KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48


“Wai  waye wannna jaguwa  din ne  ? waye km ?.gbdy sai da tanko gote ya kira sunayensu d’aya  bayan d’aya ka  amsa min tambayata boka ” ya san sunansu ne  a bakin wasu daga cikin mufukan’ yansanda da sukayi attacking  dinsu a wancan satin “. shiru bokansa    yayi  yana dube dube acikin kasa ,abubuwa   da yawa  ya gani akan jaguwa km abun ya balain tsoratar dashi dan har wani gumi ya had’a da  kyar yayi jarumtar yin magana “wannan  yaron da Jamar’sa  rikakkun  y’an fashi da makami ne  da suka ga gari kowa  acikin garin nan yana da karfin da zai iya karawa da kowa acikin garin nan ,haka yana da karfin da zai iya shiga duk Inda yaso yayi sata  batare da an dakatar dashi ba , yafi karfin kowa duk yadda kake tunanin yan fashi sun  zarta tunaninka basa ji basa gani akan aikinsu  sai dai abinda na gani a dubana  shi jaguwa  yana fanshinsa ne akan masu kudi da azzaluman kasar nan , yana da hatsarin fuskanta it’s not easy to be known as the CEO of armerobber’s association .
wannan ya wuce da tunaninka ranka shi dade karka bata lokacinka gurin sanin ko shi waye ko matakin d’auka  akanshi  tunda har ya barka da ranka da lafiyarka sai mu godewa Allah domin shifa satarsa me dalili ne Kuma ya dade acikin harkar Kuma shi kad’ai yasan abinda ya taka wanda yasa ya gagari kasa da kasa har da  jami’an tsaro suka kasa kamashi tanko gote ya numfasa kana yace “zan so yayi aiki a karkashina domin irinsa nake nema “bazai had’a Kai da Kai  ba dan baya zalinci burinsa ya taimakawa talakawa marasa  galihu Kai Kuma burinka ka danne hakin mutane da talakawa  “wai boka ya kake min  magana haka  ne ? ” kayi wani Abu da zai kawo kanshi gareni “babu abinda zan iyayi domin duba  taurarinsa ma kawai zai iya sa mutun cikin tashin hankali, kaima idan baka cire hannunka akansa ba zaka iya rasa komai naka jin abinda boka yace yasa tanko gote  shiga damuwa bai sake cewa komai ba ya kakkabe bababan rigarsa ya baro gurin boka da zumar zai nemi had’in kan jaguwa ta kowani hali “.   


Jaguwa na zaune  tare da abokinsa da yaransa a gurin  shakatawarsa   gabansu  kwalban giya ne yayinda kowannensu hannunsa ke rike da karan sigari har  jaguwa  suna tautaunawa akan sabon aikin da zasu fita zuwa garin  Ogun state sai ga me gadinsa ya rusuna ya gaishesa tare da cewa “ga wannan dattijon daya zo neman taimakonka   ya dawo ranka shi dade” “shi da nace ya dawo karshen sati  amman dai   shigo dashi kawai ”  mai  gadi ya juya da sauri jaguwa ya kashe sigarin hannunsa  dan yana matukar jin kunyar wani yaga yana shan sigari  eku tattara gurin nan  kafin azo da  dattijon nan take yabi umarninsa .ko cikakken minti biyar  ba’a yi  ba sai ga me gadi ya dawo  tare da mutumin da yaronsa wanda bai wuce shekara talatin ba  dattinjo na kokarin rusunawa 
jaguwa ya tsaidashi  yana nuna masa gurin zama “ka zauna baba  dattijon ya zauna a Inda ya nuna masa  yana rawar  jiki, gbdy su jubi suka gaishesa ya amsa yana Saka musu albarka “d’ana ga yarona  nazo dashi “jaguwa ya waigo ya  kalli Inda  yaron  yake  tsaye cikin wasu kod’ad’un kaya marasa fasali da sauri  matashin saurayin ya dan rusuna ya  gaishesa ya amsa da Kai tare da cewa ” ya sunanka sannan wani course ka karanta ? ” sunana aliyu Ahmed abinda na karanta lissafi wato  accounting .ya bashi amsa cike da girmama.
shiru jaguwa  yayi yana nazarin yaro kafin daga baya yace  “shikenan zaka zauna damu  ka zama dan aikenmu kafin  lokacin da zan  samo maka aiki inshallahu , dattijon najin haka ya fara hawaye yana godiya ” na gode na gode Allah yayi maka albarka “karka damu baba mu daman aikinmu kenan taimakawa marasa shi ,aiki kuwa ka fara hasasho  ganinsa cikin  jerin ma’akatan banking   kasar nan  yana gama fad’ar haka yasa aka dibo kudi masu yawa aka bawa dattijon “baba ga wannan   kudin kaje dashi kayi bukatunka dasu, sosai dattinjo ya zube yana godiya kafin daga baya yay sallama dasu ya wuce ya bar d’ansa .”


D’akin  taro ne dake cike da manyan  jami’an tsoro kowannensu  sanye da kankinsu  na aiki  police, yayinda  gabansu  ruwan roba ne mai sanyi   da abun   magana  a hankali cp ya fara magana cikin tsadaddan turancinsa “
Daga  ashirin da biyar ga watan daya na wannan  shekarar ta  2021 zuwa ga karshen shekarar shadaya  da muke ciki  an samu farmarki ta’addanci a qalla ashirin da biyar a cikin garin nan, duk  da k’okarin  da jami’an tsoro keyi akan suga sun kama wadan nan  yan fashi abun ya faskara wanda ni a nawa tunanin ina ganin akwai manyan kasan nan dake mara musu baya,  taya  zamu samu nasarar kama wannan  mutumin dake jagoransu wanda shi ke shirya komai  na ta’addanci   ? cp ya karasa maganar yana kallon hoton jaguwa dake ajiye akan makeken table din gabansa .” yanzu haka wannan shine tantiri na biyu da ake nema acikin kasar nan idan kuma acikin garin nan ne shine na daya , jaguwa  kenan   duk wani sata da’ake wa manyan kasar  nan da  yan siyasa da hannunsa aciki abun mamaki yadda wasu daga cikinmu suke bashi kariya ta hanyar sanar masa da halin da’ake aciki,  a offishin hukumar tsoro kuma suna yi masa duk wani alfarma daidai da wani mai fada aji a kasar  nan “.

shi din dan ta’addanci ne kuma dan fashi da makami ne Kuma gashi yanzu yayi garkuwa da diyar minister shi din mutun ne me tsananin kyautatawa jama’a da tsananin tsoro allah da tausayi  duk inda akace taimako zai bada yana da tsananin tausayin marasa shi sannan baya son zalinci yana daukarwa wadan da aka zalinta fansa idan gwanati taki yin komai, sai dai duk da hakan shi din babban me laifi ne agurin hukumar kasar nan   yana zaune a unguwar magodo  no 20  duk da ba nan kadai bane maboyarsa yana da gidaje dabam dabam   , wadan  nan  bayanai  da inda zaa samesu  duka gasu nan a rubuce  IPO investigation police officer  ne ya rubutosu “. taya zamu samu nasarar kamasu ?  ya  karasa maganar yana daukar file din gabansa  ya tsura masa ido  .”

Cp na yin shiru mataimakinsa  ya  fara magana a natse batare daya tashi ba  ” wannan  duk me sauki  ne sir  tunda  a halin yanzu maikacinmu  ya Dade da shiga  jikinsa  dan haka duk halin da suke  ciki  zai zo mana cikin sauki,  kaga kamasu bazai mana wahala ba duk wuya duk runtse sai mun ga bayansa domin bazamu marawa taaddancin da suke ma kasar nan baya ba, zamu bukaci  ganin an kamashi cikin kankanin lokaci ya karasa maganar yana duban  wanda ya turawa   jaguwa jami’in sirri   “dcp   baba abare  wanda aka kira da haka yace “yes sir ” ka tabbatar kasa ya   shiga jikinsa  sosai ta yadda  zaa  tattara duk wani mahimman bayanai akansa ya gabatar mana dasu da wuri  “yes sir kace masa ya  kiyaye da kyau  domin shi din mutun ne  mai hatsari sosai “inshallahu sir zanyi kokarin kuma zamuyi nasara kamar sauran lokutan baya a hankali suka cigaba da tautaunawa akan yadda zasu samu nasarar kama jaguwa da yaransa daga karshe cp ya sallamesu,  kowanne  ya kama gabansa.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button