KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Bangaren jaguwa kuwa kasa runtsawa yayi gbdy ya nemi bacci ya rasa wanda ya halakanta hakan da tausayin hally ,yayi juyi akan gado yafi akirga bazai tantance lokacin daya dauka yana juyi ba kafin daga baya ya yunkura ya sauko ya tsaya ya jingina jikinsa da bangon dakin sanye cikin kayan bacci wando da riga sky blue wandon iya gwiwa haka ma rigar mai gajeren hannu ne ,tunani yake sosai komai nasa ya tsaya yanzu haka yasan anas na can yana sex da hally “Wayyo allah hally wata killa tana can tana kuka tana neman dauki gashi babu wanda zai taimaka mata” ya fada yana runtse idanunshi tare da hade hannunwansa guri daya ya rufe fuskarsa duk yadda jaguwa yayi ya samu natsuwa ya runtsa ya kasa saboda tsananin tausayin kanwarsa ya bude idanunshi ya kunna wutar dakin yana duba lokaci karfe daya saura ya dauki wayarsa ya kira layin anas wayar na ringing amman bai dauka ya sake runtse idanunshi zuwa yanzu ya sadaukar anas na can yana having sex daita “haka ma ammi bata iya runtsawa ba sai faman juyi take akan gado itama dan tausayin autarta ,shafiq ta fahimci halin da ammi take ciki ,dan ita har lokacin bata kwanta ba waya ma take da gali ta gaugauta yi masa sallama ta dawo gefenta ta zauna tana kiran sunanta “ammi !
Ta sauke numfashi tana dubanta “gsky ammi banji dadin abinda kikayi ba “me nayi ?ta tambayeta tana yunkura wa ta zauna tana nazarin shafiq “da kika bari yaya ya zarta da hukunci da yayi ta bata amsa tana cigaba da magana “ammi an nunawa hali rashin gata ban taba ganin amaryar daakayiwa haka ba wallahi banji dadin hukunci yaya ba ko me yasa yayi mata haka kamar wacce bata da gata ?”ta karasa maganar cike da rauni hawaye na cikowa a idanunta.
“Ke yanzu har akwai abinda yayanku zai zarta akanku kiji babu dadi aranki ?”ai wannan …”
“Dakata karki kara cewa komai duk abinda yayi akanku daidai ne agurina saboda nasan haka kawai bazai yi haka ba, ko yayi haka a aurenki?ta girgiza mata kai “to ki barsa a yadda yayi raayi kuma kibi umarninsa kamar yadda kika saba ni a waje na abinda yayi shine gata tunda da kanshi ya kaita har dakin aurenta ammi na gama fadar haka ta koma ta kwanta jiki a matukar sanyaye ta lallaba ta samu guri a bayanta ta kwanta tana kashe wutar dakin .”
Washegari tun asuba hally ta tashi byn tayi sallah bata koma bacci ba ta shirya kanta cikin doguwar rigar shadda yellow an ratsa dralace aciki da stone’s ta fashe ilahirin jikinta da turare sannan ta kimtsa dakin duk da babu abinda yayi ta janyo akwatin data bude wanda kayan sawarta ke ciki ta isa gaban wordrobe dinta ta soma shirya kayanta sai data shirya komai a lokacin da karfe takwas ta buga ta koma bakin gadi ta zauna .
Tana zaune tayi tagumi tana tunanin da zullumi ya shigo cikin kananan kaya Wando da riga army green nan take dakin ya gauraye da kamshi turarensa dio yayi kyau sosai yayi sallama fuskarsa babu annuri sosai ,ya zuba mata idanuwanshi kunyarsa ta kamata ta sunkuyar da kanta kasa tana gaishesa,bai amsa ba ya matso kusa daita a bakin gado ya zauna ya dan dafa kanshi sannan ya dubeta yace “me yasa kika kulle min kofa jiya byn nace babu abinda zan miki?”
Tayi shiru dan gbdy ta gama gano abinda ke dawainiya dashi ta dan kallesa cikin idanuwanta “ai na fada maka tsoro nake ji dan zan iya suma wallahi “ai Kinsan bazan yi abinda zai cutar dake ba nasan yadda zan tafiyar dake a madadin kiji zafi sai ma kiji dadi ya kamo yatsun hannunta jiya nayi baccin wahala ,ki tausaya min hally karki sake kulle min kofa wallahi nayi kewar rashinki.”
“kayi hakuri ban san zaka shiga damuwa ba ,amman kuma tunda baka saba ba me zai sakaka ka shiga damuwa har kayi kewar rashina ya waigo cikin idanunshi ta hango bacin rai sosai da furucinta ya dan girgiza kai “yanzu abinda kika fada kin kyauta ? Tai shiru kawai bai kara cewa komai ba ta danyi tunani maganar data sanar masa“amman kuma tunda baka saba ba me zai sakaka ka shiga damuwa har kayi kewar rashina ta danyi murmushi ganin bata fadi abinda zai bata masa rai ba shiru ta cigaba da yi,ya tsura mata ido “kin kyauta abinda kika fada min hakan ya nuna baki yarda dani ba sannan baki damu dani ba bakya kwadayin kasancewa dani “?
Yanzu kam maganar tafi karfinta shiru tayi kunyarsa ta addabi zuciyarta sai ta dan bata rai alamun tashin hankali ta dan janye jikinta daga nashi ya dan yi murmushi yana kare mata kallo “kin canza fuska sbd baki qaunata ko ?ta danyi dim “me yasa zakace hk tay mgnr muryata na rawa ?”sbd kin gujeni a ranar dayafi dacewa ki kusanceni ta sauke idanunta kasa bata ce komai ba ya sake maimata abinda ya fada hakan yasa tace “nima fa idan ka lura bani da laifi banyi da wata manufa ba ya kai hannu ya shafa qirjinta abinda yasa ta zabura kenan da sauri murmushi yayi “lallai kina da aiki agabanki ya matso sosai allah ya taimaketa wayarsa ta soma ringing ya tashi tsaye cikin jan tsaki da damuwa ya nufi inda ya hango ta yana dubawa sunan jaguwa yagani yana yawo akan screen din wayar nan take ya saki fuska ya dauka “suka gaisa jaguwa na kokarin neman gurin zama a parlaur ,ka fito ina jiranka a parlour .
ya kalli hally dake binsa da kallo sannan yace okay ya fita zuwa falon yana zaune anas ya danyi murmushi yace “ya haka da sanyin Safiya karka manta kai fa sirikina ne ya kamata ka dinga neman izini tun daga waje kafin ka shigo gidan nan ?”
Ya dan yi murmushi yana sosa keya “haba anas Kmr a film?anas ya kallesa “Au haba ko ? Kai dan allah ka dame ni ina hallay ? murmushi anas yayi “na cinye ta,kai ka fara wannan danyen aiki ka dai ci ka rage ta shine zaman lafiyarka suka sa dry gbdy .
“wallahi jiya na kasa bacci sbd tausayinta ,au a she babu dadi kake cin tanwer kuma kaki aurenta ? yayi shiru yana kallon tsakiyar kafet din falon tausayin tanwer ya kamashi duk kwanakin nan tana ransa cike da matsanamciyar shaawarta dan duk sanda ya tuna da kayan marmarinta hankalinsa tashi yake jira yake ya gama da komai na bikin nan ya ganta
yasan itama tayi kewarsa ta dai kyalesa ne taga iya gudun ruwansa.
“ina hally anas na damu nasan halin da take ciki ?tana daki cikin koshin lafiya hankalinsa bai kwanta ba sai da anas ya tashi ya kirata ta fito ya ganta ras babu wata alamun damuwa ko ciwo sannan hankalinsa ya kwanta ta durkusa har kasa ta gaisa “ina kwanta yaya ? .
“Kin tashi lafiya auta ? lafiya yaya ta fada tana sunkuyar da kai yace “ga kular abinci can akan dining daga ammi anas yayi murmshi yace “allah sarki ammi allah saka miki da alkhairi hally takarasa kitchen ta dauko plet da spoon guda biyu ta dawo ta zuba musu abincin ta ajiye musu ta koma ta bude fridge babu abinda babu na drks ta dauko energy drkns guda biyu dan tasan yayanta na matukar son shi ta ajiye masu ta wuce da kular dakinta .”
“Adnan yasu kamil ? suna gida “Me yasa baku zo tare ba ? “Kai dai ka samu natsuwa tukun shi aure fa da kake ganinsa ba abun wasa bane karka manta alqallarmu yana da kyau gida ka da iyalinka su zamo asirance .
“sai abu na gaba bazan gaji da fada maka ba kayi hakuri da hally nasan zaka fuskanci abubuwa masu tattate da kuruciya atare daita sabanin matan da kayi muamula dasu “.Wallahi haka ne dan ta gwada min kuruciya kiri kiri yarinyar nan ta rufe min kofa jiya case din muke yi kiranka ya shigo ka duba min an daura min aure da matar da nake so nake muradi duk na danawa zuwanta sai kuma ranar tazo ta wargazamin shiri ka duba kagani kullum bani da mafarkin daya wuce aure dana hadu daita mafarkina itace tunanina son ganinta kadai ya kan sa na rasa sukuni ya runtse ido ya dan já jiki ya koma kan kujera kwanta ya kasa cigaba da cin abinci .
jaguwa yay murmushi ka gamawa mutane kurin gauraye kai ma gashi har yanzu a layinmu kake wallahi su jubi najin wannan sai sun tasaka gb da dariya sun jima suna hira ya tashi tsaye anas ya shiga ya kira hally sannan ya nufi hanyar waje jaguwa ya kalleta “hope babu wata matsala ?babu komai yaya .“Alhamdullahi ki sanyawa zuciyarki hakuri Kinsan gidan aure gidan zaman lafia ne da hakuri ,Jin dadi wani Abu ne da yake zuwa babu Kuma babu tabbas din zuwansa iyayen mu ba Wani dadi sukeji ba arayuwar aure su amma zaman lafia da hakuri yasa mutuwa ce ta rabasu kiyi duk abinda mijinki ya umarceki sabanin haka tsinuwar malaiku ne ,tunda ya fara magana kanta ke sunkuye akasa “ni zan wuce zan kawo miki shafiq wani sati inshaallahu to yaya na gode sosai allah qara girma allah kuma ya tsare mana kai ,”Ameen ya fada yana sa kai ya fice.
Aharaban gidan ya iske anas tsaye ,ya bude motarsa yana kokarin shiga “karka yarda naga kafafunka a waje ko kace zakazo gurin mu ka zauna kaci amarcinka har sai mun nemeka sai an jima ya fada yana shigewa ya tada mota ya wuce.
shi kuma anas ya koma cikin gida yana shiga falon yaji motsinta a kitchen dan haka ya karasa ya tsaya a bakin kofar kitchen din yana kallonta tana wanke plet din da sukai amfani dashi yana tsaye har ta gama ta goge hannunta sai dai ta kasa motsa jikinta da zumar barin kitchen din saboda yayi bake bake ya rungumee hannuwansa akirji yana kallonta a ranta tace “wannan kallon maitan da yake min yana matukar daga min hankali ta juya masa baya tana kallon wani bangare a natse ya sauke hannuwansa ya tako zuwa inda take sam bataji motsinsa ba sai saukar laulausan tafin hannunsa taji a kugunta a matukar tsorace ta zabura ta waigo aiko cikin sautsayi hannunta ya bugi glass cup yayi tsalle ya fadi akan tays ya fashe a daidai gefen kafarta cikin tsananin tashin hankali ya tsuke fuskarsa yana kallonta jikinta har wani rawa yake itama shi take kallo ido cikin ido suke kallon juna yadda ya kasa dauke idanunshi akanta cikin damuwa haka itama ta kasa dauke idanunta cikin tsoro .
ganin yaki dauke idanunshi, ta nemi gurin kallo tuni kanta yayi kasa tana kallon kasan kitchen “kayi hakuri ,da akayi me kenan ?”
Ya tambayeta yana kallonta tun daga kasanta har sama “uhmmm na …..”sai kuma tayi shiru ta kasa karasa mgnr domin rasa abinda zatace dan tasan bata kyauta ba “tsoro ma yasa kin kasa yin magana kawai saboda kin tsanane “.
Ta dago idanunta ta dube shi Kmr zatai kuka “ni na tsaneka ?allah ya tsareni tayi mgnr tana wasa da yatsun hannunta yayi dan gudun murmushi “idan ba haka ba mai zai sa ki dinga guduna daga jin na tabaki kinyi yunkurin gudu dan kawai ki jazamin yanzu da glass din akafarki ya sauka me kike expecting?
tayi shiru kawai domin ganin yafita gsky ya kai hannu ya riko ya zagayo daita ta gefen inda babu kwalbar ya mannata ajikinsa yana sauke numfashi “haba my princess me zai sa ki dinga guduna nifa mijinki né na sunnah idan baki tabani ba ni bai kamata ace in na kawo kaina ki dinga yunkurin guduwa ba komai zan miki ke din tawa ce bata kowa ba still bata ce komai ba ,ta dan tayi karfin halin mgn nifa ba gudunka nake yi ba kai kasan bazan gujeka ba abun nan ne dai kawai nake ….”
“Wani abu kenan ?
Tayi shiru wannan abu yafi karfin bakinta sarai ya fahimceta “ ki dan rage tsoron nan dan zai wahalar dani ya karasa mgnr yana tafiya daita zuwa falo ya zauna akan kujera mai zaman mutun uku ya kwanto daita jikinsa fuskarsu daf da juna yana shafa bayanta yana shakar numfashinta da kamshinta sosai tayi luf ajikinsa tai zurfi cikin tunani .