KUSKUREN BAYA 1 TO 48

dakata dan Allah malam ni babu abinda nayi daita “to me amfanin rike musu yarinya da kayi ? “Ka ….
kit ya katse kiran yana dafe goshinsa tare da rike kugunsa da daya hannunsa wani kiran ne ya shigo ya sake katsewa ya kashe wayar gaba-daya ya koma d’akin yana Kallonta idanunta a lumshe alamun tana jin bacci rabawa yayi jikinta ya kwanta tare da matseta ganin haka yasanya shi gaggawar birkitota suka fuskanci juna eye’s dinsu suka haɗu zuciyarsu yayi mummunar bugawa a tare laulausan tafin hannunsa taji yana yawo ajikinta tun tana jin abinda yake har bacci yayi nasarar d’aukarta amman stil tana jinsa , gabad’aya ya gigice irin gigicewar da bai taba yi akan kowace mace ba, duk tunaninsa ya kau burinsa kawai ya samu biyan bukata sai dai bazai iya aikata komai daita ba…….
sama da awa biyu ya ɗauka yana romacing din jikinta daren da yake jin kasancewarsa na musamman gareshi dan kuwa ji yake tamkar yana tare da matarsa ce ina ma zai iya daya yaki zuciyarsa ya aureta kamar yadda ta bukata dan yasan zai samu dukkanin wani kulawa daga gareta ,zata shayar dashi soyayya ,a hankali har ya samu natsuwa ya kwantar daita a saman faffadan kirjinsa yana sauke numfashi …
hannunsa ya daura saman gashinta yana shafawa zuwa gadon bayanta haɗe da kissing foring head d’inta “acikin zuciyar tanweer kuwa addu’a take da Allah ya tsaida shi iya haka batare da ya kusanceta ba , Allah kasa wannan bawa naka ya aureni dan zan sha soyayya shi din na daban ne i love you adnan ta furta haka acikin ranta , rufe musu jiki yayi yana sake lumshe kyawawan idanunshi har bacci yayi nasarar daukarsa…..
A hankali ya bude kyawawan idanunshi ya daura akan ƙaramin agogon dake ajiye akan abun gado, karfe takwas ya gani har ta wuce da wasu yan mintuna tsaki yaja saboda ya makara idan akwai abinda ya tsana bai wuce makara gurin sallah ba , ya kwantar daita tare da lullu’beta da bargo ya mirgina ya sauko ya janyo towel ya d’aura ajikinsa cike da natsuwa ya shiga bathorrom , bathtube ya shiga ya tsaya ya soma sakarwa jikinsa ruwa, wankar tsarki yayi tukuna domin tsaftace jikinsa sannan yayi wanka soso da sabulu bai dade ba ya fito yana goge jikinsa yana kallon fuskarta da gashin kanta mai tsantse da sheki komai nata mai kyau ya furta hakan a kasan ranshi ..
Jallabiya ya ciro wani design din yasa ya karasa kibabben gurin sallarsa ya soma gabatar da sallah gabansa na faduwa , yana matukar fargaba da tsoron mahalincisa a duk sanda zai yi sallah sai yaji gaba-daya komai ya kwance masa ,yasan abinda yake aikatawa bai da kyau har yana jin tamkar ibadar da yake ma ba’a amsa ,yayinda take zuciyarsa ta kawar masa da wasi wasin data shiga ya dinga yi mata naci da karfafa gwiwar da ana amsa har ya idar zuciyarsa rawa take ya mike ya dawo inda take kwance tana sauke numfashi hannuwansa duka ya kai jikinta ya d’agota ta zube jikinsa ta lafe tare da turo masa karamin bakinta gaba , bakinsa ya kai cikin kunneta “ki tashi kiyi sallah lokaci ya tafi mika tayi ajikinsa wanda ya haddasa masa jin wani irin shock , “uhm zanyi zuwa anjima bacci nake ji jikina duk ciwo yake min ,gefen kunneta ya ciza da dan karfi ta saki qara tana sake shigewa jikinsa “dole ki tashi kiyi sallah me kika yi da kika gaji ya k’arasa maganar yana busa mata iskan bakinsa take tsigar jikinta suka mike sake turo masa bakinta tayi tana kokarin buɗe bakinta taji yayi sama daita ya shige bathorrom daita ya sakata a bathtube “ba’a lattin sallah a gidana oya kiyi alwala ya juya ya koma d’aki bayan kamar minti uku ya dawo hannunsa rike da jallabiya ya ajiye mata ya sake fita ..
Jiki a mace ta fito tana kallon inda yake zaune rigingine da gado ta isa inda taga dadduma ta tada sallah bayan ta idar ta koma dayan bangaren da yake ta zauna “good morning ?”morning ya faɗa atakaice batare daya kalleta ba “ya kamata na koma gida ina so..
“zaki tafi nan da wasu awani dan zamanki bashi da wani amfani , ya fada yana mik’ewa akan katifa bata sake cewa komai ba ta zame ta kwanta tana runtse idanunta “komai cikin gadara da isa da nuna rashin kulawa ta fadi haka a kasan ranta …….
ya mike ya fita daga dakin zuwa wani dakin , yayi shirin fita operation dinsa tsaf ya shirya cikin bakaken kaya riga da wonda na suit ya ɗauki bindigarsa pistor guda har guda biyu ya soke ajikinsa yabi jikinsa da turare mai sanyi kamshi sannan ya fito zuwa babban parlou’n gidan yana d’aura agogo a tsintsiyar hannunsa turus yayi ganin jabir kamil jubi da Anas zaune suna tautaunawa akansa ganinsa yasa suka mike suna kallonsa , kallonsu shima yayi daya bayan daya yana tabe baki sannan yace “ku kuma fa ? “a tare suka bude baki mun zo ne akan wannan fitartaka bama son ka fita aikin nan dan Allah ka hakura ,”me yasa bakwa gajiya da magana ɗaya nifa wannan ba sabon abu bane agurina,”,Koda yaushe kana jayayya damu akan ra’ayinka amman akan wannan dole mu fi karfin ka “karfin wa ? ya furta yana musu wani irin kallon kasan ido
“Duk ma abinda zakuce kuce but I must face tanko gote zasu sake magana ya dakatarsu har zai fita yaji jikinsa yayi masa wani iri a hankali ya juya ya koma ciki ,kai tsaye d’akin da tanweer take ya shiga ya hawo har saman gado ya shige jikinta yana kissing din bayan wuyanta jinta yake kamar matarsa ya zira harshensa cikin kunneta sannan ya kamo hannunta cikin nashi “zani wani aiki mai mahimmanci da zarar na dawo zan kai ki gidanku ajiyar zuciya ta sauke tana juyo ta zuba masa ido batare da tace komai ba shima bai sake furta komai ba wani iri suka ji ajikinsu a lokacin da kwayar idanunsu suka tsarke cikin juna ,bai sake cewa komai ba ya fice tabi bayansa da kallo kamar ta hanashi fitar duk da batasan inda zashi ba , har lokacin su Anas suna tsaye ya nufi haraban gidan suka biyo bayansa suna masa magana amman ko tari bai yi bare su saka rai zai amsa musu , kai tsaye dakin ajiye makamansa ya nufa ya dibi harsashi da kudi masu yawa ya ɗauki keyn motarsa city ya fito still suna biye dashi ya karasa inda aka tanada domin ajiye motocinsa ya danna key din hannunsa ya bude kofa mazaunin direba ya shiga ya tayar mai gadi na ganin hancin motarsa ya bude masa, ya cilla motarsa waje .
mutanen dake tsaye jiran fitowarsa suka mike tsaye ,kamar ba zai tsaya ba sai kuma ya tsaya batare daya kashe motar ba ,yayi warning glass din motar ya ciro bandir din kudi yan dubu day day ya soma raba musu kamar yadda ya saba suka dinga amsa suna zuba masa ruwan addu’a da samun nasara yana kada kai ,sai daya sallamesu sannan ya dauki hanyar zuwa donping estate ..