KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

     “Taurin kai taurin kai mutun kamar mutanen farko duk abinda kaji ance ka barshi barinsa shine alkhairi duk kuma abinda zaka samu a duniya zaka bar shi jubi ya faɗa cike da taikaici da bakinciki taurin kan Jaguwa “wayyohlly Allah wallahi har na fara tausayawa yan’uwansa da halin da zasu shiga idan wani abu ya faru dashi  kamil ya fada yana marairaice fuska , jabir yace ” wallahi tunda ya soma shirin aikin nan naji ajikina babu nasara  “muyi masa addu’a kawai Allah ya dawo dashi lafiya domin shine karfin gwiwarmu bamu taba samun saɓanin ra’ayi ba sai a wannan lokacin inji cewar anas daya fi kowa shiga damuwa ” ameen suka had’a baki gurin fadar haka..

A hankali yake murza stearing  yana tunanin yadda abubuwan zasu kasance gaba-daya ya gama tsara komai da yadda zai shiga ya fito har ya dauki  titin da zai kai shi  estate din  ya  karaso bakin get din estate din yayi parking ya ɗan dade sannan ya fito     daga cikin motarsa yana gyara zaman suit d’insa kai tsaye gurin securitys din bakin get ya nufa suka gaisa a mutunce bazakace masa dan fashi ba bayan sun gaisa yace “ina son ganin Alhaji tanko gote  ..
Daya daga cikin securitys ya leko daga cikin wani karamin daki yana dubansa ganinsa cikin shiga ta kamala ya koma ya zauna dayan yace “me ye sunanka na duba ko kana cikin list din masu son ganinsa ? Shiru yayi ya kasa magana yana ciza lip’s d’insa na kasa security ya sake kallonsa yana  tambayarsa “uhm don’t worry bari na kirasa “better dan ba’a bawa Kowa damar shiga sai da izininsa  wayarsa ya ciro kamar zai yi kira ya koma cikin motarsa ya zauna yana tunanin yadda zai shiga cikin sauki .

”  Anas……..”
jabir  ya kira sunansa yana zama a gefensa “na’am jabir Anas ya amsa jiki a sanyaye”  everything will be fine naga duk ka damu tunda jaguwa ya bar gidan nan  “dole na damu jabir ina jinsa tamkar danuwana bana son wani abu ya sameshi bana son na rasashi yayi mgnr kamar zai zubar da kwalla “jaguwa ba kamar sauran mutane bane , gabad’aya alamuransa akwai lisssfi  ,yana da kaifin kwakwaluwa bazai bari mu rasa shi ba saboda yasan muna son shi “jabir nasan da haka nasan yana son mu duk duniya bashi da aminan da suka kai mu but bansan me yasa yayi irin wannan taurin kan ba ,nayi kokari fahimtar dashi nayi komai akan ya bar wannan aikin amman yaki ya kasa fahimtata jabir zuciyata na cike da tsoro yanzu idan wani abu ya sameshi  adalilin tango gote ya zanyi da rayuwata ? “Anas kana tsoro da tausayinsa with  reason nima zuciyata tana cikin damuwa amman abinda na lura dashi  yana sane so yake mu rasa shi inji cewar kamil wallahi idan wani abu ya sameshi bazan taba yafe masa ba yayi maganar yana goge hawaye “ba haka bane kamil  Anas ya fada shima hawaye ne cike da idanunshi “zai dawo   zai dawo anas ya dinga maimaitawa zai dawo da kafafunsa domin shi din ba mutun bane kamar sauran mutane mutun ne mai matukar amfani ga rayuwar mutane yayi handling din matsaloli a rayuwar data gabata ina da tabbacin zai dawo da kafafunsa suka rungume juna suna kuka ..


Alhaji tanko gote  zaune a cikin  tangamemen parlou’n sa daya ji kayan more rayuwar duniya tare da manya abokansa kowane hannunsa rike da glass cup  suna kurban ruwan  win yayinda gabansu table ne dake dauke da kayan itatuwa kala dabam dabam,tun daga kan ginin gidan da tsarin da’aka bi dashi za ka san mamalakin gidan attajirin ne,gidan  zagaye  yaje da flowers sannan  yafi Kowane gida dake cikin estate din kyau da tsaruwa  .

shewa ne ke tashi acikin parlou’n “mutunen  da zasu ce meye namu acikin lamuran   kasar nan ina tunanin mutanen sun tabbata    dakikai ne , domin daga kasar nan tamu har  zuwa kashen ketari sunanmu ya zagaya sannan a san da zamanmu,   maga Wanda ya isa yace meye namu acikin lamarin kasar nan bayan mune gwanati  “wannan haka ne inji cewar Alhaji amadu dan iya wanda ke fuskantar alhj tanko gote   “muna da tarin kudi muna da tarin mutane muna da hanyoyi daban daban akwai connection me muke so  acikin kasar nan da bamu samu ba  da har wasu zasu dinga cewa meye namu aciki ?  “babu ma wanda ya isa domin mune gwanati kuma ko ana so ko ba’a so dole a dama damu  kuma muyi abinda muke so  “wannan gaskiya  ne …

“waɗan kananun maganganun yasa  nake gudun shiga siyasa Gara na tsaya iya haka tunda duk abinda nake nema ina samu sannan ina juya waɗan da nake so  na bada umarni kuma abi inji cewar Alh Tanko gote   suna cikin hirar wayar Alhaji tanko gote ya ɗauki kara ya mike sanye da bakin kaya wando da riga da hula ya ɗauki glass cup  ya dauki  wayarsa ya miko dogon coridor din gidansa  sannan  ya ɗauki wayar  ya soma magana kasa kasa   “ranka ya dade  aka fada  daga dayan bangaren na turo  da kudaden  yanzu haka yarona na bakin get din  estste ” oooooo my  god me yasa baka da fahimta ni da nace a wuce akai kudi banki shine zaka turo min yaro madadin ma ka kirani na turo body guad “am sorry  sir gani nayi idan na turo kudin zaka fi maida hankali   “haka ne   kana da  fahimta dan   a daidai wannan lokacin ina tare da  shi wanda zai saka hannu   “to kagani sai ka  bashi ayi agama komai dan so nake ya fito zuwa jibi dan Allah kasa a kashe wani a madadin falsa ..” shikenan  a gama karkaji komai  ” zan bada umarnin a shigo da yaron  yanzu ya fada yana  canza magana “you have to understand that you should  know that what someone like us can do  in this land be left ,ya maida  wayar zuwa dayan kunnenshi  tare da shiga karamin parlou’nsa ya  bude window dining area  “nasani ranka ya dade  nasan zaka iya komai murmushi tanko gote yayi” ka kwantar da hankalinka komai zai tafi daidai cikin haka amaryarsa ta shigo  tana taku day day ta nufi inda yake tsaye ta rike hannun daya daga cikin kujerun dake zagaye da dining yana ganinta yayi saurin “cewa  I will call you later  uhm alright “my dear  ta matso jikinsa ya cire wayar a kunneshi yana rungumota jikinsa ya manna mata kiss tayi murmushi “darling  har na fara kewarka da tunanin tsawon lokacin da zaka ɗauka idan ka tafi hong Kong dan Allah kar ka dade  kamar sauran lokuta karka  ɗauki lokaci mai tsawo  bana son ka  dade ka dawo da wuri   duk yau sati ne fa da dawowarka  “uhmmm gaskiya ne amman this time a round just 1 month zanyi na dawo nayi wata uku ban fita kowace kasa ba   “really ?  ya gyada mata kai “idan zan dawo zan biya ta itly  “kai dan Allah tayi maganar a shagwa’be “dole na biya dan akwai abinda zai kai ni daga nan naga bilal  ta soma tafiya tana farinciki  yana biye daita  abaya suka zauna akan farar kujera mai zaman mutun biyu har zai ajiye wayarsa ya tuna bai kira securitys ba ya soma ƙoƙarin kiransu kira ɗaya suka ɗauka “hello sir daga ɓangaren Tanko gote yayi shiru yana tsotsa keya yana ciza baki saboda bai tambayi sunan yaron da aka aiko gurinss ba iska ya furzar yaceb”akwai wani yaro  yana ….
“Okay sir gashi nan ma “yauwa ku barshi ya shigo “okay sir ya katse kiran tare da janyo amaryarsa jikinsa “,zanyi missing din waɗan abubuwan ya kai hannu ya shafo qirjinta bata yi sanya a gwiwa ba ta kai hannunta ta soma wasa da sansar jikinsa kusan minti goma suna rungume da juna wayarsa ta sake ɗauka qara  ya zareta ajikinsa yana ƙoƙarin  d’aga wayar  gabansa yayi wani irin muguwar  faduwa  yayi shiru rike da wayar ya kasa ɗauka babu abinda yake ji sai faduwar gaba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button