KUSKUREN BAYA 1 TO 48
xagi ba kalar da tanweer bata musu ba da hausa da turanci Amman Babu Wanda ya kulata haushi ya isheta ta bar gurin mota ta nufi bakin get nan ma babu hali dan me gadi yaki bude mata get duk Inda tasan zata bi ta fita daga gidan babu hali ta shiga maseefa tana cewa ” sai na bar gidan Kuma Babu wanda ya Isa ya hanani fita idan na bar gidan sai na sa ankamaku anyi muku hukunci me radadi,wallahi da Kun San Koni wacece a garin nan da baku tsaya bin umarnin wannan ba Kun hanani fita ba, ta juya ta Kalli Inda jaguwa yake tsaye jikin motarsa Idanunsa na kanta yana cigaba da kallon bakin tsiwa “zan nuna muku ko ni wace acikin garin nan tare da juya masa baya.
“Kashi Amman na tausaya miki wannna shi ake kira da power less” juyowa tayi cikin fushi ta Kalli Inda yake idanunta ya sauka akanshi.
yana nan tsaye sai dai zuwa wannan lokacin ya harde hannuwansa a qirji yana mata murmushin mugunta fuuuu ta nufosa cikin tsananin fushi da zuciya tace “zan nuna maka wannnan power din kasa Ido ka gani”tayi mgnr tana nunashi da yatsa “me zaki iyayi ?ba abinda zaki iya yi min ,ki daina takama da wannan dan matsayin da mahaifinki yake dashi dan baki da wani power da zaki iya min koma” .
ba bata lokaci ta cukumi wuyansa “zaka ga abinda zanyi “.
Yaransa suka bishi da kallo haka ma abokansa me gadi kam saurin kawar idanunshi yayi kamar bai ga abinda ke faruwa ba ran jaguwa yayi mugun ‘baci sai dai bai ce mata Komai ba har sanda ta hau fad’a da maseefa da zaginsa da fada masa bakaken maganganun ,sai da tayi mai isarta sannan ta sakar masa wuya ta dukurshe ta zube kasa ta runtse idanunta wasu hawaye masu zafi suka zubo mata .
shi kuwa ya matsa gefenta ya tsura mata Ido ransa na quna kafin daga baya ya canza kallon zuwa natsana yayi taku biyu zuwa Inda take durkushe dafe da goshinta “sorry tanweer bazaki iya komai ba sai da kiyita ihu kina kuka kina zagina
just like a baby ,the great tanweer, kyakkyawar matashiya mai ji da
kudi yanzu ta zamo abar tausayi agidan nan , gidan nan fa ba yadda kike tunani bane dan ba haka kawai yake ba ko mahaifinki da karfin masu karfin garin nan zasu zo basu Isa su shigo ba, Ina tabbatar miki muddin kika bar gidan to nine na fitar dake amman rashin kunyarki da ihunki bazasu fitar dake ba cikin sauki ba .”
wani mugun kallo take masa tabbas da zata samu bindiga a halin yanzu da zata hakura da son da take masa
ta harbesa ta huta, hakan ne ma zai zame mata sauki a rayuwarta dan tasan muddin bai duniya zata hakura dashi , “amman bari na gwada miki karfina ai kina son fita ko?tayi shiru taki cewa komai sai hawaye dake zuba “Ammar bude mata get tuni
taga get ya bude “how dare you? ta fada tare da k’arasawa gurin me gadi ta d’aukeshi da mari “Kai har ka Isa na maka mgn Kaki bin umarnina kasan kuwa waye ubana a garin nan? “ubana shine minister of health na garin nan waye shi wannan daya ajiyeku ban da tantiri ?jaguwa ya matso gabanta ya mika mata roban ruwan faro me sanyi “,Sha ruwa sanyi tanweer kiyi aiki da kwakwaluwa ” me yasa mahaifinki zai d’auki mataki akansu ?”anan basu san kowa ba sai sani , babu dokar kowa da zai yi aiki sai nawa ,gidan nan gidana ne mahaifinki bashi da wani matsayin bashi da power haka kema , shi wannan matsayin ko power din ki bari sai kin koma gidanku dan anan babu Wanda zaiyi respect dinki babu Wanda zai ga girmanki sannan babu Wanda zai bi umarninki sai nawa , nawa za’a bi kin san me yasa ?Yayi kusa kusa daita “kowa yasan matsayina, dan fashi ne dake sata wa kasa da kasa the CEO of armrobber’s, armrobber’s din daya yi suna da girma a fad’in Africa gbdya kowa yasan jaguwa wato Adnan amad gwoza anan wa yasan matsayin tanweer har ta bada umarni abi har ta kafa doka abi a zauna ?ke ba kowa bace sai diyar common minister of health da iya garin nan da wasu tsirarun garuruwa akansansa
sannan mutumin dake zaman banza
a offishinsa da suna yana aiki wa alumma mutumin da maci amana kasar ne , bai San komai ba sai shaye shaye da neman matan banza da bata rayuwar mutune wannan shine cikakken halin mahaifinki da kike takama dashi ,bari kiji da zai fito da boyayyen halinsa fili babu mutun d’aya da zai ga girmansa hatta ke kanki sai kin tsaneshi ,wallahi idan baki yi amfani da tunaninki kin kiyayeni ba kin daina zagina ba zan nuna miki asalin waye jaguwa, zan fito miki da true colour dina, zan yaga miki rashin mutunci ,zan mayar dake baiwa a gidan amadadin bautar da nake miki , sannan ki zamo daya daga cikin karuwaina nayi duk yadda nake so dake idan bukatata taso nayi ko sau nawa nake so yana gama fad’ar haka ya juya abunsa .”
ran tanweer yayi mata zafi ta dinga Jin zuciyarta kamar wuta magangunsa suka tsaya mata arai ta kasa motsi, ta bishi da Ido kawai
tana kallonsa ,lokaci na farko kenan da’aka fad’a mata bakaken maganganun da suka daga mata hankali Km akan masoyinta data fi qauna akan komai,sosai taji mgnr sun tokare mata zuciya Kuma ta kasa Koda motsi balle ta bud’e baki ta zagesa ko ta fad’a masa bakar mgn. shiru tayi tana mamakin abinda ya fad’a akan mahaifinta karyata hakan zuciyarta tayi sai dai Kuma ta rasa dalilin da zuciyarta ke wasi wasi akan maganarsa .”
Shi kanshi jaguwa yayi mamakinta Yana jiran yaji ta balbalesa da masifa da balai akan furuncinsa sai yaji shiru don haka byn ya dan yi nisa kad’an sai ya juyo yaga me takeyi, har yanzu tana zaune tana kallonsa yaga wani bacin rai atattare daita wanda bai ta’ba gani ba tayi sanyi sosai bazai iya karantar meye a kwakwaluwarta ba tuni yaji hankalinsa yayi matukar tashi Anya bai fadi magana dayawa ba kuwa akan dad dinta ? “Shi kansa yasan ya fadi abinda bai dace ya fad’a ba , jikinsa ne yayi sanyi ya Isa d’akinsa yana tunani hankalinsa ya tashi dan arayuwarsa baya qaunar ya batawa wani bare ita da yake jin duk saukar numfashinsa yana sauka da tunaninta ne ,yadda yaga yanayinta yasan ya ta’ba zuciyarta” me yasa na fadi abinda na fada “karka damu is a very good respond to her akan furucin bakinta km ya kamata tasan kadan daga cikin halin mahaifinta .
” amman Kuma karya zamo da gaske zata shirya daukar fansa akanka ? tsaki yaja dan me zakaji tsoro ko ka manta ko kai waye ? Yayi shiru na dan tsawon lokaci sannan yace “babu abinda zata iya ya kwanta akan kujerar kushin ya janyo pillow kujerar ya rungume a qirjinsa yace”tanweer you can’t do anything coz na zamo wani bangare na rayuwarki .”
Tanweer ta koma d’akinta ta kwanta lamo akan kayan da tayi kaca kaca dashi sai dai tsabar zafin zuciya ta jima tana tunani wani lokaci hawaye ya zubo mata ta tsinci kanta cikin kewa ta dinga Jin kamar bata da kowa da komai a duniya a tattare daita haka ta yini kwance agurin ta Kulla wannan ta kwance har dare jaguwa yasa aka yi order abinci kala kala wanda yasan take so, ya nufo d’akinta Yana bud’ewa yaga wani duhu ya kunna wutar d’akin ya sameta kwance cikin yanayi mai ban tausayi ya matsa gareta ya tabata “tanweer “!
ya kira sunanta ai kamar wanda ya dana mata shoking din wuta tayi saurin mikewa ta buge masa hannunsa “ka kyaleni ka rabu dani kaji dadi burinka ya cika kasani cikin wani hali ,ka rabani da kowa nawa,kasani cikin damuwa hawaye ya zubo mata “ka rabani da masoyina ka rabani da dady ka rabani da komai hatta matsayina da mutuncina ka rabani dashi kana Jin wai Kai wani
ne shiyasa ka dauki kanka a wata tsiya to bari na fad’a maka sai dai idan ban bar gidan nan a raye ba amman wallahi sai na ……” shiiiiii ki Daina wahalar da kanki coz you can’t do anything “.
dukkaninsu sukayi shiru suna kallon juna a zahirin gsky bai so ya fad’a mata abinda ya fad’a ba amman tunda ya fad’a babu abinda zai goge hakan, muryarsa can kasa yace”ga abinci kici ki km huce dan nasan baki ne babu abinda zaki iya yi ya mike ya juya yana cewa “ki tabbatar kin gyara d’akin ko ki kwana cikin datti “. kifi abincin tayi a kasa “baza’a ci abinci ba, gbdy ta zubar dashi tabisa da fad’a da tsawa bai kulata ba ya wuce ya tafi a wannan daren dukkaninsu babu wanda ya runtsa kowa da abinda ke ranshi ke sakawa jaguwa da bacci ya gagara ya tashi ya shiga d’akin anas kusan kwana sukayi suna Hira sai dai bai yarda ya Sako mgnr tanweer ba yayinda Zahra tayita Kiran wayarsa bai d’auka ba , wannan abu yayi mugu mugun d’aga hankalin zahra ta kwana da matsanacin fushi da bacin rai a zuciyarta da sake d’aukar burikan mugunta akan tanweer haka ma washegari bata hakura ba tayita kiransa bai d’auka ba shi kuwa duk kiranta yana gani amman yaki d’auka dan bai ga abinda zaiyi da kiranta ba ya cigaba da harkokin gabansa .”
A daidai wannan lokacin kuwa Zahra na can cikin tsananin tashin hankali tsaye cikin bakake kaya kunneta manne da waya cikin yanayi na tashin hankali take waya da blessing “matsalata daya yanzu arayuwa shine Adnan .”
“Na fada miki zaki samu Adnan zaki auresa ta kowani hali duk Wanda zai shiga tsakaninki dashi karshensa mutuwa ,mutuwace makomarsa dan haka ki kwantar da hankalinki mu gama da next target dinmu ki natsu karki rusa mana plan idan aikin boka yaki akwai makirci bare zai ci zan sake kaiki wani guri Ina tabbatar miki duk abinda yake takama dashi da asiri baya cinsa sai mun rusa, mun ruguza komai nashi yaji baya qaunar ganin kowa sai ke .”
“Shine abinda nafi qauna blessing ya zo da kanshi ko bai rokoeni soyayya ba ni dai yazo blessing bazan iya rayuwa babu Adnan ba “ki daina kaskanrar da kanki kina da komai da duk wani cikakken nmj zai soki akanshi kece kika fi dacewa da cancata dashi ba wacan tsinanniyar yarinyar ba, ya soki ya qaunaceki amman saboda rashin hankali da tunani me kyau irin nasa ya rasa Inda zai ajiye soyayyarsa sai gurin….” “excuse me blessing don’t ever call him mad karki sake zaginsa idan kina cewa bashi da hankali da tunani ni Kuma da nake so shi fa ?don’t don’t try to insult him “am sorry kit Zahra ta katse Kiran batare da ta jira taji me blassing zata sake cewa ba .”