KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

shiru  jaguwa yayi  yana nazari sannan ya dan Kalli Inda dattijon  mutumin yake tsaye cikin kod’ad’un kaya marasa fasali  yana cigaba da nazarinsa ,a hankali ya fito ya soma tafiya   har ya k’araso garesa , dattijon na ganinsa ya shiga rawar jikin “barka da fitowa ranka ya dade  “barkanmu  baba ya kwanan iyalin ?” Alhamdulillah duk muna Lafiya  ,
jaguwa ya kad’a Kai sannan yace  ” baba fatan  dai lfy kake son ganina ?”dattijon ya marairaice murya  kmr zai yi kuka sannan ya fara mgn muryarsa na rawa gwanin tausayi “daman matsalace ke tafe dani gareka a wajen mutane na samu labarin irin taimakon da kake yiwa mutane “.  jaguwa na jin haka ya sauke numfashi yana dubansa a tsanake  ” Ina Jinka baba wacce irin matsalar ce ?”daman akan yarona ne  shekararsa biyar kenan da kammala karatunsa  na  degree sai dai  yadda kasar nan tamu ta  dawo yasa  har yanzu yake gida zaune, duk Inda yaje apply din aiki sai ace sai ya biya kamin dubu dari biyar kudin office kafin a daukeshi  gashi  bashi da hanyar da zai samu kudin,  ni ya kamata na biya  masa ya samun aikin  to ni din ma babu dan na abinci ma da kyar muke samu, dan Allah ka taimakeni kamar yadda Allah ya taimakeka  ka samo masa aiki ko Kuma  ka yarda ya kasance a karkashinka ya karasa maganar yana zubar da hawaye .”

jaguwa yayi shiru yana sauraronsa har sanda ya dasa aya “karkayi kuka baba    inshallahu zan yi iyakar kokarina  yanzu dai Ina kan hanya ne zani wani  aiki amman ka dawo zuwa  karshen sati da yaron   inshallahu matsalarka  tazo karshe dattijon ya soma k’okarin durkusawa jaguwa domin yi masa godiya, jaguwa  yay saurin sa duka hannuwansa ya taresa “haba baba karka min haka  mana ” na gode  d’ana Allah ya albarkaci rayuwarka , Allah yasa ka gama da duniya lafiya ,Allah ya jikan iyayenka  idan sun rigamu gidan gsky, idan Kuma suna raye Allah ya Kara musu Lafiya mai amfani na gode na gode  daman da gaske ana samun mutane irinka  ?karka damu baba ya k’arasa maganar yana tsaida dattijon bisa kafafunsa ya Ciro  dubu goma  a  aljihun wandonsa ya mika masa “ga wannan kayi kudin  mota  yana gama mikasa ya juya ya shiga mota suka bawa motacinsu wuta suka bar unguwar ,da sauri dattijon ya Ciro  wata rubabbiyar   wayarsa ya shiga neman  number d’ansa  domin yi masa albishiri  .”


Bangaren  minister of health  kuwa  gbdy  hankalinsa yaki kwanciya   kullum yana manne da hjy zainab yana rarrashi wacce kuka ya zame mata abincin ruhinta , yanzu ma zaune yake kusa daita  yana aikin daya  saba tare da babban  amininsa alhj Tahir  dake k’okarin shawo kanta   “kada kiyi fushi  da hukuncin  Allah  zainab  wannan  abu daya faru gbdy bai mana dadi ba sai dai  bawa  baya wuce qaddararsa  Allah ya rigada ya  qaddaro surayya zata fad’a cikin wannan tashin hankali bamu Isa mu canza mata qaddararta ba,  fatan mu  dai Allah yasa bata cikin tsanani cikin muryar kuka tace “na kasa  jurewa   dady  dake hk take kiransa kmr yadda Ib ke kiransa ”  yau  da mutuwa tanweer tayi na binneta da  zan fi samun natsuwar zuciya  amman Ina raye tanweer  tana hannun  ‘yan fashin da ko labarinsu ba’a samu ba , taya kuke tunanin hankalina zai kwanta ?”.  Suma kiramu muji me suke  bukata daga garemu sunki  ta k’arasa maganar tana kallon saman falon hawaye masu zafin gaske na gangaro mata wanda zafinsu da rad’ad’insu ya wuce tunanin mai karatu .
“wannan haka ne  amman duk da haka  addua zamu  taru muyi allah ya bayyanata cikin koshin lfy “amen ta furta a kasan makoshi tana cewa ya jikin Ib kuwa?   kullum Ina sa ranar zanzo na dubasa   mutanen dake shige da fice agidan nan  zuwa jaje ke hanani  fita ammn inshallahu zan samu lokaci na  leko na dubashi  .
“to jikinsa dai da sauki zamu ce Allah dai ya iya mana  da iyawarsa dan rayuwar Ibrahim na daf da fuskantar matsala da Kuma qalubalin rayuwa ya kasa jurewa rashin tanweer  “Allah  sarki ib yana qaunar  tanweer  kmr yadda yake qaunar rayuwarsa  inshallahu zata dawo har ma suyi aure  ta k’arasa maganar tana sake matso ruwan  hawaye sun dade suna tautauna wa akarshe  minister ya  kira  cp  yaji halin da’a ake ciki  ,byn  cp   ya d’auki Kiran  suka gaisa “wai ya ake ciki ne da batun yarinyata  shirun fa yayi yawa zuciyata ta fara tsinkewa Ina Jin kamar Allah ya d’auki raina  na huta ? na kasa jurewa rashin diyata da rashin kwanciyar hankalin matata “.naunayen ajiyar zuciya cp  ya sauke sannan ya fara magana a natse”mun baza mutanen mu  cikin   gari    yanzu haka mun  fara  samun improvement akan lamarin   “to alhamdulillah   Allah ya taimaka   yasa aga  yarinyata  cikin koshin lfy “karka damu inshallahu komai yazo karshe ka kara mana lokaci kad’an “na gode na gode ”  sukayi  sallama minister ya  fuskanci  hjy zainab tare da yi mata albashiri da abinda cp ya fad’a masa  nan take farinciki ya mamaye zuciyarta  shi kuwa alhj Tahir  cikinsa ne  ya duri ruwa gabansa ya  shiga  fad’uwa hankalinsa yayi kololuwar  tashi .
babu shiri yayi musu sallama   ya  shiga motarsa direbansa ya ja suka  kama hanyar zuwa gida ,yasan ya taro wa kanshi  match tunda yayi sanadin da’aka d’auke tanweer  wayarsa ya Ciro yanata  Kiran number jaguwa  ana ce masa akashe  take har ya k’araso gida bai samesa ba ,  ya rasa yadda zaiyi da rayuwarsa  yasan muddin  su jaguwa sukazo  hannu   kashinsa ya  bushe domin asirinsa ya tono .”

fitowa yayi da sauri daga cikin motar bai tsaya jiran direbansa ya fito ya bude masa ba  kmr zai tuntsura ya shiga cikin gidansa gumi na karyo masa ta koina a sansar jikinsa  kai tsaye bedroom dinsa ya shiga ya rage kayan jikinsa ya shiga zariya  yana neman mafuta , yana tsaye hjy baseera ta shigo tana binsa da kallon mamaki dan ta kwana biyu bata gansa cikin yanayi irin haka ba  “wai Lafiya ka shigo kamar wani kububuwa me km ya faru ? tsaki yaja   yace “babu  komai . “To daga Ina kake yanzu “?. daga  gidan minister nake ya bata amsa yana fifita da hannunsa dan wani irin  azababben zafi yake  ji ta koina    tana Jin  haka na gane komai   ta  kama  gabanta  zata fita ya d’auki remut din ac yana kokarin  qara karfinta tare da cewa  “ya kuma zaki wuce ki barni ga dan iska kin samu  kin tmbyeni na baki amsa kawai zaki juya ki kama gabanki  “oh to ni me  zanyi  maka ?”   zata sake magana ya d’aga mata hannu”jeki kawai bananason jin komai tunda babu abinda zakiyi shasha kawai  ya  fad’a a matukar fusace  yana juya mata baya.
tabe baki tayi a ranta tace  “ai Kai ne Sha Sha ,mutumin banza kawai  da bai san ciwon kanshi ba aurenka ko hasara duk a tunaninka ban San halin da kake ciki bane  byn na san komai  a juri zuwa rafi dai wata rana tulun zai fashe  juya tayi ta barshi tsaye  yaji da damuwarsa .ta nufi gurin  d’anta ta bashi maganin karfin jiki  dan ta sha alwashin bazata sake yarda da tsarin mijinta  ba   hk kawai  ta rasa tilon d’anta a banza, gbdy magungunan da yasa  nazifi ya rubuta masa an siyo sai dai bata bashi ya sha ba  wasu dabam ta bashi  jikin ne dai nashi yaki daidai saboda an rigada an karya masa garkuwar jiki ” .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button