KUSKUREN BAYA 1 TO 48
A hankali ya shiga d’akinsa Kai tsaye had’ad’d’en bayinsa ya nufa ya tsaya gaban mirrow Wanda ke hade da washing hand basing ya fara wanke fuskarsa a hankali qirjinsa na wani irin bugawa da karfin gaske , sai da yayi minti biyar duke sannan ya d’ago fuskarsa kwance da ruwa, fuskar nan nashi a had’e tamkar hadari ya tsurawa mirrow bayin Idanunsa yana kallon kyakkyawar fuskarsa yana zurfafa tunanin yadda zai yi da tanweer arayuwarsa shi kansa ya fahimci yarinyar ta fara tasiri a zuciyarsa amman zai yakiceta ta karfin tsiya .a naste ya soma daga kafafunsa ya fito zuwa falonsa ya karasa gaban fridge ya bude ya tsurawa lemunka dake jere idanunshi yayinda zuciyarsa ke tafarfasa da quna baya jin daya daga cikin lemunka zasu sanyaya masa zuciya yana Jin kamar yasa akawo msa giya mai sanyi ya kwankwad’a ko zuciyarsa zatayi sanyi ,sai yanzu yake nadamar sanin ko shi waye da tayi shiru yayi agurin yana tunanin mafuta .”
Ita Kuwa tanweer sai data ci kuka mai isarta sannan ta tashi ta fad’a bayi ta cika bathtub da ruwa ta shiga ta kwanta lamo cikin ruwa tana sauke ajiyar zuciya ta d’auki tsawon lokaci tana tunanin yadda zata gudu ta bar gidan “idan na tafi ya zanyi da matsanacin soyayyar da nake masa ?tsaki taja” soyayyar banza karki yarda ki biyewa wata soyayya ki cutar da kanki ,a yanzu tsana ce ya kamata ya maye gurbin soyayyar, ta dade acikin bayin sannan ta fito daf da magariba , yana shigowa tana fitowa daga bayi ya tsaya ajikin kofa d’akin yana aika mata da wani irin kallo me kashe gabobin jiki ,kallonta yake yana kallon santala santalar cinyoyinta dake fitar da sheki .
a hankali yayiwa Kansa mazauni agefen gado tare da jingina rabin jikinsa da filo yayi mugun tsura mata Ido , kallo d’aya tayi masa ta d’auke idanunta akansa qirjinta na wani irin bugawa da karfin gaske ,a halin yanzu kallosa ma storon yake bata ko ma tace bata qaunar ganinsa kyawun dan maciji garesa tunda babu hali , cikin sauri ta d’auki kayanta ta sake shiga bayi.
shiru yayi zaune yana kallon d’akin har kusan bakwai da wani abu bata fita ba , ganin bata da niyyar fitowa ga lokacin sallah na ƙoƙarin wucewa ya tashi ya fice ..”
Da misalin karfe tara na dare ya shigo d’akin sanye da kananan kaya army green riga da wando three quarter ,kafafunsa sanye da farin silifas , hannunsa d’aure da agogon silver sai kamshi jikinsa yake fitarwa , ya kawo mata abinci ya ajiye akan table zai fita tace “dama ka dawo ka d’auki d’an iskan abincinka dan wallahi bazan ci ba gara na mutu da yunwa dana Kara cin abun hannun dan fashi.” banza yay mata tare da jan tsaki ya sake d’aga kafafunsa yana soke hannunsa cikin aljihu “dan Allah karki ci idan yunwa ta kasheki bani da hasara, ni mu hudu ne agurin mahaifiyata kefa ? ya karasa maganar tare da juyowa gbdy ya fuskanceta sosai , Ido cikin Ido suke kallon kwayar idanun junansu ” idan kin mutu iyayenki kikawa hasara sannan karki dauka idan kin mutu ni jaguwa zan kaiwa iyayenki gawarki , no a ruwan teku zan watsaki kifaye suyi wuf da gangar jikinki “. Ai ko gama rufe baki bai yi ba ta bare baki ta fara kukan shagwa’ba “Allah ya Isa tsakanina da Kai mugu azalumin sai Allah ya saka min “. bai sake saurarata ba ya kama gabansa yana jan dogon tsaki .”
Bangaren ammi kuwa har qarfe goma saura na dare tana jiran Kiran Adnan dinta da yace ta jirashi kome dare kar tayi bacci zai kira ,ta tashi daga falonta ta shiga dakinta dan tuni yaranta sun shige d’akinsu ta fara shirin bacci har ta gama shirin bacci bata ga Kiran Adnan dinta ba tai shiru tana tunaninsa “ai har yanzu da sauran lokaci bari naga bugawar 11 idan bai kirani ba sai na kirasa “.ta kwanta akan gado tana ambaton sunan Allah kwanciyarta ke da wuya sai ga kiransa ya shigo ta d’auka had’e da sallama byn ya amsa “tace yanzu na gama maganarka a zuciyata , “okay fatan dai Lafiya yasu shafiq da hally “duk muna lafiya ya aikin ? “Alhamdulillah ammina yau dai naji jiki sosai , gbdy jikina ciwo yake kamar na taho gida “ai kaga irinta shiyasa kaga na damu kayi aure Adnan bamu da lokaci idan kaji ance babu lokaci to mutuwa ake nufi zata iya zuwa ma mutun Ako wani lokaci ,baka rasa komai ba , Allah ya rufa maka asirin da zaka iya ajiye mata hud’u a karkashinka me yasa bazakayi ba ?”,zanyi ammin inshallahu nan kusa “ko na nemo maka mata ?shiru yayi ya kasa ce mata “eh ! sannan ya kasa cewa a’a
“Kayi shiru kana jina idan na nemo maka ne sai na bazama ko cikin ya’yan kawaye da dangi ne na nema irin wacce nake so ? murmushin gefen baki yayi kana yace “duk yadda kikayi daidai ne ammina zabinki abun so ne , hira sukayi sosai na tsakanin uwa da d’a Wanda hakan ya sanyaya zuciyarsa ya dan ji damuwarsa ta Kau, sun dan jima suna hira sannan sukayi sallama .”
zahra basu Isa garin Edo ba sai gurin karfe goma da wani Abu na dare kasancewar motarsu bata samu passger da wuri ba gashi motar tayita tsayawa a hanya dan haka basu yi tunanin zuwa gurin boka ba sai suka kama hotel , washegari kuwa karfe shida a gidan boka tayi musu, tunda suka shiga cikin gidan bokan gaban Zahra ke fad’uwa , sun iske mutane dayawa da manya motoci parke a haraban gurin ta sha mamaki ganin lokacin da suka zo amman still sai da suka tarar da mutane ,suka k’arasa gurin amsar kati suka amsa suka samu guri suka zauna suna tautauna akan matsalarta , a hankali har layi ya kawo kansu suka mike suka nufi d’akin da bokan yake aikinsa , da baya da baya suka shiga wanda haka dokarsa take ba’a shiga ta gaba sai da baya .
babu komai ajikin bokan sai wani gaye da yasa ya rufe gabansa dashi suna k’arasa shiga cikin d’akin suka fuskancesa sannan suka buga kafarsu na hagu sau uku wanda shima kaida ne ga duk wanda yazo sai yayi.
da hannu yayi musu alama da gurin zama suka zauna shi kuma ya fuskanci gunki dake daskare a gefensa mai yatsu bila’adadin fuskar gunki kamar na aljanu gbdy ilahirin jikin gunki jini ne kuma na mutane .
Blessing ta bud’e baki zata fara masa bayani ya d’aga mata hannu “karki fara cewa komai ni ne shad’anin boka, bokan da baya gudun mutuwa sai dai mutuwa ta gujeshi, bokan da ba’a fad’awa abinda zai faru sai dai ya fad’a “kin kawo kawarki adalilin tana son ta mallaki zuciyar saurayinta wanda shi a halin yanzu zuciyarsa naga diyar minister of health ,zahra da blessing sukayi shiru gabansu na faduwa barin zahra da hankalinta yay mugu mugun tashi jin zuciyar jaguwa ta kamu da soyayyar yarinyar”.