KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

cikin kankanin lokaci ya k’araso gida  Kai tsaye bangarensa ya wuce da tanweer ta tsaya tana dubansa “ki kwanta ki cigaba da baccinki nasan bai isheki ba “batun komawata  gida fa ?”zan maidake amman ba yanzu ba  ki bani lokaci tayi kicin kicin da ranta kamar wacce aka aikowa da sakon mutuwa  “gsky nifa na gaji wallahi gida nake bukata idan baka yarda ka maidani ba  zan bi ta kowani hanya na bar gidan nan  “ki gwada ki kigani idan hakan abu ne me sauki yayi mgnr tare da yin  shiru yana dubanta  dan tuni idanunta sun cicciko da ruwan hawaye “ban San me yasa kake min haka ba ,idan km kasan kana da dalilin rikeni ka fad’a min nasan zaman da nake yi amman bawai ka rikeni ba alhalin ni din ba muharamarka bace  ta k’arasa maganar tana jan numfashi da danne kukanta tabbas  jikina na bani akwai  sirrin da  kake boye min meye shi  Ina son sani ?”.Tayi taku daya  biyu ta qaraso gabansa qirjinta na dokawa da matsanacin karfi ta cigaba da magana a natse zuciyarta na rawa “zuwa yanzu ya kamata ka sanar dani menene shi abinda kake k’okarin  boyewa ” take jikinsa yayi sanyi kmr Wanda aka jefa cikin kankara “zuciyata ta fara jefo min abubuwa masu wuyar misaltuwa akanka  sai dai na shirya jin koma menene ta k’arasa maganar tana kuka dan ta kasa rike kukanta .”

ya Kai hannuwansa duka yana  qokarin zagaye kugunta ta zame jikinta  ta koma bakin gado ta zauna ta kife Kanta akan cinyarta  tana cigaba  da  kukanta ya k’araso ya janyo stood ya zauna a gabanta ya riko hannunta daya cikin nasa ta d’ago runannun idanunta ta zuba masa tana sauraron abinda zai ce sai daya furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya fara magana a natse kmr me koyon mgn  “kunnewanki  bazasu iya Jin dalili
ko sirrin dayasa nake rike dake a gidan  ba , hankalinki bazai iya dauka ba wallahi zuciyarki zata buga idan kikaji mafi alkhairinsa ki bar wannan maganar “na bar wannan maganar saboda me byn kana rike da rayuwata ka tsareni ka hanani naje ga iyayena alhalin suna cikin damuwar rashina ta k’arasa maganar tana fixge hannuwanta ya sake riko hannuwanta da sauri  “shikenan ki bani  lokaci kad’an  nasan dai bazaki sake d’aukar lakacin da kikayi tare dani  ba a gidan  nan “.  ya qarasa mgn Yana  goge mata  hawayenta dake tsiyaya a idanunta  tare da yin shiru yana  kallonta itama shi take kallo  zuciyarta  na zafi “to shikenan amman kayi min alfarma ka bani waya  Ina son Jin muryar iyayena ,Ina kwadayi jin muryarsu dan Allah karka ce a’a”.

” ya  mike  tsaye yana cewa  “zanyi  nazarin  akan haka  yana gama fad’ar haka ya fita daga d’akin ta kwanta sharaf  akan makeken gadonsa tana kuka tana  tunanin yadda zata bar gidan  ta kowani hali .Kai tsaye d’akin ajiya makamansa  ya nufa Inda ya iske  abokansa  da yaransa suna zaman  jiransa a hankali  ya shiga yi musu bayanin Inda kowannensu zai tsaya da zarar sun Isa  airport ya d’auki sama da awa biyu yana  musu  bayanin har sanda  karfe  goma shabiyu  ta buga  ya d’ago yana duba agogon dake d’aure  a tsintsiyar hannunsa  a natse ya d’auke kyawawan idanunshi ya d’aura akan   Scorpio tare da bashi  umarni  “kaje ka siyowa  tanweer  abinci ya lumshe sexy eye’s na second biyu sannan  ya Bude ya  jiyo ya Kalli  eku “Kai  Kuma  kaje ma’ajiyin  kudi ka diba ka  siyo kayan  d’anye abinci da duk abinda kasan za’a bukata na abinci ka tabbatar ka siyo “okay boss “.
gbdy  abokansa suka zuba masa Ido kawai suna kallonsa cike da tsananin mamakinsa ” kamil ne yayi karfin halin tambayarsa “me za’a yi da  d’anye abinci  Kuma ?””Wa wannan  yarinyar ne ya bashi amsa atakaice yana furzar da iska , duk da  yaki  yarda da  son yarinyar  yake  amman su sun fahimci  matakin soyayyar  da  yakewa yarinyar , soyayya ce me zafi  da  wuyar bari, soyayya ce da mutun bai Isa ya iya barinta ba  cikin dadin  rai    ” jaguwa  amman dai ….” saurin  d’agawa  anas  hannu yayi  saboda yasan  me  zai fito daga bakinsa “ya zaka katseshi ka barshi yayi magana mana ?”.bazan barshi ba dan nasan maganarsa  iska ce da shirme  ya fad’a yana runtse idanuwanshi tare da shafa sumar kanshi  . kamil yace “kenan mu din yan iskanka ne sannan mashiririta  ? tsuke bakinsa yayi yana kallonsu d’aya byn daya yana girgiza musu Kai  alamun a’a “haka ne mana jubi ya fad’a “ada Kai din mai son a fad’a maka  gsky ne amman me yasa yanzu  duk ka canza bafa ayi haka damu  ba ,ba’ayi damu zamu d’auko yarinyar mutane mu ajiyeta ba meye ma amfanin rike musu yarinya idan kana son yarinyar why not ka fada mana mu san abunyi ?”no no jubi  Sam babu wannan a raina ta ya ma zan d’aukarwa  kaina soyayya  soyayyar ma da diyar minster Sam Sam hakan ba me yiwu bane ?
“me yasa zaka fadi  haka byn zuciya gareka kamar  kowani  halitta “kunga dan Allah ku bar maganar nan haka, bama zan iya wata soyayya ba a yanzu  kawai dai Ina gudar mata  sharrin wannan mutumin ne  me  Katon ciki  ban San wani tuggu zai sake had’a  mata ba  Ina tausayinta Ina Jin kamar zai cutar daita ne Idan na mayar daita  “,saboda zunzurutun qaunar da kake  mata  ba  shiyasa kake Jin tausayinta “,oh my god jubril wai ya kuke min haka ne ?”idan Ina son yarinyar nan wallahi zan fad’a muku dan bamu Saba boyewa juna komai ba , ku yarda bana son yarinyar nan ” shiru sukayi  suka cigaba da kallonsa  ba dan sun yarda dashi ba  har ya juya  ya kusan kofar fitar  sannan yace ” eku   Scorpio  “zaman munafurcin  me kukeyi  dan Allah ku tashe kuje kuyi abinda na sakaku bamu da lokaci ”  da sauri suka mike suna shafa kansu  .”

       
Cikin  takun  Isa  da Jin shi wani ne  ya nufi  haraban   gidan  hannunsa d’aya soke  cikin  aljihun  wandonsa   eku da Scorpio   suka  fice da  sauri  suka nufi Inda  ya aikesu , yana  nan tsaye yaga fitowar   tanweer   tana  karewa haraban   gidan   kallo  fuskarta d’auke da   murmushin  jin dadi ba kamar   d’azu   ba ,  a kallon   da  yake   mata    ya   lura   hankalinta   na   kan   shukokin     gidan    ne  ,yana  kallonta  ta   cigaba    da    takawa    a hankali   har   ta  Isa   Inda   shukokin suke  tana  shafawa   a hankali  tana lumshe idanu , a  natse   ta  karya  kwana  tabi hannunta  na   hagu  ,cike  da natsuwa ya biyo bayanta , bata tsaya koina ba sai  gurin   fararen   fure  dake shuke   cikin  ruwa  har  lokacin  fuskarta da murmushi , ya  k’araso  ya  tsaya  a bayanta   yana  sauke numfashi, saukar  numfashinsa  yasa ta juyo  a  tsorace  har qirjinta na ta’ba  nashi  saurin  d’auke numfashi yayi qirjinsa  na tsananta  bugu ,  ganin  shine  tsaye  yasa  ta sauke  naunauyen  ajiyar zuciya  sannan  ta juya ta cigaba da kallon fararen  fure  muryarta a sanyaye  tace ” ina son fararen fure ko zaka tsinko  min? ta fad’a tana duban Inda yake  tsaye  har lokacin  hannunsa na  soke cikin aljihunsa ” kina son fure ne haka ? ya tmbyeta  yana  kare  mata kallo  tsab ” sosai Ina qaunar fararen  fure arayuwata  ya  qara taku biyu  yayi kusa  daita sosai yana cewa   “yarinyar da nake so itama  tana matukar son fure ” qirjinta ne yayi wani irin bugawa da karfi , taji saukar maganarsa  kamar  saukar aradu ,zafi ta dinga ji a qirjinta tamkar ana diga mata ruwan dalma  nan take ta nemi natsuwarta ta rasa    idanunta na kan furen tace “wacece ita yarinyar da kake so ? ta tambayesa  kwayar idanunta cikin nashi ,bai  bata  amsa  ba duk da ya lura da canzawar da tayi a lokaci  daya  sakamakon  jin yana son wata  dariya taso  subuce  masa dan  yadda  ta had’e rai abun babu sauki kace shi din mijinta ne .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button