KUSKUREN BAYA 1 TO 48
a hankali ta shiga girgiza Kai “no no impossible bashi bane sam bai yi kama da irin wad’an nan mutane ba dukkanin alamun sun nuna shi din mutumin kirki ne ya dai taimaketa daga hannun yan fashi ne zuciyarta ta tsayu akan haka ,cikin natsuwa ya juya ya cigaba da tafiya cikin Isa da izza ya barta tsaye adaidai lokacin da alqali ya fito daga cikin motarsa wani yawu ta hadeye tana qoqarin daidaita numfashinta da natsuwarta ta biyo hanyar da ta ga yabi tana waige waige karaf idanunta ya sauka akan alqali da hannunsa yayi mata alamar ta tsaya amman dake a tsorace take cikin sauri ta shiga d’aga ka’fafunta kmr walkiya ya nemeta ya rasa Yana nan tsaye su anas suka fito daya bayan daya suka wuce ta gabansa kowanne ya kama gabansa kasancewar kowannensu akwai bangaren da yafi so .”
Tsaye tanweer tayi aguri d’aya kamar wacce aka dasa tsabar tashin hankali Inda ta tsinci kanta a yau din nan , ta rungume hannuwanta duka aqirji har loakcin sauti ne ke tashi akoina acikin Rita Lori yayinda jaguwa tuni ya samu guri ya zauna akan d’aya daga cikin fararen kujerarun dake gurin ta waiga bangarenta na dama tsaye taga wasu matasan mata su biyu akan stage daya sanye da kaya wando da riga yellow dinki gbamu gbamu ka’fafunta sanye da sander shima baki hannunta rike da speaker tana rera waka yayinda yaranata ke mata amshi dayar mata itama sanye da wando da riga sai dai nata kalar ja ne gbdy haraban gurin shirye yake da fararen kujeru da table a tsakiya .”
tun daga nesa mawakiyar ta fara bud’e hakoranta dan ganin anas na shigowa nan take salon wakar ya canza salo ta soma masa waka tana sake fad’ada fuskarta da murmushin irin nasu na gogaggun yan duniya Shima murmushi ya sakar mata sannan ya soma qarasowa Inda take itama ta nufo shi suka rungume juna har da kiss ta manna masa a goshi kana ya nufi gurin empty chairs ya samu guri ya zauna zamansa ke da wuya ma’aikatan gurin suka qaraso garesa tare da kwalaben giya da soyayyen nama da yaji yaji domin sun san irin abinda yake bukata kenan sa’banin jaguwa da malt kawai yake sha idan yazo.
“subhanallah tanweer ta furta a ranta tana mamakin “wai yau itace a irin wannan gurin wasu hawaye ne masu zafi sukayi nasarar biyo gefen fuskarta tana k’okarin sharesu jaguwa ya qaraso gabanta yana girgiza mata Kai alamar kartayi kuka sannan ya rungumota jikinsa ta kwantar da kanta a faffadan qirjinsa dake fitar da sihirtaccen kamshi , cikin tsananin tashin hankali yasa hannunsa ya share mata hawaye ya sake rungumeta tsam yana zagaye weist dinta da hannunwansa duka wani irin tsalle hade buguwar zuciya tanweer tayi Wanda har hakan ya haifar mata da tsayawan numfashi na wasu yan mintuna haka duk wani tunani dake tafiyar da bugun zuciyarta sai daya motsa ta dinga Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta.
yau ce rana ta farko da jaguwa ya rungume mace acikin mutane batare daya ji komai ba ajikinsa hasalima wani sanyi yaji yana bin jijiyon jikinsa ,bakinsa ya Kai cikin kunnenta yana mata rad’a wanda hkn yasa tsigar jikinta tashi “kukan ya Isa haka please kar zazzabi ya kamaki ” cike da muryar kuka tace “me yasa ka kawo ni nan ? shiru yay mata tausayinta na kamashi ya d’ago fuskarta suna kallon kwayar idanun juna can ya motsa lip’s dinsa “baki so mu wuce na mai dake gida yanzu ?shiru tayi ta cigaba da kallonsa yayinda zuwa lokacin idanun mutane sunyi caa akansu ciki kuwa har da abokansa da alqali daya samu nasarar shigowa “kiyi min magana idan baki bukatar kasancewa damu anan na mayar dake ” nan ma shiru tayi hawaye na sake zubo mata masu zafi da radadi “wai kasancewa dasu ko su dawa oho masa ?tafiya ya soma yi daita tana makale ajikinsa har ya Kaita kan table din daya fara zama ya zaunar daita a hankali .
kuka tayi sosai taki yin shiru yayi mata magana yafi sau goma dan gbdy ya manta Kansa a gabanta sai wani narke mata yake zuciyarsa na sanyi akanta sannan baya son rabuwa daita shiru tayi kawai tana makale ajikinsa tayi yawo kasashen duniya sosai amman bata ta’ba Kai kanta irin wad’an guraren ba sai gashi a kasarta ta tsinci kanta da kyar ya rarrasheta tayi shiru ya bude mata kwalban malt ya Kai bakinta idanunshi na kanta . suna nan zaune mawakiyar ta fara bin Site by site tana waka yayinda mazauna kan table suka dinga mata liki har ta k’araso table din da jaguwa ke zaune bai daga idanunshi ya kalleta ba sai anas ne ya taso daga mazauninsa ya shiga lika mata ‘yan dubu day day ta dan durkusa tare da furta “thank you sir shiyasa nake son ganinka sannan ta tsaida wakar tare da cewa ayi mata tafi nan take gurin ya d’auki tafi raf raf banda jaguwa da tanweer , sautinta ne ya cigaba da karad’e gurin anas ya tashi yana layi ya shiga rawa bayan ya gama rawa ya nufi gurin zamansa Yana rawa aikuwa makiyar ta biyosa nan gurin ya hargitse da dariya har shi anas din dariya yake sakamakon ya fahimci abinda take bukata daga garesa kudi take so ya fito da bandir din kudi ya shiga lika mata yana rawa irin tasu ta mashaya .”
Yammata ne su uku zaune acikin runfa me zagaye da wutar lantarki sai tsirarun bishiyoyi kowacce daga cikinsu hannunta rike da karan sigari da glass cup dake cike da ruwan giya “Kalli d’an iskan mutumin nan , ai na sha fad’awa sweet zahra ta fita hanyarsa ta tsaya taci lokacinta taki kamar jijiyarsa ce kadai ke da dadi , “ai Ina ganin sai ta tsinci kanta a lahira zata gane matakin daya dace daita , sam taki yarda tayi muamula da masu bukatarta inji cewar helen “kyale banza yanzu dey kirata tazo ta ganewa idanunta wata Killa tasan Inda ke mata ciwo wallahi tunda ta had’u da mutumin nan komai nata yayi qasa Ina dalili inji cewar hafcy no-no suna cewa mata haka kasancewarsa tana da dukiyar Fulani over “haka za’a yi hafcy bari na kira shegiya ta bud’e jakarta ta ciro wayarta kira d’aya zahra ta d’aga wayar cikin fara’a” sweety nah dake haka suke Kiran junansu dashi “yes sweet Helen meye labari ne ? ta amsa mata ciki fara’a.