KUSKUREN BAYA 1 TO 48
sadiq yayi murmushi yana kallon tan wacce ta dago ta kalli jaguwa sannan ta d’auke kanta ita dai addua take har lokacin ,shi kuwa sadiq ya kasa hakuri hakan ya tsinci kanshi da cewa “aunty nah ya jikin naki?” ya sake tambayeta cike da kulawa.” da sauƙi!” ta basa amsa murya a sanyaye a natse sadiq ya soma haɗa kayan aikin da zai mata amfani dashi yana gama had’awa yace “miko hnnunki shiru tayi Taki mika masa sadiq ya
kalli yayansa, jaguwa ya wani haɗe fuska yace “kiyi abinda yace mana karki batawa mutane lokaci “
Hawayen dake makale a kwarnin idanunta suka zubo duk da kasancewarta likita amman Allah yayita da tsananin tsoron allura muryarta na rawa tace “ni…ni banason allura a bani magani “.
“dole kiso allura ko mutuwa zakiyi sai an Miki ” cikin sanyin jiki sadiq yace “, father ka bita a hankali kasan mata akwai su da mugun tsoron allura “rabu daita munafurcin ne kawai ita kanta likita ce mutane nawa tayiwa allura? murmushi sadiq ya sake yi yana cewa ” aha ai likitocin nan sun fi kowa shegen tsoron allura ganin tana ta bata musu lokaci yasa jaguwa kamo hannunta tare da matseta gam ajikinsa “bismillah sadiq kayi mata allura ” sadiq ya soma k’okarin tsira mata ta makale ajikin jaguwa sosai tare da sakin K’ara mara sauti ,wani irin harbawa jijiyar jaguwa tayi da karfi take yanayinsa ya sauya bayan hk wani sanyi yaji yana taso masa tarayyarsu ta shekaranjiya ce ta dawo masa a hankali tsigar jikinsa suka dinga mkewa gbdy ya nemi natsuwarsa ya rasa ana gama mata allurar ya saketa dan idan suka cigaba da kasancewa haka komai zai iya faruwa dan zai iya danneta a office din.
sadiq ya had’a mata maganunguna har dana zazzabi ya mika mata yana sake mata Sannu jaguwa yayi masa sallama suka fito kmr farkon da zasu shiga yanzu ma hakan ce ta kasance taji kmr ta fixge daga hannunta ta kwasa da gudu .”
suka karaso Inda sukayi parking suka tsaya abakin mota kamar ya sani ya bude mata sai data shiga ta zauna ya kulle sannan ya zagaya ya shiga bai zauna ba sai daya d’auke wayarsa
ya zauna yana danna gefenta yayi mamakin ganin wayar a kashe ya kunna ya ajiye a ma’ajinta tare da yiwa motar key ko cikakken minti biyar bayi da kunna wayar ba kira shigo da sauri zuciyar tanweer ya shiga bugawa da karfi .
ta kame guri d’aya ya d’auki wayar da hannun d’aya yana dubawa yayinda hannunsa ke kan stearing yana tuki sunan Abubakar Hamid ya gani yana yawo akan screen din wayar da yake yana da truculler a wayarsa ,bai gane ko waye ba ya dai d’auki wayar yana dauka yaji saitin muryar hade da Kiran sunan tanweer …!wani wawon burki yaja a tsakiyar titi ya waigo yana kallonta “tanweer !!! are you okay ? shiru cikin tsananin tashin hankali minister yace “Talk to dady tan where are you ? “Inna lillahi ta furta a fili tare da juyowa da sauri Jin sautin muryar mahaifinta dake fita cikin tsananin tashin hankali .
Kit jaguwa ya katse Kiran tare da ɗauketa da barin makauniyar take hancinta ya balle da jini ,wani kuka ta saki mai ban tausayi ta bud’e baki zata yi mgn ya sake yarfa mata wani mari wannan karon gilmawar duhu ta gani acikin kwayar idanunta ta sake fashewa da wani sabon kuka tana neman d’auki tana kallonsa ya bud’e bayan wayar ya cire sim din ciki ya karya ya watsa a bakinsa ….”
????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
????️17
A matukar fusace ya bawa motar wuta gabansa banda fad’uwa babu abinda yake , ita Kuwa kuka take sosai kamar ranta zai fita .
zuciyarsa ke wani irin ciwo da zafi dan idan akwai abinda ya tsani gani shine zubar hawayenta sai dai a halin yanzu baya jin zai iya rarrasheta ,zai jure Jin zafin saukar hawayenta .hannunta ta Kai kan hannunsa ta rike gam hawaye shabe shabe kwance a fuskarta ,
da sauri ya waigo fuskarsa ya kalleta yana zabga mata katuwar harara ,gashi fuskarsa gbdy babu annuri , cikin muryar kuka ta kira sunansa “Adnan ‘!
Yana jin ta yayi mata banza tare da d’auke kanshi ya maida kan tukin da yake yana jan dogon tsaki “me yasa Adnan ? ” me yasa bazaka maidani gidanmu ba ?”
Shiru yayi yaki ce mata Komai dan ko yace zai yi magana muryarsa bazata fito ba saboda ‘bacin rai dake daskare a zuciyarsa ,zubewa tayi ajikinsa ta saki wani sabon kuka me tsuma zuciya tana cewa “kayiwa Allah da manzonsa ka maidani gidanmu nagaji ! nagaji !! ” .
bai ce ta daina kukan ba haka zalika bai ce ta bar jikinsa ba ya barta tayi kukanta , shi Kuma ya cigaba da falfala gudu akan titi .”
Bangaren minister kuwa cikin lokacin da bai wuce minti biyu
da yaji wayar farko da sukayi da tanweer ta mutu ba ya soma neman number din commissioner batare da bata lokaci ba ya d’auka nan minister ya shiga zayyano masa abinda ke faruwa . cikin sauri commissioner ya katse Kiran ya kira dcp dake rike da halakin kula da binciken tanweer kafin kace me jimi’an tsaro sun hallara a gabansa ,cike da natsuwa ya soma magana “please ku maida hankali sosai yanzu nan minster yace sun gama waya da diyarsa tana 1829 amman ga number data kirasa dashi ya turo mana ku tafi kuna tracking din number ku samu location Inda gurin yake .
Nan take dcp ya amshi number suka fito cikin sauri suka shiga motocinsu suna tracking din number sai dai yaki nuna musu location saboda number bata shiga gbdy bare su samu location din da akayi amfani da wayar har suka hau babban titi .
dcp ya kira commissioner yana d’auka yace “sir layin nan bai shiga ba bare mu samu locacin din Inda suke amman zamu k’arasa 1829 plaza dake igando ko zamu dace a nan akayi amfani da layin yanzu dai zamu cigaba da Kiran layin har mu Isa .”Allah yasa ba fahimta yayi ya kashe wayar ba ? “Dan Allah kuyi aiki yadda ya kamata dan yarinyar ta kira cikin mawuyacin hali da alamun tana cikin tsaka me wuya, wannan wata dama ce me kyau da muka samu kada ku bari ta subuce mana “okay sir inshallahu zamuyi iyakacin k’ok’arinmu “.
Commissioner ya katse Kiran yana juyi akan kujera gashi dai shirin tafiya gida yake Kiran minister ya same shi Amman a yanzu ya zama dole ya fasa tafiya gida ya zauna zaman jiransu idan ta kama ya kwana ma a office zai yi “.