KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48


A natse yake murza stearing  motarsa, lokacin  daya shigo unguwar  aguje  su  Anas dake  tsaye a kofar gidan  sukayi  gurin motarsa suna  murnar ganinsa, kanshi  kawai  ya  girgiza yana murmushin  sannan  ya saita hancin motarsa  get din gidan  , kamil ya zundumawa mai  gadi kira  ganin  zai ‘bata musu lokaci yasa  suka shiga sauri saurin  buɗe masa tafkeken get din  gidan  yana gama  karasa  shigowa ko gama daidaita tsayuwar motar bai yi ba  suka hau kiciniyar  bude motar  suka  fito dashi tare da d’aga shi sama  suna ihun jin dadin sake ganinsa   “Winner ooo winner Winner ooo winner ,Winner we don win ooo winner
Pata pata  we go win forever winner  suka nufi babban  parlou’n  gidan dashi  suka  zaunar dashi akan kujera mai zaman mutun uku , Anas ya karasa da sauri  ya bude fridge  ya d’auko  masa power  horse mai sanyi  ya bude ya  mika masa yana zama kusa dashi cike  da  tsananin murna jubi ya d’auko ruwa mai sanyi  “,wayyo  Allah nah  jaguwa nasan kasha wahala  ko da ganin yadda motarka tayi ” “babu wata wahala tunda gani a gabanku  yanzu”
a tare sukayi  dariyar jin dadi  sannan sukace “Allah  mun gode maka daka  dawo mana da farincikinmu lafiya  “shine  abun godiya  ya fada yana furzar da iska  “gasky kai  din na daban ne namijin duniya  ,jaguwa ya ɗan lumshe  idanunshi  sannan ya gyara  zamansa   ya soma ƙoƙarin cire yar saman rigarsa Anas yayi saurin cire masa jubi ya dawo gabansa ya soma cire masa takalmin kafafunsa  ya  saura safa  kallonsu kawai yake yana girgiza kai “kasan tun da ka bar gidan nan  babu wanda ya sakawa cikinsa wani abu tsabar tashin hankali inji cewar jabir “

“uhmm bari jabir ban taba tsintar kaina cikin tashin hankali irin na yau ba wallahi   da zarar na runtse idanuna sai inga kamar wani abu zai same shi  anas ya fada yana shafa fuskar jaguwa  ,ya ɗan juyo ya kalle shi yana haɗe rai “duk cikin murna dan ban maka kiss ba suka sa dariya gabadaya  “yau fa akwai celebrate jubi ya fada yana dauko musu kwaban win ya jere a gabansu  “kamar kuwa kun sani ,”ina zamu samowa jaguwa mai zafi data iya chilling fiyye da zahra ?
“ai babu wata  mai zafi sosai data wuce zahra ita zan kira yanzu “zaro ido jaguwa yayi “lallai ku yanzu  wannan  shirmen ne a gabanku ni yadda zanga ammina nake tunani ba wannan shirmen ba “
“Ogbeni ejalo shaye jare Oti sele oppprr kpk Eyonla chuwale sir???????? se kinwa gbenusi no be atenu ” zaka gun ammi amman amman dole zahra zata yi aiki “

A hankali Anas ya kira su eku remo cikin minti goma  suka karasao suka  shiga fito da buhuhun kudadde da jaguwa yazo dasu  suna shigowa dashi daya bayan daya  , yayinda su Anas ke zaune suna mamaki yadda har ya iya rabo  tanko gote da wadan nan  makudan kudaden shi kadai , cikin  minti da bai wuce goma ba sukaji mai gadi yana  kwankwasa kofa jubi ne ya tashi   ya tsaya daga bakin kofa ya bude , cikin yaren turanci mai gadi yace  “akwai wani bako da yake ta zuwa gidan nan yau shine zuwansa na biyar baya samun nasarar ganin  oga yana fama da matsalolin rayuwa ne gashi yana da yarinya  mara lafiya mai kimanin shekara goma  tana igondo  general  hospital ,likitoci sunki bata kulawa sakamakon rashin kuɗi , kafin  jubi yace wani abu  jaguwa  yayi  gyaran murya , juyowa jubi   yayi a hankali  ya  dawo inda suke ya tsaya yana duban jaguwa  nuna masa wata yar kamara jaka mai zip yayi da hannunsa  “zuba masa adadin da zai cika jakar nan ka bashi “yesssss boss an gama Allah yaja da nisan kwana ,jakar  ya cika da kudi  yayi ziping  dinsa  ya mikawa mai gadi da hanzari mai gadi ya amsa jakar ya rungume  ya juya ya  nufi kofar waje ya mikawa mutumin  , mutumin na ganin kudin gabad’aya ya rude ya gigice ya soma  wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya,lallai baa rasa na allah koina kuma yadda aka bashi labari wannan matashin mai tsatsanin kirki da tausayi haka ne,  take ya nemi mai gadi da yayi masa iso gurin mai gidan domin yi masa godiya , amman mai gadi  yaki saboda sanin da yayi wa jaguwa baya son godiya ko kyauta yayi maka kace ka gode sai yace ka godewa Allah  ,duk da ban samu ganinsa ba tabbas zan dangwama ina yiwa rayuwarsa addua  domin allah  ya  buda masa  kofofin  farinciki kamar yadda  yayi min , iri mutanen da ake so kenan  masu taimako dan allah”
” karka damu ba kai ba duk wanda kaga yana bukatar taimako kana iya masa hanya wannna gidan gidan masu tallafawa rayuwa marasa shi ne da marasa galihu a haka nasan shi da zaka zo kofar gidan a duk safiyar allah zakayi mamakin yadda mutane suke shawagi kayi masa adduar kamar yadda ka kudurta domin shine zai zama tsani na rayuwarsa “mutumin ya sauke numfashi ya kama gabansa yana masa addua.

Duk yadda yake kallon buhubuhun  kudaden dake gabansa  hakan bai sanya shi jin  farinciki ba, waɗan nan  makudan kudadde daya amsa daga Tanko gote ba zai taɓa  goge  abinda yayi masa  a shafukan rayuwarsa  ,sannan bazasu taɓa  maida masa  jin dadin daya rasa a shekarun da suka gabata ba, fuskar ƙaramar  kanwarsa ne ya shiga yi masa gezo a lokacin da numfashinta na karshe ke shirin barin gangar jikinta tana kallonsa hawaye na turereniyar zubowa daga kwarnin idanunta bakinta na amai jini  ,yayinda  mahaifinsa da mahaifinyarsa ke manne da jikin bangon daki  sun dawo tamkar matattu a tsaye  tsabar firgici da tashin hankalin halin da diyarsu ke ciki   kukan  zuci dana zahiri suke   a wannan lokacin har rai  yayi halinsa wanda sanadiyyar haka zuciyar mahaifinsa ya buga take shima yace ga garinku …….”

“Anas ya dafa kafad’ansa   saboda yasan abinda yake  tunani “ka manta da abinda ya faru, jiya ta wuce mu fuskanci yau samun waɗan kudadden kadai ya isa ya goge abinda ya faru a zuciyarka  sannan waɗan nan  kudade  zasuyi maka abinda basu yi maka a da can baya ba “

“bazasu yi ba Anas rayuwar mahaifina data kanwata sun fi min waɗan nan  kudadden  mahimman … hatta mahaifiyata da zata san abinda ke gudana a rayuwata  zata iya saka hannu cikin raba Tanko gote  da duk wasu masu hali irin nasa daga duniya  “me yasa bazaka ɗauke shi daga duniyar gaba-daya  ba kowa ya huta ?inji cewar kamil , girgiza kai jaguwa  yayi sannan ya fashe da wani kuka mai cin rai da ban tausayi yana tuna rayuwar da suka yi a baya shi da yan’uwansa rayuwar kunci da talauci da rashin galihu , a hankali komai  ke dawo masa gabad’aya sukayi kanshi suna bashi baki da hakuri “

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button