KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Saurin mik’ewa yayi yana kallon parlou’n kansa na juyawa a matukar zabure amaryarsa ta mike “what happened ? “gabana ke fad’uwa da matsanancin karfi “gabanka ke faduwa ta maimaita tana kallonsa” ina jin kamar takun mutane “how is there tayi maganar tana kallon kofar parlou’n tayi maganar a tsorace ganin haka yasa ya riko hannunta “colm down never mind “what do You mean never mind ? tayi maganar a tsorace “don’t leave the parlou “ban fahimceka ba ? ” Ina zuwa yayi foring head d’inta kiss “i think I will back don’t leave the parlou ya juya ta riko hannunsa da sauri “karki damu zan dawo yanzu ya sake rungumeta ya mannata mata kiss ita dai a sanyaye ta bishi da kallo “meke faruwa ne haka daga gabansa na faduwa yace na tsaya anan na jirasa zai dawo tafiya yake gabansa na faduwa ya biyo dogon coridor da zai kai mutun wata kofa data fuskanci hagu ya fito a hankali yana dube dube har inda wata motar take parke yana dubawa gabansa na faduwa wanda duk sanda yaji haka yasan akwai wani mummunar abu da zai samesa cigaba da dube dube yayi a hankali ya juyo yabi wani hanya stil bai ga kowa ba bai ga komai ba, ya tsaya yana waige waige hagu da dama sannan ya sake juyawa ya nufi kofar daya biyo “Alhaji tanko gote……….”
yaji sauti daga bayansa cak ya tsaya tare da juyowa gabansa na wani irin dokawa a hankali Jaguwa yake daga kafafunsa “waye kai ? tambaya kake ko neman sani ? “duka ya fada cike da tsoro , jaguwa yayi murmushin “colm don Tanko gote zaka san komai cikin second daya yayi mgnr haɗe da ciro bindigarsa daga maajinta ya soma gyarawa yana kusanto inda tanko gote yake tsaye a matukar tsorace yake kallonsa da bindigar hannunsa alama su shiga ciki yayi masa babu mutsu ya juya Jaguwa na biye dashi har suka shiga parlou’nsa na uku ya tsaya ” ba wani abu ne ya kawoka ba illa kudin da’aka …
“Dakata kafin wannan kamar baka ganeni ba ?ya girgiza masa kai “Jaguwa yayi murmushin “daman mutane irinka basa iya gane mutane abinda yafi haka ma zaka iya saboda mutun azzalumi irinka ba lallai ne ya zamanto mara mantuwa ba well ba wannan ne abinda ya kawoni ba shiga ka fito dan zuwa yanzu ka fahimceni “sosai ai idan kudi ne zaka samu har sai kabari ni Dai ka barni da Raina da lafiyata “ban soma wannan aikin dan na dauki ran wani ba sai dai a rashin sani amman kai wallahi zan iya daukar naka take jikin Tanko gote ya sake ɗaukar rawa ….
” muje inda kudin suke jikinsa na rawa ya nufi wani daki suna shiga sanyi ac ya ratsasu buhu ne cike da kudade daban daban na kasar negeria da kasashen ke tare ka ɗauki duk wanda yayi maka “Jaguwa yayi murmushin yana shafa qirjinshi da hannu “ai gaba-daya zan wuce dasu dan haka ka soma ɗauka daya bayan daya “ka bari na bada umarni a kai maka su cikin motarka tana ina “ance maka ni karamin kwaro ne karka bata min lokaci ka soma abinda ya kamata kafin na fasa maka kwakwaluwa …..
Darling’s????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
WRITING BY
BAGUDO& MIMI’S QUEEN
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
????️09
…..Mamakin jin furucin Jaguwa na karshe ya cika zuciyar Alh tanko gote mutumin daya shahara a cikin fadin duniya da aikata masha’a bangaren neman mata cin amana ,makirci, son abun duniya ba dan bashi dashi ba ,daurawa mara laifi laifi domin bawa mai laifi gsky saboda abun duniya ,idan kana son ka kasance dan ta’adda mai lasisi da neman gindin zama acikin kasar nan nemi tanko gote,idan aikinka garkuwa da mutane ne fayde zama dilan kwaya da sauransu nemi tanko gote duk zai tsaya maka asirce kaci karen babu babbaka ko an kamaka zai sa a sakoka cikin kankanin lokaci ………….
Duk wannan mugun aikin daya ɗauki tsawon shekaru yana aikatawa adalilin connection din da yake da acikin yan siyasa babu wani mutun ko ɗan fashin da makamin daya taɓa kawowa rayuwarsa farmaki ,
hasalima yana jin sign dinsu ajikinsa kafin su karaso gareshi yake maganinsu , sai gashi yau da ranar Allah dan fashi kwaya daya tal ya farmaki rayuwarsa har yana masa barazana da rayuwarsa , jiki a matukar sanyaye ya soma jan buhun kudi jaguwa na gefensa “idan kayi wata alama da wani zai gane halin da ake ciki wallahi zan ɗauke numfashinka daga doron kasa sai dai nima a ɗauke nawa numfashin wanda daman ni da wannan shirin na fito mutuwa ko akasin haka ….. “
“Karka damu babu wanda zai fahimci komai ya fada hannusa na karkarwa, kai tsaye bayan but din motar Jaguwa suka nufa ya jefa buhun kudin da kyar yana haki , haka suka dinga jerewa suna shiga yana dauko buhun kudi har ya kwashe tasssss ya tsaya tare da nad’e hannunwansa guri daya har lokacin zuciyarsa cike take da mamakin irin gogewa da kwarewar jaguwa .
Jaguwa ya manna gun a gefen brain d’insa “muje ka kaini gurin yar gaban goshinka Alh tanko gote ya kalleshi a matukar frigice zuciyarsa na dokawa da karfi “karka taɓa lafiyar iyalina idan wadan nan kudin basu isheka ba zansa akawo ninkisu yanzu
” yayi kyau shugaban fataken dare sai dai kar kwakwaluwarka tayi maka wanann banzan tunani dan nasan daraja da kimar dan adam ba irinka ba wanɗa yake danne hakin dan Adam domin son duniya , a hankali ya dinga daga kafafunsa zufa na karyo masa a gaba-daya sansar jikinsa yana tunanin “waye shi wannan ? “da dukkanin alamun yasan shi farin sani har suka shigo parlou’n zuciyarsa na cikin frigici , yayinda har zuwa wannan lokacin amaryarsa na tsaye hankalinta a matukar tashe tana ganin bindiga a gefen brain din mijinta tayi saurin durkushewa bisa gwiwowinta tana furta “na shiga uku me zan gani haka ni salma ? Alama jaguwa yayi mata da bindiga take tayi shiru jikinta ya kama kyarma ..
“kin san me yasa na bukaci wannan azalumin mijin naki ya kawoni gareki ban bukaci ya kai ni gungu mattarar tsiya ba ? tayi saurin girgiza masa kanta jikinta na rawa “saboda nasan kece tauraruwar gidansa da dokarki ake aiwatar da komai na gidan nan , sai yadda kika so za’a yi dan tanko gote mijin tace ne agurinki sai yadda kikayi dashi “ki faɗa masa kar ya kuskura ya kawo wa aikina hauka , bayan wannan ya kamata ki san ko waye wanda ke tsaye a gabanki duk da idanunki a halin yanzu a makance suke ,”sunana jaguwa akaro na farko da wani a duniya zai san wani abu daya danganceni sannan ya san sunan dan fashin daya gagarin kasa da yan sanda “