KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

yayi shiru yana kallon cikin lambun yana saka da war wara acikin zuciyarsa gargadin da anas yayiwa alhj tahir ne dazu ya shiga dawo masa daya bayan daya yana samun kyakkyawan mazauni acikin kwakwaluwarsa “lallai su din sunfi kama da yan fashi da makami  abinda  ma zuciyarsa  yafi yarda dashi  kenan sune sukayiwa mahaifin tanwer fashi sannan suka wuce daita  na tsawonlokaci , idan ba haka bane a ina suka san alhji tahir ? me ye kuma hujjarsu nayi masa gargadi akansa? tambayar da yayiwa kansa kenan wanda bashi da mai basu amsarta .shiru  ya cigaba dayi agurin  yana sake yiwa tunaninsa dalla dalla  lallai so yake ya gano wani abu a tattare dasu  da zai bayyana masa gaskiya sai dai duk dogon tunaninsa da nazarinsa bai hango  abinda zuciyarsa ke zarginsu akai ba dan kuwa  babu ta inda sukayi kama da yan fashi ,idan kuma sun tabbata yan fashi ne to kuwa nasu fashin mai kyau ne da adalci “to ma ina tanwer din take ?tambayar da zuciyarsa ta sake aikawa kwakwaluwarsa kenan har ya bude  baki da niyyar yi magana sai kuma ya fasa yaji kamar an saka superglue ya manne masa baki ne .”

cikin kankanin lokaci sky ya dawo  hannunsa rike da wayar nazifi ya mikowa anas shi kuma yace ya mikawa nazifi ,ya karba yana sake yin godiya  sannan anas ya bawa scorpion umarnin ya kai shi gida atare suka mike suka soma tafiya ,yayinda gbdynsu suka tsura wa jaguwa idanunsu suka cigaba da kallonsa eku sky suka kallesu sannan suka kalli jaguwa  tare da kwashewa da wata dariya garin subawa juna hannu dan su kashe suka bugi table din gabansa nan take glas cup’s din dake ajiye akai suka tarwatse ,bugun table din ne ya dawo da hankalin jaguwa jikinsa ya kuma ankarar dashi halin da yake ciki  “Am ranka ya dade daman haka idanunka suke ?” “Sosai ya sake dawo wa haiyacinsa yana dubansu fuskarsa tattare da alamun tambaya “lallai wannna soyayya hakika ta tabbata sosai  jabir ya fad’a yana murmushin tsokana” da wa kenna?jaguwa ya tambayesa  ya dan kallonsa  idanushi still  a lumshe tamkar wani mashayi “da kai mana idan ma ba kai ba wa za’a nunawa irin wannan soyayyar ? “uhm ka duba dan allah sai kace ita  din ba diyar  minister  ba,  idan tana yin wasu  abubuwa  sai ka dauka ita din ba diyar  babban mutun bace ,amman kowa ya ganta yasan yar gidan manya  ce jubi ya fad’a yana kwashewa da dariya.”

“Nata kuke gani shi fa ?gbdy ya canza tamkar ba jaguwa ba ,yau dai kowannenmu ya gano wani sirri atattare dai kai ba kuma ka isa ka mutsa mana ba ,mu dai zamu maka fatan alkhairi dan gaskiya jaguwa ka dace kaji dadi  wallahi karka tsaya sanya ka duba yarinya irin wannan haka amman ta makale sai kai  congratulations kamil ya fada yana mika masa hannu yana sakar masa murmushi amman kememe jaguwa yaki bashi hannu dan wani mugun haushinsu da haushin kansa yaji .”

“yanzu dai ku me kuke tunanin abun zai  kasance ? jaguwa ya mike tsaye cike da jin haushi  “kai dan allah kuyi min shiru karku dame ni da wata magnr soyayya”  ya soma tafiya anas yabi bayansa da ido cikin jimami kawai yana kallonsa ko har sai yaushe zai fahimci halin da yake ciki ?yana gudar masa randa soyayya zata wujijigashi tayi waccajali dashi ,
yaso yadda ya samu damar nan  yayi amfani daita “kaji abinda yace Ana’s wai kar mu damesa a zuwan ba gskiya bane ?”Haka zai ta nuna mana anas ya fada tare da kokarin mikewa tsaye “ina ma zanga wannan yarinyar dana fada mata ta rabu dashi da fita rayuwarsa wallahi zai fito da abinda ke ransa “bazata iya ba domin ba irinsu jaguwa mace
kewa irin wannan wasan ba , ko kun manta cewar shi din dokin tsare ne  ya fada yana cigaba da tafiya ya nufi hanyar fita daga cikin lambum.”

kai  tsaye  jaguwa hanyar  dakinsa ya nufa yana gyara kwalar rigarsa yayinda hoton  fuskar tanwer ya shiga  masa gezo acikin kwayar idanunshi ,tun daga kwayar idanunta  karamin bakinta hip’s dinta har zuwa qirjinta dake cike bammm a nan ya tsaya yana kare musu kallo tamkar a zahiri , nan kuwa tunaninsa ne kawai ,a hankalin ya fara  juyi acikin dakin  tare da zaro tsarkar gold dake makale a wuyansa boye cikin rigarsa yana juyawa a hankali tamkar yadda yake zagaye dakin fuskarsa kunshe da murmushin farinciki yana sake zurfi  acikin  tunaninta.”

a natse ya daga kansa  saman dakin yana kallon celling dakin  “ina sonka adnan dina ban samu damar yin soyayya da kowa ba sai da kai ,dan allah kace kana sona ,ka canza  sana’a zanyi confused din iyayena su bari na aureka sannan zan nemo maka sana’a bazan barka haka ba kalamanta suka dinga dawo masa daki daki suna haskaka zuciyarsa ,
a hankali ya jingina bayansa da bangon dakin tare da tokare kafarsa daya “bayan kamar minti goma ya sauke kafarsa yasa dan yatsantsa jikin bangon takin yana tafiya yana bin bango da yatsansa har lokacin murmshi ne kwance a fuskarsa ,yau yana cikin farincki mara misaltuwa ,na kiran da tanwer tayi masa ne ko kuwa naji albishirin dinta ne shi dai bai sani ba amman dai yana cikin farinciki da bai san dame zai misaltashi  ba .”

“nima ina sonki tanwer   son da ban taba  tsammanin yiwa wani mahaluki irinsa ba ,ina jinki  ajinina  acikin bargona da tsokar jikina  bazan iya rayuwa babu ke ba but just give me time  ina bukatar lokaci zanyi wani abu akai ,wani irin sanyayyen dadi ke bin lungu da sako  na sansar jikinsa ,jinin jikinsa ya ninka gudu akan yadda yake yi ,a natse ya karasa gaban mirrow ya tsaya ya tokare hannunsa da jikin bango yana kallon kansa ta cikin mirrow , yatsan dayan hannunsa ya kai cikin bakinsa yana cizawa a hankali a hankali yana jin kamar yatsunta yake cizawa “ina son fararen fure ko zaka dauko min ?ina sonka adnan na yarda da kai na kuma amince da kai ,ya tuna lokacin daya kai kangon gida da bai yi tsammani zata iya rayuwa acikinsa ba amman da budar bakinta tace “me zai hana adnan ?wallahi zan zauna dan fiyye min kowani gida muddin da kai zan rayu acikinsa karka wani damu zan zauna “. ya sauke naunayen ajiyar zuciya a daidai lokacin da ana’s ya turo kofar dakin ya shigo ya tsaya ya harde hannunwansa a qirji idanunsa akansa,jaguwa bai juyo ba sai ma kura masa ido da yayi ta cikin glas mirrow  yana kallonsa kafin daga baya ya juyo gbdy ya fuskanci anas  soyayyar tanwer na sake kanainayesa “yanzu me ka tsayar akan yarinyar nan tanwer?” I don’t know what to say but is like bazan iya cigaba da rike wasu abubuwa ba zan dai yi shawara da zuciyata  nan kusa zan tsaida maka
yayi mgnr hannunsa na shafa faffadan qirjinsa  ,
gyada kansa kawai anas yayi tare da sauke boyayen  numfashi yace “please jaguwa ka hanzarta kayi abinda ya dace ka daina barazana da rayuwar yarinyar mutane ” .

Ajiyar zuciya ya sauke tare da tsura masa ido yana jin yadda zuciyarsa ke mugu mugun bugawa ya kira sunansa “anas look at me babu wasa acikin kwayar idanuna idan bazan yi wani abu akai ba kai kasan waye  ne I won’t lie to you ,zanyi wani abu akai amman ban sa yaushe bane , yau né gobe ko anjima né bansani ba ya karasa maganar tare da yin shiru ya cigaba da kallon anas ,dakin dakin ya dauki shiru bayan ya rungume hannunyensa  duka sannan ya janyo wayarsa da yaji tayi kara alamun shigowar sako ya shiga dubawa yana gamawa ya fesar da  iska mai zafi daga bakinsa sannan  ya soma magana a tsanake ” satin nan  zamuyi aiki ma  alhji bello yanzu sakonsu ya shigo da inda zaayi aikin sai dai bana jin acikin mu biyar din nan akwai  wanda zashi zan tura sconpio  domin aikin zai fi dacewa da mutun daya ne ,nan  da 2 week kuma zamu shiga aikin akan masu safarar hodar iblis ,sannnan ina  saka rai mlm mudi zai turo mana sako yau ko gobe domin musan ta yadda zamu bibiyi alhji tajudenni da duk wasu masu irin sana’arsa .”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button