KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Ya mike tsaye ya goya hannuwansa duka a bayansa ya soma zariya acikin d’akin yana zurfafa tunaninsa ” yanzu ba lokacin tunanin wata tanweer bace , kamata yayi ka tsaya kayi tunanin akan yadda dcp ya samu number wayarka Kai tsaye , hannuwansa dake goye abayansa ya cire ya zura cikin ajihun wandonsa yana cigaba da taku kafin daga bisani ya soma cire rigar jikinsa ya Saura daga shi sai far singlet da dogon wando a hankali ya kira sunan anas “anas…!
ya amsa da na’am yana dubansa “had’omin kan mutanen gidan nan  gbdy Ina da magana dasu .” Yana gama fadar hk ya shige bayi shi Kuma anas ya nufi kofa fitar da sauri zuwa falon baya inda ya iske su jubi zaune suna shan tabar wiwi kowannensu idanunsu yayi jajur sannan d’aya byn d’aya ya tattara kowa ya sanar dasu sakon jaguwa . “

A babban parlour jaguwa suka had’u Suka zauna zaman jiran karasowarsa ya fito yana taku a hankali yana shafa qirjinsa yana kare masu kallo d’aya byn d’aya yana masu kallo mai cike da tunhuma tunda suka ga yanayinsa kowannensu ya sha jinin jikinsa bare jamin sirrin dake tare dasu Wanda yafi kowa shiga tashin hankali da fargaba sai dai yayi k’okarin daidaita natsuwarsa dan karsu ganoshi .
a diririce yake amman ba lallai ka fahimci hakan ba sai kwararen ma’aikaci irinsa ne kawai zai iya ganosa .
sosai jaguwa ya had’e girar sama data kasa kafin daga baya a hankali muryarsa ta fito amman cike da tsawa “wa nene acikinku ya siyar da number wayata “?.
Shiru sukayi gbdynsu suna kallon junansu har sai daya sake maimaitawa sannan jikinsu na rawa duk sukace basu bane.
a tsawace ya dakatar dasu da hannunsa “karya kuke anas koma can ya fad’a yana nunawa anas gefensa “wannan kawai zuciyata zata iya cirewa acikinku Amman gbdynku ban yarda daku ba dan haka a fad’a min gsky kafin nayi kwakkwaran bincike na gano Wanda keda hannu cikin wannan aika aikan na aikashi lahira “.
“Haba jaguwa mu da Kai da anas fa duk Abu daya me yasa zaka dinga ware anas acikinmu idan Kuma ya zamo anas din ne ya bada numberka fa?”
“Impossible anas can’t do that to me bazai ta’ba min haka ba” kana da dalilin da yasa ka tunhumemu ne ? Ko kuwa mun ta’ba cin amanarka ne dayasa ka ware anas ka barmu?inji cewar jubi da ransa yafi na kowa dungunzuma.
Shiru jaguwa yayi dan bashi da wani dalilin dayasa ya tunhumesu ban da anas .
Sai daya furzar da iska mai zafi sannan yace bani da wani dalili amman muddin na sameku da haintata wallahi sai na kasheku daya bayan daya na binneku acikin gidan nan ya k’arasa maganar yana tsaida idanunshi akan mai gadinsa da sauri yayi kasa da Kansa dan bazai juri kallon jaguwa ba duk da shi din ba wai mai laifi bane .
parlour ya d’auki shiru yana cigaba da dubansa yana nazarin wasu abubuwa sai dai nan take gabansa ya cigaba da fad’uwar da yake anas ya matso kusa dashi ya riko tsintsiyar hannunsa cikin nashi sannan ya zaunar dashi akan d’aya daga cikin kujerun falon yana cewa “ka daina zargin su dan Allah , kamata yayi kayi tunanin mai zurfi akan lamarin , “mai ma yasa baka fad’a min ba tun a d’aki domin muyi tunani a tare domin mu san ta inda matsalar take ? ” Sam banji dadin abinda kayi ba dan bana zarginsu da aikata hakan ya k’arasa maganar tare da karasawa ya bud’e fridge ya d’auko kwalban wine mai sanyi ya balle ya siyaya a glass cup ya Mika masa” ungo ka Sha kaji sanyi sarkin rigima kawai idan baka d’aga hankalin mutane ba baka samun natsuwa”.
jiki a sanyaye jaguwa ya amsa cup din ya rike sai dai ya kasa sha sakamako kwakwaluwarsa data Lula duniyar tunani .
Anas ya juya ya fuskance su jubi “dan Allah Kuyi hakuri karkuyi fushi dashi Kun rigada kunsan halinsa idan ransa ya baci babu abinda bayayi dan yaga ya huce akan mutane ni daku duk abu d’aya ne agurinsa babu wani bambamci .
wani irin mugun kallo suka masa mai tattare da tsananin bacin rai suna jin kamar su shake masa wuya agurin su aika sa lahira, babu wanda yace uffan acikinsu illa juyawa da sukayi suka bar falon cikin tsananin damuwa.”
anas ya dafa goshi yana furzar da numfashi sannan ya dawo Inda jaguwa yake zaune “Adnan dan Allah ka daina nuna Kafi qaunata akan sauran abokanmu , tsakani da Allah ni banga abun wariya aciki ba tunda kana zargine kamata yayi kayi zargin har dani ,kawai giyar soyayya na dibarka kazo kana wa mutane shirmen banza ” tunda anas ya fara magana yake ta jan tsaki aransa kafin daga baya ya mike yace “Kamin shiru anas karka dameni da hauka idan ba haka ba zan fasa maka Kai yanzu ya fad’a yana zaro bindiga pesto a bayan wandonsa ya saita Kansa yana huci .”ka harbeni mana”. anas ya fad’a yana dubansa cike da fushi, jaguwa ya turesa kan kujera ya ijiye bindigar hannunsa ya fito yana tsuma kamar wani mayuncin zaki Kai tsaye gurin shakatawa ya nufa Yana sake shiga duniya tunani Dan dole so yake sai gano inda dcp ya samu numbersa .”

Tafiya minister yake a hankali yana jan tanweer da hira cikin hikima yake tambayarta abubuwa da suka faru daita, ita Kuma tana bashi amsa tare da Allah Allah su k’arasa gida ta ga mumynta , shi kuwa a ransa ba gida yake da burin kaita ba hospital zai zarce daita tukun nan
domin a bincika masa lafiyarta . kafin ya karaso cikin gari tuni bacci ya d’auke tanweer sakamakon hodop din da suka tarar a hanya , a hankali ya waiga bangaren da take zaune ta d’aura kanta a saman kafad’arsa yaga bacci take da alamun ma yayi nisa ya shafa gefen fuskarta cike da matsanacin farinciki yana sauke naunayen ajiyar zuciya .
A bakin had’add’en get din ST hospital ya tsaya tare yin hon masu gadi suka Bud’e masa tafkeken get din ya sanyo hancin motarsa ciki .
yana gama daidaita parking ya cire kanta a saman kafad’arsa har lokacin bata Farka ba dan haka ya kwantar daita akan kujera ya fito ya bud’e Inda take zaune ya cirota ya sa’bata a kafad’arsa ya nufi cikin hospital din daita , yayi tunanin kawo wannan hospital din ne bai kaita nashi Wanda ya mallaka Mata ba dan rufawa kai asiri domin acan duk bincike da za’a yi ba lallai bane ace wasu daga cikin likitocin bazasu sani ba.”
Duk da dare ne amman daga cikin mutane sun fahimci minister lfy ne da Ido kawai jama’a suka dinga binsa .

Har karfe goma sha biyu saura na dare hjy Zainab bata ga shigowar minister ba zuciyarta cike da mamakin Inda ya tafi a daidai wannan lokacin dan rabon da yayi nisan kiwo irin haka har ta manta tun kafin a d’auke tanweer.
ta kira dukkanin layukansa basa shiga abu daya ake fad’a mata switch off gashi bazata iya runtsawa batare datasan halin da yake ciki ba.
tana cikin wannan halin sai ga wayarta ta soma ringing cike da tsinkewar zuciya ta Kai hannu kan bedside dinta Inda wayar take ajiye ta d’auka tana duba screen din wayar sunan minister ta gani yana yawo da sauri ta d’auka tare da Jan Koren madanni ta manna wayar a kunnenta tana furta “Assalamu alaikum”. bai tsaya amsa mata sallamarta ba yace “ki shirya yanzu dolapo zaizo ya daukeki ya kawoki ST hospital”. “Hospital Kuma”? “Lafiya ?
“waye bashi da Lafiya? ta furta a lokaci daya muryarta na rawa. “karki damu idan kinzo zakiga ko waye bashi da Lafiya “a’a dan Allah ka fad’a min wallahi gbdy ka d’aga min hankali gabana banda faduwa babu abinda yake a yanzu . “Kai Zainab matsalata dake kenan saurin d’aukar abu da zafi kiyi abinda nace dolapo zai zo ya daukeki. “banason irin haka fa kasan a yanzu komai na iya faruwa dani, ni dai ka fad’a min nasani tun kafin nazo “nima banason yadda kike d’aga min hankalinki ki karaso zaki ga komai yana gama fadar haka yayi disconnecting din Kiran hankalinta a matukar tashe ta mike ta soma shiri, tun kafin dolapo ya karaso har ta gama ta fito suka d’auki hanya cikin kankanin lokaci suka karaso hospital dolapo na gaba tana biye dashi Allah Allah take takaraso taga waye bashi da Lafiya.
dolapo bai tsaya a koina ba sai a bakin kofar d’akin da minister yayi masa kwatance yasa hannu ya kwankwasa kofar daga cikin d’akin aka bada umarmin shigowa ya tura kofar batare daya shiga ba sai hjy Zainab ce ta sa Kai ciki d’akin tana shiga dakin idanunta suka sauka akan tilon diyar kwance Kamar a mafarki kusan mutuwar tsaye tayi kafin daga bisani ta dafe bangon d’akin ta manne sosai tana murza idanunta da hannunwata duka ” .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button