KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

   “sweety   kina  ina ?” Ina gida  kwance wallahi Ina hutawata  ” bazaki  fito bane  ma yau  ? cikin Marairaicewa murya Zahra   tace “da wahala na fito Ina son na  cigaba da kame kaina a gida dan ta haka ne  kawai  burina zai cika akan Adnan idan ya daina ganina a guraren shakawata ko  hotel hotel   may be zai yi kewata  har ya nemini ,ni Kuma ta haka zan bijiro masa da lallai sai dai muyi aure “wani dogon  tsaki helen taja  “Kinga ki raba  mutane da zance wani  Adnan  mutumin nan ba aurenki zai yi ba sau nawa yana fad’a miki bazai aureki ba amman da yake ke karamin brain gareki kin kasa ganewa? “me Kuma ya kawo wannan maganar  sweety ? kin kirani ne  dan ki ta’ba zuciyata  ko me ? Ko d’aya na kiraki ne dan na fahimtar dake wani abu me mahimmam na tura miki Sako ta what’s app dinki ki shiga ki duba  idan  km zaki iya zuwa  Rita  Lori  hotel yanzu  kina iya zuwa  ki ganewa  idanunki  komai  tana gama  fad’ar  haka ta katse  Kiran  .
zahra tayi shiru  sororo da waya a hannunta tana tunanin maganar Helen what’s app dinta ta shiga nan idanunta suka ci karo da mugun Abu domin kuwa  adana  dinta ne rungume da  wata yarinya  da bata san  kowacece   ba , ta sake bude wani hoto su din ne yarinyar na tsaye a gabansa shi km  yana rike da kugunta wani irin abu taji yayi mata diran makiya a qirjinta nan take ta  fara  jin  zafi   a zuciyarta  tasa hannu ta dafe daidai saitin zuciyarta adalilin bugawar da take .

  take gumi ya shiga  karyo mata ciwon  daya dade yana damun zuciyarta ya sake taso mata ya mamaye kahon zuciyarta , wannan alamarin akwai ciwo, ciwon da mikinsa ke azabtar da zuciya da gangar jikinta ,ciwon da kullum yake qara girma acikin zuciyarta, tunda ta fara son Adnan ta tsani ganinsa da kowace mace sannan   Kuma  zuciyarta ke cikin tashin hankali , ta zabura  ta mike ta sauya kaya  riga fara sol  iya gwiwarta ta sakala jaka fara , haka ma takalimi fari   ta fito cikin sauri tana  Uber  ,cikin kankanin  lokaci mai Uber ya k’araso dan yana kusa  daita, ta shiga gidan baya ta kame zuciyarta na wani irin zafi da ciwon da batasan ranar dainashi ba “why Adnan?  me na
 rasa ? “me kake so ajikin mace da bani dashi ?.me wannan yarinyar ta fini dan Allah karka bari bakincikinka ya kasheni Ina sonka fiyye da komai ta k’arasa maganar tana goge hawayenta  ..”

tana gama  karasowa Rita Lori ta sallami  me  Uber sannan ta  kira layin Helen kira daya  ta d’auka tayi mata kwatance gurin da suke  zaune .”ta k’araso ciki  hankalinta a matukar tashe  tana baza idanu taga ta  Inda jaguwa  yake  da yarinyar  dan  idanunta babu abinda suke son da burin  gani    agurin kamar  tagansa   aiko  cikin sa’a idanunta  ya  sauka akansa   makale da tanweer  kamar  zai  mata  numfashi  ita Kuma  ta d’aura  kanta a saman  kafad’arsa  saboda  baccin data soma  ji  ga sanyi gurin dake ratsa  jikinta ta shige masa sosai har suna  iya jiyo numfashin juna  tuni  idanun Zahra suka  kawo  ruwa  wani tunani yazo  mata  ko dai yayi aure  ne ?”  kai impossible ace  Adnan dinta  yayi aure Kuma ko yayi aure  bazai  ta’ba  zuwa da  matarsa gurin nan ba sai  dai  idan  sabuwar karuwa   yayi  wani  naunayen  ajiyar  zuciya ta sauke  ,hankalin   zahra yayi kololuwar tashi gadan  gadan  ta nufi Inda  suke  zaune  tana gama  Isa  gurin tasa kafarta  d’aya  ta  take kafar  tanweer  qara ta saki mara sauti tana furta ” subhanallah   tare da  runtse  tsamammun idanunta  dake  cike da mayen  bacci  ,a hankali jaguwa yabi  inuwar da ya gani tsaye  akansu  itama tanweer  ta d’ago  domin taga  abinda ya take mata  kafa  kafin tanweer ta gama kare mata kallo har zahra ta cakumi wuyan rigarta da iyakacin karfinta  “dan  ubanki me kike  yi tare da mijin da zan  aura ? nan da nan jikin tanweer ya d’auki rawa  wata razananniyar tsawa zahra ta buga mata wanda yasa jikin tanweer ya sake d’aukar qyarma  zuciyarta ta karye hawaye ya soma sintiri bisa  kuncinta muryarta na rawa tace “ki…kiyi hakuri wallahi  babu komai a tsakaninmu kawai  tai …”
“Shut up useless kawai  hakurin uwarki zanyi  ko da yake da ganin  nasan kema  sabuwar  shigowa  karuwanci  ce  bancin haka da  Koda  millioyoyin   kudi  ba zaki Kalli  Inda Adnan yake ba bare har ki yarda ya daukeki “inna lillahi karuwa?  ta furta kalmar a matukar firgice .

cikin tsananin faduwar gaba jaguwa ya lumshe sexy  eye’s dinsa na second  biyu sannan  ya bude su fess   yana mai jin  bakinciki mara misaltuwa sam bai ji dadin Kalmar  data fadawa tanweer ba   murya qasa qasa yace ” ke  wacce  irin mahaukaciya  ce  daga zuwanki kin  fara wa mutane  hauka saboda ke din mara mutunci ce ki saketa  kafin na tashi na  targadaki  yanzu  yayi maganar  yana  janye idanunshi  akanta tsayuwa zahra ta gyara sannan ta maida dubanta ga jaguwa tana  kira sunansa kusan minti biyar tana Kiran sunansa batare da ta saki wuyan tanweer ba  ranta ya Kai koluluwar baci wato cin mutuncinsa gareta yayi yawan  da  zai  mata a gaban  sabuwar karuwarsa yana jinta yaki amsa mata  yayi  kamar bai san da tsayuwarta ba “Adana !!!! ta qara Kiran sunansa a fusace wannan karon  idanuwansa  a  lumshe ya  mike ya ɗauketa da wasu maruka har biyu ajire   da sauri  ta saki  wuyan  tanweer  zuciyarta na bugu  da  karfi “ka mareni adnan ?na mareki idan kika sake wata magana ko kiran yarinyar nan  da karuwa sai na  ballaki  sannan   minti biyu  kawai  na  baki ki ‘bacewa  idanuna banason ganinki .

tai shiru ta  kasa aiwatar da hakan  “haba wannan naci na menene haka ki bar rayuwata ko dole sai munyi  rayuwa tare ? ya fad’a yana kafe tanweer  da sexy  eye’s dinsa wayanda kallonsu  kadai ke haddasa mata shiga wani hali  zahra ta girgiza masa Kai alamun bazata iya rabuwa dashi  ba “bazan iya ba Adnan  ta furta qirjinta na dokawa da matsanacin karfi” kiyi  kokarin ki iya dan nafi bukatar haka Ina son ki bar rayuwata ki manta kin taba haduwa da Adnan arayuwarki yana gama fad’ar haka ya riko hannun tanweer ya soma tafiya daita a hankali .”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button