KUSKUREN BAYA 1 TO 48
*“
bangaren Zahra kuwa daren ranar kasa bacci tayi tana zaune cikin tsananin tashin hankalin data tsinci kanta dan gbdy ta kasa runtsawa data runtse idanunta da zumar bacci jaguwa take gani tare da yarinyar da bata san ko sunanta ba , daf da asuba bacci ya fixgeta a matukar firgice ta farka ta zauna tana haki , jikinta ya d’auki zafi kmr garwashin wuta tsinuwa kuwa ta tsinewa yarinyar yafi sai babu adadi daga karshe ta rushe da matsanacin kuka “wayyohhhly Allah naci amanar kaina , na yaudari kaina dana d’auki soyayyar duniya na daura ma Adnan kuka take sosai har da shesheka, bazan taba barinka haka ba sai na tabbatar da na kawar da hankalin kowace mace akanka tsam ta sauko daga kan katifa ta jingina jikinta da bangon d’akin ta runtse idanunta masu zubar da zafafan hawaye masu zafin gaske tana Neman mafuta.
wata zuciyar na bata shawarar ta hakura dashi yayinda wata zuciyar ke karfafa mata gwiwar tabi kowace hanya dan ta mallaki jaguwa sosai tayi zurfi cikin tsananin tunani da tashin hankali ,babu wacce tazo mata sai kawarta blessing da suka had’u a shurem blessing yar asalin edo state ce akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu blessing ta sha bata shawara ta dinga binta zuwa garinsu idan zata domin ta had’ata da manyan bokaye dan ta qara samun d’aukaka a harka karuwanci amman taki naunayen ajiyar zuciya ta sauke na samun mafuta dan kuwa tasan blessing zata taimaka mata tun da asuban fari ta kirata tana kuka ta sheida mata halin da take ciki take blessing tace “ki shirya kawai ki zo muje garinmu na gode blessing ai muddin kika min wannan taimakon bazan taba mantawa dake ba “karki damu zahra ai wannan ba wani abu bane amman Ina tabbatar miki muddin na Kai ki gurin malamai sai yadda kikayi da jaguwa sai ya zamo tamkar bawanki “na gode na gode “,Kai haba Zahra ai mun zama daya tuntuni kece dai baki d’auki hakan ba ki shirya mu hadu a iyanapaja dan Ina royal stream hotel nan kwana zan k’arasa na siya mana ticket kafin kizo “okay sai nazo cikin saurin ta soma shirinta tana jin sanyi da natsuwar zuciya.”
Mika jaguwa yayi had’e da salati Ya sake kwakumeta tsam ajikinsa yana sauke numfashi a hankali kmr bazai bud’e Idanunsa ba amman dole ya bud’e sakamakon wayarsa dake Kiran sallah alamun lokacin sallah yayi ya bud’e tsumammamun idanunshi ya kunna wutar d’akin wanda yasa ta d’an motsa tana shigewa jikinsa hade da d’aura hannunta akan chest Kuma daidai nipples dinsa sauri d’auke numfashi yayi gabansa na faduwa yayi shiru na tsawon lokaci yana tunaninta abubuwa dayawa akan yarinyar ya d’an dade kwance idanunshi biyu sannan ya cire hannunta a chest dinsa ya sauko a natse ya karasa Inda wayoyinsa suke ya d’auki daya yana dubawa karfe bakwai saura na safe bai so wannan lokacin ya taddashi a hotel din ba shi daya so tun asuban fari ya bar hotel din Kai tsaye bayi ya shiga ya fara da sakarwa jikinsa ruwa sannan ya dauro alwala ya fito ya saka kayansa ya Kalli gabas ya tadda sallah byn ya idar ya mike ya Isa Inda take kwance ya Kai hannuwansa tsakiyar kafafunta yana shafawa a hankali ta bud’e idanunta sakamakon jin damshin ruwan hannunsa na ratsata idanunshi cikin nata yace “tashi kiyi sallah lokaci na tafiya ta janyo bargo ta lullu’be jikinta sosai dan babu komai ajikinta muryarta can kasa tace “okay ka miko min towel na d’aura “Dan Allah malama ki tashi kije dauka karki bata min lokaci ya k’arasa maganar a fusace shagwabe fuska tayi kmr zatayi kuka “babu komai ajikina fa tsaki yaja ya mike ya janyo towel ajikin kofar bayi ya jefa mata a fuska ta d’aura ta soma k’okarin saukowa “kiyi sauri please Ina da appointment ya fad’a kwayar idanunshi na kanta bata ce Komai ba ta nufi bayi yabi bayanta da kallo yana kallon every step of her komai nata dabam ne ta had’u sosai ilarta dai rashin kunya har ta shige bayi idanunshi na kanta itama sai data yi wanka sannan ta dauro alwala ta fito a lokaci da yake waya da anas “karka damu ku bani minti ashirin yanzu zaku gani murmushi yayi yace “Kai anas me yasa ka fiyye damun kanka nace maka ba abinda kake tunani bane shikenan koma dai menene ba abinda kake zato bane ya katse Kiran ya kira ammina Inda yake sheida mata Yana da aiki me mahimmancin da zashi shi da abokan aikinsa yana bukatar adduarta”Allah ya tsareku yasa ayi aiki cikin nasara amman dan Allah kabi a hankali kasan Kai ne rayuwarmu sannan da zarar ka kammala da komai kazo
naganka karka ce sai karshen sati zaka zo gbdy “karki damu ammi inshallahu bazan Kai ba me zan taho Miki dashi ?”.Shiru tayi tana tunanin kafin daga baya tace “komai ka kawo amminka zatayi farinciki murmushi yayi yace “shikenan my happiness murmushi tayi daga bangarenta ta sake Aiko masa da addua komai dare idan na dawo zan kiraki karki yi bacci har sai Kinga kirana kinji ammina tace “to Adnan inshallahu zan jira kiranka sun d’auki minti biyar suna waya har da kannensa ,sanda tanweer ta kammala shirinta taja ta tsaya tana kare masa kallon tsab yana matukar burgeta yadda bai wasa da lamarin mahaifiyarsa da kannensa a dan zamanta dashi ta fahimci yadda yake mugu mugun son mahaifiyarsa har sanda ya k’araso gareta ya riko tsintsiyar hannunta tana can duniyar tunani kumatunta ya ja kadan tayi firgib ta dawo natsuwarta tana sauke ajiyar zuciya tsurawa juna idanu sukayi batare data ce masa komai ba
ya nufi hanyar fitowa daga d’akin daita tana biye dashi .”
Yana fitowa haraban hotel din idanunshi suka ci karo da motar alqali murfin motar a bude wasu mutane na tsaye suna duba cikin motar ,sai lokacin ya tuna da yasa a tsare masa shi ,Kai tsaye gurin motarsa ya nufa ya bude wa tanweer gaban mota ta shiga ta zauna ya rufe ya zagaya ya shiga bangaren direba ya shiga ya zauna ya tadda motar yana fitowa ya sawa motar wuta kamar Wanda zai tashi sama “kabi a hankali please Ina matukar son rayuwata domin tana da matukar mahimmanci ga iyaye saboda nice duniyarsu “Ina da mahaifiya da kanne day day har guda uku mafi soyuwa a zuciyata bazan so suyi maraicina ba bare ki fada min maganar banza yayi mgnr a tsawace yana dukan stearing motar shiru tayi tana zance zuci kafin daga bisani ta motsa labbanta a hankali “kana son mahaifiyarka da kannenka sosai ?” tayi maganar tana kallonsa da gefen Ido da kmr bazai yi mgn ba sai dai mahimmancin su ya wuce ya banzatar da amsar dan haka yace “kwarai kuwa ina matukar son mahaifiyata da kannena so na gaskiya son da bana Jin akwai wani mahalikin da yake wa ahlinsa “Amman shi ….” maid your thought karki sake furta komai akan ahlina ya fad’a yana cigaba da murza stearing ,dole taja bakinta tayi shiru “.