KUSKUREN BAYA 1 TO 48

DARLING’S????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
WRITING BY
BAGUDO& MIMI’S QUEEN
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
????️07
……Kusa daita ya ɗan duka yana kallonta ,a hankali yaji ta kamo yatsun hannunsa cikin nata tana murzawa bai san sanda ya zauna a gefenta yana sauke numfashi tare da tankwashe ƙafarsa ɗaya yayinda d’ayar kafar ke kan tayis yana jijigawa , matso da kanta tayi ta d’aura a saman cinyarsa, idanunta a lumshe take jin yadda idanunshi ke yawo a fuskarta ,motsa hannunsa yayi da niyyar zarewa daga cikin nata saboda yanayinsa daya ji yana sauyawa, ta bud’e idanunta tar akanshi Ido cikin ido suke kallon juna lumshe idanunshi yayi na second biyu sannan ya bud’esu akanta ya mik’e dan baya son kusancinsu tare “me yasa baki jin magana ?”
cikin sanyi murya tace ” me nayi maka ?” tana janyo hannusa ya rankwafo jikinta bakinsa ya sauka a daidai kunnenta hucin numfashinsa yasa ta runtse idanunta da sauri. “Ki tashi muje na maidake gidan ku” yayi mgnr yana sakin numfashi haɗe da ciza gefen kunnenta ta saki qara mara sauti tana jin wani iri a gabad’aya ilahirin jikinta .”No! bance maka bazan tafi gida ba but atleast na…..
“Shiii!”. ya katseta ta hanyar d’aura yatsansa a kan lip’s d’inta, shiru sukayi gbdy zuciyarsu na bugawa da karfi “ka hanzarta maida yarinyar nan tun bata zame maka kaska ba’. zuciyarsa ta faɗa masa haka, mik’ewa ya sake yi yana kamo hannunta “Ke! tashi muje Karki bata min lokaci “. banza tayi masa tana yatsina fuska “bana son Ki sake min mutsu akan komai ” yayi maganar yana matse yatsun hannunta cikin nashi yana ko’k’arin sauko dai ta, Cikin rashin sani ta fad’o jikinsa tare dan sakin k’ara “Ahm!”. Idannunta rufe, yadda ta runtse su yasa ya k’ura mata idanunsa masu matukar kyan gaske, dan kanne d’aya idon tayi ta bud’e sai tayi saurin mayarwa ta rufe hakan ya bashi murmushin da bai shirya yiba me sauti jin haka yasa tayi saurin bud’e idannunta akansa.
Murmushin ya k’ara mishi kyau sosai kamar kar ya daina , d’an k’ara ware idanunta tayi tana kallonsa wanda har lokacin fuskarsa na d’auke da murmushin. Ko’k’arin gyara tsayuwarta ya soma yi , Tanweer kuwa da sauri ta kai ma bakinsa cafka tamai peck a lips d’insa , ware idannunsa yayi sosai yana kallonta cike da mamaki ‘Do want to kill me wannan yarinya’. Ya furta a ransa Tan kuwa murmushi take masa, sake kai mai Cafka tayi a karo na biyu sai dai wannan karon taji ya bude ‘yan lip’s dinsa inda ya soma kokarin kissing d’inta,ya cafko laulausan harshenta cikin nasa kamshi sweet taji mai kamshi lemun ,ware idannunta tayi ganin kallon da yake mata yasa tayi saurin runtse idanunta jikinta na dan rawa saboda wannan shine karo na farko a rayuwa data yi kokarin shan bakin wani nmj .
Tsura mata idanunshi yayi tare da d’an murmushi, yana jin yadda take jujjuya harshenta da sweet din dake cikin bakinsa take zuciyarsa ta dasa masa ayar tambaya akanta. ‘anya kuwa yarinyar nan cikakkiyar buduwar ce ? anya kuwa ba watsatsiba ce take neman kawowa zuciyarsa farmaki? to idan itace kai meye ?Me ye marabinka daita? ” wata killa ma ta fika tunda bata aikata abinda kake …….
Kasa k’arasa zancen zucin nasa yayi saboda yadda take bin kunnensa da lallausan yatsunta tuni ya kasa jure abinda take masa a hankali ya cafko harshenta yana tsotsa a tare suka shanye sweet din sai ji sukayi sweet din ya kare aiko ta saka masa kukan shagwa’ba. “Wayo! Why?”
Tsura mata ido yayi yana kallonta tare da d’an janyewa, Tanweer banda tab’e baki ba abunda take tana kallonsa. “Ba…ka..kaine ka shanye sweet din byn bai isheni ba”. Tayi maganar a shagwab’e kamar zatai kuka. ‘bata face yayi wannan karon ba alamun wasa yanzu a fuskarsa. “okay tashi muje idan ma dubunsu kike so zan miki guzurinsa ta sauko tana gama saukowa ta rungumeshi a jikinta “i love you Mr.No Name!” I will miss you no name tsintar kanshi yayi da kasa rabata da jikinsa “Just one day with you but ina jinka tamkar kar mu rabu, is it necessary sai mun rabu?”. bakinsa ya kai cikin kunneta yana busa mata hucin numfashinsa, lumshe ido tayi “ka barni zuwa gobe plz ban gaji da kasancewa tare da kai ba”ta furta cikin sanyin murya kamar zatai kuka, dan ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta. “ta kowani bangare mahaifinki ya baza mataken tsoro ya damu sosai da rashinki me yasa zaki so zama dani fiye da iyayenki why?”
yay mata tambayar tare da ko’karin kaucewa.
“I know zasu damu sosai hatta I.B ma zai damu da rashina mutumin da muryata kadai idan bai ji ba a rana babban tashin hankaline gareshi “
take qirjinsa ya buga zuciyarsa ta shiga rawa shiru yayi yana ƙoƙarin ‘ban’bareta a jikinsa idan bai manta ba shine mutumin da suke waya daita a wancan ranar da tayi accindent “wannan kuma damuwarki ce yayi maganar cike da rashin damuwa , murmushin karfin hali tayi wanda yafi kuka ciwo “mutum mai dakakkiyar zuciya kamarka bai dace ya damu da lamuran mutane ba sai dai acikin kwayar idanunka kadai za’a iya hango tarin tausayi mutane bila’adadin”. “Ki daina wasa da zuciyarki da tunaninki muje kawai”. Yayi yunkurin sake bambareta a jikinsa ,sake manne masa tayi tana gyara tsayuwarta a jikinsa gabansa na bugawa da matsanancin karfi yayi nasarar zareta a jikinsa suna fuskantar juna ” ki daina bata mana lokaci saboda hakan babu abinda zai janyo sai tarin damuwa dan bazan taɓa sonki ba kuma ki daina sona dan soyayyata babu amfanin da zata miki , sannan daga yau ki sawa ranki bazaki sake ganin ko mai kama dani ba, kiyi rayuwarki tare da wanda kika fara zai fiyye miki , ni ba irin mutumin da zaki yi rayuwa dashi bane”
gabanta ya dinga dokawa da karfin gaske jikinta ya kama rawa bakinta ya kasa furta komai a dalilin maganarsa dake bugar mata da zuciya , riko tsintsiya hannuta yayi, yana gaba tana d’aga kafafunta da kyar tana kallon bayansa yayinda wani duhu mai haɗe da juya ya gilma cikin kwayar idanunta daidai tsikiyar d’aki yaji jikinta ya sake tana kokarin yin baya ya juyo idanunsa ya sauka akanta gbdy yanayinta ya sauya ta dafe daidai goshinta da hannunta daya cak ya tsaya a lokacin da take kokarin zubewa kasa yayi saurin tarota jikinsa hankalinsa a matukar tashe gabadaya ya rungumeta , ita kuwa cike da bakinciki take fidda numfashi kusan minti biyar suna tsaye tana rungume ajikinsa tuni hawaye ya wanke fuskarta, cike da tashin hankali take motsa lip’s dinta ” muje ka maidani gida kawai thanks for all the helps tun daga ranar farko da muka hadu har zuwa yantoni daga hannun yan fashi”. magana take jikinta na rawa take yanayin jikinta ya sauya daga dumin zuwa zazzaɓi mai zafi, cikin tsoron da bai san yana dashi ba ya matseta gam ajikinsa yana fidda numfashi tare da lumshe idanunshi, “ki dawo daidai sai na maidake” ni muje kawai ina son ganin iyayena, i really want to see them”. ta k’arasa maganar tana shirin zubar da hawaye jin numfashinta na kokarin tsayawa ya fara tafiya daita cikin sanyin jiki ,ya kwantar daita a gefen gado a hankali hannunsa daya dafe da byn kanta, yayinda d’ayan hannun ke tsarke cikin nata ya rankwafo jikinta “ki natsu plz qirjinta na dokawa tace “dan Allah say you love me ka fad’a min dan Allah koda itace zata zamo kalmar da zanje karshe daga bakinka ina son ji …
cike da matsanancin fargaba yace “dan Allah ki bar zancen nan babu wata soyayya a gabana, soyayyata ga kowace mace bata da wani amfanin ,bare ke karamar yarinya dake banason zunubin laifina ya shafe ki ,gara duk wani hukunci da zai zo min ya sameni ni kad’ai bazan ta’ba barin zunubina ya shafi kowa ba bare ke plz, dan Allah ki dawo daidai mu tafi dan hankalina bazai taɓa kwanciya ba idan na kai ki gidanku cikin wannan yanayin lumshe idanunta tayi numfashinta na tsarkewa heart beat d’inta na k’aruwa akai akai.