KUSKUREN BAYA 1 TO 48
zaune dcp suke tare da yaransa gbdy zagaye da makaken table kowannensu ruwan roba ne a gabansa sai dai gbdy hankalinsu naga ogansu dake zaune yana koro bayani “Wannan aikin musani ko mu mutu ko mu rayu ne ,wannan aikin sai mun sadaukar da rayukanmu akanshi kowannenku ya shiryawa mutuwa ko nasara ku shirya anything will happen in diaters wannan aikin ne da gbdy ba’a bukatar kuskure acikinsa , kuskure daya idan munyisa to mun fa rasa wannan damar kenan Kuma bazamu Kara samun dama irinta ba ,mai da hankali shine babban abinda ya kamata ,ku Saka idanuwanku akan komai idan mun Isa yana gama fad’ar haka ya mike gbdynsu suka mike kowannensu rike da bindigarsa suka fito suka shiga motocinsu suka hau titi suka d’auki hanyar da zata Kai su magodo estate .”
da misalin karfe takwas jaguwa na kwance a falonsa yana kallon Tashar labarai domin yasan halin da gari da kasar gbdy take ciki, gabansa ne yayi wani irin mummunar fad’uwa kamar Wanda aka buga masa guduma ,shiru yayi kawai yana tunani sai dai idanunshi na kan tv ,duk sanda gabansa yayi irin wannan faduwar tabbas akwai gagarumar matsalar dake shirin kunno Kai cikin rayuwarsa .
Remut ya ɗauka ya kashe tv sannan ya mike ya koma uwar dakansa ya kwanta akan makeken gadonsa ya fuskacin kofar shigowa gidan gbdy tare da runtse idanuwanshi .”
a daidai wannan lokacin kuwa jami’n tsaro ne kewaye da unguwar kowannensu rike da bindiga tun daga nesa suka hango gidan koina zagaye da hasken fitilu , a hankali sautin muryar dcp dake gaba ta fito “
“be careful lokacin mu ya fara kowa ya kasance cikin shiri a hankali suka fara tafiya cikin sand’a suna taku da k’okarin isowa gidan suna gama karasowa suka nemi gidan kasa ko sama suka rasa gabad’aya gidan ya dawo rafi a matukar firgice sukayo baya da sauri kowannensu na kallon dan’uwansa cike da tsananin tashin hankali ,bayan kamar minti biyar dcp yayi gaba kad’an ya kira wayar IPO investigation police”kana ina yanzu IPO ?”Ina cikin gidan “kamar yadda mukayi fa mun zo sai dai babu gidan sai rafi “what ?”rafi Kuma?”tabbas haka ne abinda muka gani kenan “kana dai lafiya ko ?Ina lafiya Anya kuwa zan cigaba da aikin nan na fara karaya da lamarinsa ?
“tantiri ne na karshe ,asirin jikinsa yayi yawa “ka dai ka Kara hakuri tukun nan tunda har yanzu bai gane kana tare dashi ba ka cigaba da bincike akansa ka gano mana makarin asirinsa zan sake komawa malami nan gsky layar daya bani bata yi aiki komai ba shi daya ce zamu samu nasarar shiga gidan sai gashi gida ya dawo rafi “shinkenan sir jiki a sanyaye suka juya cikin sauri suka bar unguwar .
Gudu sosai suke akan titi karfe goma daidai suka Isa station zuciyar dcp kmr ta kama da wuta mafuta kawai yake nema “ta Ina zai yi galaba akanshi ,sam baya bukatar wani ya kamashi sai shi ko IPO abokinsa Kuma yaronsa wannan nasarar da zasu samu shine silar daukakarsu wujiga wujiga suka shigo office suna haki shigowarsu bai fi minti talatin ba wayar dcp ta soma ringing kamr bazai d’auka ba sai Kuma ya d’auka yana cewa “hello !Ya furta hello ya Kai sau uku sannan yaji an kwanshe masa da dariya “masoyina kenan wallahi har na fara Jin wani Abu akanka yana Jin hk ya fahimci jaguwa ne shi kuwa yana gama fad’ar haka yace sai anjima masoyina mara nasara .
” no ka tsaya Ina son muyi magana da Kai abinda kake aikatawa babban kuskure ne Wanda zakayi danasani akansa “wani irin kuskure Kuma bayan Wanda aka aikata a can baya ? har kullum bazan gaji da fada maka ka daina bibiyata ba domin bibiyaar mutne masu laifi Abu ne me wahala bana tsammanin zaka iya samu wani Abu ballatana ka shigo inda nake”.
” meye abun bata loakcin da Kai da yaranka ?ku manta da ni kawai idan Kuma Kuna bukatar wani tamako zaku iya sanar dani na taimaka muku dashi “what?
“Haka nake nufi domin dukkanin ku babu Allah a ranku kanku kawai kuke so ,kuje ku jajurce akan masu aikata miyagun laifufuka wanda zasu cutar da mutane daku gbdy.
“ka sani kaima hakan zai cutar da kai tunda kana da yan’uwa “haba da gaske ? to shikenan na fahimta Ina bukatar komawa bacci yanzu sai wani lokaci .
“Ka dawo da diyar minister
kada ka bari ta Kai mu ga daukar mugun mataki akanka. cikin sauri jaguwa ya dakatar dashi “kamata yayi yalla’bai yaje ya huta haka nan yayi aiki tukuru shi da yaransa shiru dukkaninsu sukayi jaguwa bai kashe waya ba haka dcp .
sun d’auki tsawon minti biyar suna misayar yawu sannan dcp ya numfasa yace “me kake bukata ayi maka ka dawo da diyar minister ? bangaren shigo da miyagun kwayoyin sunyi yawa a wannan garin namu domin har satificate ga masu shigo dashi suke da wanda daga hannunku suka samu.”
kashe kashe da fayde ga yara kananan da’ake wani irin mataki kuka dauka?
“Kun kasa daukar mataki alhalin kuna da karfi da makamai Kuma kunsan masu aikatawa har lasisi kuke basu suyi yadda suke so duk baku damu da masu aikata wannan laifi ba sai akan me tayaku aiki .
” me kake k’okarin cewa ?”, abinda nake so ku janye jikinku ga abinda bai shafeku ba shine zai fiyye muku ni nan nasan yadda zan hukunta duk wasu masu aikata laifi idan da dama Kuma ku maida hankalinku izuwa kan tayani aiki idan Kuma babu dama ku share kawai duk Kuma abinda zakuyi tunani akaina baxai ta’ba muku amfani ba ku tsaya a matakin da kuke domin wuce gurin zai iya zamo muku tangarda a rayuwarku wanda ya shiryawa mutuwa yayi k’okarin sake dumfarar gidana wallahi nayi alkwari zan kawar dashi a doron kasa bazan taba canzawa daga abinda nakeyi sai dai ban sani ba ko ta bangarenku zakuyi sorounder ku fita a rayuwar jaguwa .”
shiru sukayi gbdy suna saurarensa suna daukar maganarsa kowannensu da abinda zuciyarsa ke sakawa akan yadda za’a bullowa jaguwa gbdy idanun dcp ya canza kala babu komai acikin kwayar idanunshi sai tsantsar bacin rai hannunwansa duka ya hade guri d’aya ya rufe fuskarsa dashi yana dogon nazari da zance zuci yayinda har lokacin idanunshi ke kan wayarsa .”
tashi yayi ya soma tafiya har yayi taku uku d’aya daga cikin yaransa ya tsaidashi ta hanyar cewa”yalla’bai yanzu me ya kama muyi ?”ka dauki bindigarka kaje ka kwanta kawai “kayi hakuri sir ban san tmbyata zata bata maka rai ba “ka sani mana , idan ba haka ba meye na tmbyta abinda za’a yi byn kasan dole zamu sake nemo mafuta yadda zai shigo hannunmu ?”irin wannan lokaci nazari ake bukata idan ba haka ba zamu tashi a tutar babu yana gama fad’ar haka ya juya cikin tsananin fushi ya bar d’akin taron yana fita kowa ya kama gabansa .