KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

ranta a  ‘bace ta soma tafiya zuwa wani  bangaren “ke   Ina   zaki  ?itama banza  tayi masa kamar yadda yayi mata  “ba dake nake magana ba kina jina ? still banza ta masa ” ki   koma  ciki  kar  na   sake  ganin  kafafunki  kin fito  haraban  gidan nan bare nan. “dan   me  yasa bazan fito ba ? ta fad’a a fusace  tana Jin wani irin zafi mara misaltuwa sannan   ta juyo ta fuskancesa  fuskarta a had’e tamakr ba itace take murmushi a sakwanin da suka wuce  ba , ta rasa dalilin wannan so da take masa  , soyayyarsa me  karfi ce  agareta  ,bata ta’ba sanin  tana  da  kishin irin haka ba sai yanzu daya  furta  yana  son wata ba ita ba  yace baya son zahra sannan baya sonta to wacece wannan daya furta da bakinsa ?   Ido  cikin Ido suke kallon cikin kwayar idanun  juna  kamar ta rufesa da duka ko zata samu sausauci ,k’okarin danne kishin tayi ta sanyawa jikinta  jarumta   “ko bazanje koina ba ka barni na dinga  fitowa Ina ganin fararen  fure tayi mgnr kmr zatayi kuka ,bai ce mata Komai ba   ya riko tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita bai tsaya a koina ba sai d’akinta ya bud’e kofar ya turata “iya nan na yarda kiyi rayuwa aciki ko falon gidan nan ban yarda ki fito  ba  idan Kuma kikayi kuskuren fitowa zaki  ga abinda zan miki ya k’arasa maganar tare da  ya janye kofar ya rufe garam , ita duk wannan abun  da yayi  bai dameta ba akan zance budurwa da  yayi  mata shi yafi komai ta’ba zuciyarta  da d’aga mata hankali, tsaki taja yafi sau goma ajere  ” Allah! Allah !! ka tsi ….” shiru tayi ta kasa tsine masa shi da budurwar da yake so  ta koma karshen gado ta zauna tare da zuba  tagumi  .”

ya  shiga d’akinsa  ya cire kayan jikinsa ya shiga  wanka ya tsaya  shiru cikin bathtube ruwa na tsiyaya a sansar jikinsa  yana tunanin maganar abokansa  akan yarinyar “duk suna min kallon d’an soyayya alhalin ba haka bane acikin zuciyarsa ,” taimako ai  ba soyayya ce?  ya tambayi kanshi  ya  d’an dade ruwa na sauka ajikinsa sannan ya fito kugunsa d’aure da farin towel wanda bai wuce cinyoyarsa ba   byn ya goge jikinsa
ya shafa body lotion yayi cumb din sumar kanshi ya soma shirya kansa cikin Kanana kaya  riga blue wanda a gabansa  aka rubuta  polo  1967  yayinda wondon  da canvers din kafafunsa suka kasance ja ,kansa sanye da facing cap ja kmr yadda rigar jikinsa  yake , tsintsiyar hannunsa  d’aure da agogon  rolex   ya rufe idanunshi da  glass baki  ya feshe ilahirin jikinsa da turare mai sanyi kamshi, sosai  kyawunsa ya bayyana ya soke hannunsa daya cikin aljihun wandonsa kamar Koda yaushe ya nufi kofar fita,  falon ya dawo Inda ya iske scopio ya dawo bai tsaya bata lokaci ba ya karbi farar ledar hannunsa ya juya zuwa d’akin da tanweer  take .”

 tana Jin shigowarsa amman  taki  d’agowa daga kwance da take  dan wani irin haushinsa take ji ,ya ajiye ledar akan bedside yana cewa  “ga abinci nan ki tashi kici sannan zanje  wani aiki me mahimmanci  zan dan dade kafin na dawo batare data d’ago ba tace “a dawo Lafiya amman dan Allah ka bani waya “. “ki  daina  damun kanki ba waya ba gidan ma zaki bari gbdy  idan lokaci yayi  ya juya ya fara tafiya  cikin hanzarin wannan karon d’akin dake gefen  d’akinsa ya shiga ya jima sosai dan kusan awa d’aya  yayi sautin muryar scopio ya fito dashi “boss komai ya kammala “okay kana iya tafiya   ya fad’a d’akin tanweer  yana cewa ”   nasa a kawo  komai na kayan abinci muje kiga kitchen  din “. banza tayi masa taki cewa komai hakazalika taki tashi hatta abincin da ya kawo bata ci ba   ya zuba mata Ido har kusan minti biyar  kome ta tuna tayi zumbur ta mike tsaye tana dubansa  yayi gaba ta biyosa a baya har cikin had’ad’d’en kitchen din .”

a hankali ya dinga nuna mata komai daki daki kitchen  din  very Niet  kamar mace ce ke amfani dashi  babu abinda babu na kayan abinci  komai gashin nan  ajiye   yasa  an  kawo,” ki duba ko akwai abinda bai miki ba a canza akawo miki wanda kike so “.  idanunta  da suka canza kala sukayi jazir  tsabar kishi ta d’ago ta sauke su akan fuskar  jaguwa dake tsaye a gabanta  yana kare mata kallo ,Shep dinta yafi komai daukar hankalinsa irin  matan nan ne masu  shep din cocakola   “dan tani da baka tanadin wad’an nan abubuwa ba dan ba sune abinda nafi bukata ba bukatata na ..” “.shiiiii ya d’aura yatsansa akan lips dinta yayi kusa kusa daita har suna iya jiyo numfashin juna wani irin tsalle zuciyoyinsu yayi  wanda har sai da hakan ya haifar musu da tsayuwar numfashi , take jikinta ya soma kyarma   rungumeta   ajikinsa  yayi tsam yana busa mata numfashinsa .
 tuni zuciyarta ta karye hawayen kishinsa da kewar gida   ya soma zuba bisa kuncinta ya rungumeta  sosai ajikinsa kamar zai mata numfashi yana shafa gadon bayanta .

wani irin haushi  ne  da bata ta’ba  jin irinsa  ba  ya diran mata a kahon zuciya  ,kullum yana ikararin baya sonta amman ya iya nesanta kanshi daita yana son maidata yar  iskar karfi da  yaji   ta soma mutsu mutsun kwatar  jikinta domin zuwa wannan lokacin   zuciyarta  ban da zafin  kishinsa babu komai aciki ,ganin yaki sakinta yasa ta soma dukan qirjinsa da iyakacin  karfinta amman yaki sakinta  ya kamkameta tsam  yana son yaga karshen karfinta   “Kai dai wallahi mugu ne Kuma azalumi inshallahu yadda kake quntata min wallahi Kai ma sai Allah ya  quntatawa  kannenka “.  cak  ya saketa   yana furzar da numfashin mai zafi  daga bakinsa   idan  akwai abinda ya tsana bai wuce a ta’ba kannensa ko aibantasu da mugun abu ba . ta zube kasa bisa gwiwowinta tana wani irin kuka tare da Kiran sunan iyayenta , muryarsa  a tsarke yace”tan ….”bata d’ago  ta kallesa ba “karki sake sako kannena cikin shirmenki   idan kina son ki zageni kiyi amman kannena karki sake .”
“Dan Allah malam ka min shiru daga yanzu  muddin  baka maidani ga iyayena ba  wallahi na dinga ma kannenka  mugayen fata kenan , ada na dauka ka taimakeni  ne sai dai a yanzu taunina ya  Kashi dabam dabam tare da tambayoyi masu wuyar amsawa “waye Kai Adnan ? Ka fad’a min waye Kai Ina son sani kai din  waye ?cikin sauri ya juya ya bar kitchen din   zuciyarsa na rawa bai ta’ba Jin tsoron wani yasan sana’arsa ba ko sanin ko shi waye  sai yau , bazai iya sheida mata shi din waye ba , zai barta a matsayinsa na me taimakonta  bazai ta’ba yarda tasan ko shi waye ba yana tafiya yana jan tsaki ji yake kmr zuciyarsa zata buga .
ya rufe kofar falon ya fita zuwa  haraban gidan , tuni su  kamil ,anas, jubi, da jabir  da sauran yaransa sun hallara har wasu ma sun shiga mota sun zauna  shi kadai suke jira yana daf da karasowa eku ya  bud’e masa gidan baya ya shiga yana  cewa “hope  kowannenku  yayi shiri  me  kyau? ”  sosai  suka bashi amsa  motarsu na kokarin fita daga gidan Idanunsa  ya sauka  akan wani dattijo  zaune a gindin bishiyar dake gefen gidansa nan take yace wa eku “stop ! “.eku  ya tsaya   nan take mutumin ya mike tsaye yana kallon motocin  jaguwa masu shegen kyau da  daukar hankali da hannu ya yafito  me gadi  ya k’araso  da d’an saurinsa  ya   tsaya yana rusunwa  “wacan mutumin fa me yake yi  anan ? “wallahi oga gurinka yazo wai yana son ganinka tun jiya byn fitarka yazo nace baka nan shine dazu byn dawowarka sai gashi ya dawo  na  shiga domin nasar maka sky  yace Kuna meeting shine na dawo na sheida masa ya dawo Koda karshen sati ne amman yace lallai sai ya ganka .”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button