi kad’ai ya haifa a duniya mugunta.ji yake kamar ya tattara ib da komai nashi ya turasa zuwa kasar england domin ya samu kulawa daga manya likitoci , dan allurar da mahaifinsa yake sa shi yayi masa bata da maraba da poising me karya garkuwar jiki gashi sanadiyyar haka an tsaida komai nashi bayan shi din mutum ne mai qulafucin akan aikinsa”gbdy zuwa yanzu ya soma zargin manufar alhj Tahir akan d’ansa Ibrahim, idan kuwa haka ne babu shakka akwai lauje cikin nadi wato akwai saka hannun alhj Tahir cikin kidnappin din tanweer da yan fashi suka yi .
“haka ne ma zuciyarsa ta tabbatar masa da hakan , wannan dalilin yasa alhj Tahir baya son Ibrahim ya tashi bisa kafafunsa ya nemi tanweer da karfin da iKon da Allah ya bashi, tabbas Ibrahim nada gogewa da jajircewa da qulafici akan aikinsa da duk wasu masu laifi a kasar nan.
” idan ya gangara ta bangaren aikin sirri shine kan gaba saboda kwarewarsa ya iya binciken sirri tamkar aljani tare da abokan aikinsa har su gano me laifi yanzu abinda zai yi zai cigaba da boyewa alhj tahir tare da biye masa har sanda zai kammala komai akan abinda yake zarginsa akanshi tare da nemo sheidu masu karfi ta yadda za’a samu nasarar kamashi a sikwane , yana da tabbacin muddin aka kamashi za’a kama ragowar abokan sana’ar tasa dukkaninsu su girbi abunda suka shuka ya kusan awa d’aya agurin yana saka da warwara har hawayen tausayin Ibrahim ya zubar saboda rashin dacen mahaifi da yayi sannan ya tada motarsa zuwa office dinsa har ya Isa office tunanin aminisa yake ..”
Tanweer bata farka ba sai gurin karfe d’aya na rana ta farka cike da matsanacin azaban ciwo dan ta sha wahala sosai jikinta na rawa koina ciwo yake mata sai numfashin wahala take fitarwa , wani abu ya hadiye sannan ya matso kusa daita sosai ta bud’e idanunta da suka mata nauyi ta ga shine zaune a kusa daita wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka, muryarsa a kasalance yace “lafiya kike kuka me ya sameki ? ya fad’i haka ne dan ya sake tabbatar da tana sane da abinda ya faru a daren jiya duk da baya doubt akan gaskiyar abinda baba ya fad’a masa .ta fashe da wani sabon kuka tana cewa “nima bansani ba amman duk ilahirin jikina ciwo yake min tunda nake ban ta’ba Jin irin wannan ciwon ba dan Allah ka taimakeni ka maidani gida …..” ta k’arasa maganar tana sheshekar kuka bai sake yin magana ba ya ɗauketa cak ya nufi bayi daita ya had’a mata ruwan zafi ya Kai hannu zai riko hannunta ta goce ya bita da wani kallo.
ta zabga masa harara tana hura masa hanci ,shiru yayi yana cigaba da kallonta yayinda kukanta yaki tsayawa ganin ko ya rarrasheta ‘bata bakinsa zai yi yasa a hankali ya Isa Inda take jingine acikin bayin ,batayi expecting ba taji ya rungumeta ajikinsa tsam , ajiyar zuciya ta saki ta had’e rai sosai .