KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Suna zaune sai ga zahra ta shigo cikin doguwar riga marun colour tana karairaya tana gama tsayuwa a tsakiyar falon onexpecting taji jaguwa ya mike ya ɗauketa da wani gigitacen mari da sauri ta dafe daidai Inda ya mareta tana dubansa “ki fita rayuwata Zahra , ki tsaya matsayinki” zahra tace “me yayi zafi haka Adnan ? “dazu anas ya kirani yake fad’a min abinda kake zargina akai amman ka sani ……
“wani marin ya K’ara kifa mata sai data ga taurari masu duhu “amman kasan me din ubanki ?”me zaki fad’a min na yarda dake maci Amana kawai, daga karunwaci kin koma bin bokaye saboda ke katuwar jahila ce wannan ya zamo Karonki na farko ya Kuma zamo na karshe babu ruwanki da yarinyar nan wallahi muddin wani abu ya sameta sai na kasheki da hannuna , wai ma meye hadinki daita? ni kike wa kwakwa ni Kuma nace banayi ko dole ne sai na aureki ?ya tambayeta yana sake tsare girar kasa da sama. “duk ta rud’e sai wani gumi take fitarwa cike da matsanacin firgici tace “ka yarda wallahi babu hannuna ci…ciki ” ta k’arasa maganar tana in Ina gani yadda yake mata mugun kallo yasa ta soma neman hanyar guduwa dan kallon fuskarsa kad’ai ya Isa ya tsorota mutu da sa mutun ya shiga hankalinsa sam sam babu alamun wasa atare dashi kafa yasa mata sai gata ta zube kasa bisa gwiwowinta tana kallonsa cikin muryar kuka tace “ni kad’ai kake bi bare kayi tunanin nice na aikata abinda kake zargina? Ina Jin tsoron Allah Adnan bazan iya ……”shiiiiiiiii ! banason Jin komai d’aga bakin makira irinki .”
“Zahra!
ya kira sunanta muryarsa a tsarke ta zuba masa Ido tana amsawa da” Na’am “babu tsoron Allah”n daya halicceki acikin zuciyarki dan hk nasan zaki iya aikata komai akan cikar burinki ,masu kyakkyawan zuciya da tsoron Allah su suke tsoron aikata mugunta ke Kuma baki da ko daya aciki “yayi shiru yana numfasawa sannan ya cigaba da mgn “daga yau idan kika sake shiga harkata zan mugun baki mamaki kuma dan Allah karki cire hannunki akaina da duk wacce zaki ganni idan Kuma kinki yiwa kanki kiyamul lail zaki hadu da cuuttuka ,sannan zan ganar dake da yaren da zaki gane yana kaiwa nan yace ” ki tashi ki bani guri bana son ganin wannnan fuskar taki “.
“naji zan tafi amman kayi hakuri kayi bincike sosai akai muddin aka tabbatar maka Ina d’aya daga cikin wad’an da suka aikata wannan laifin ka min hukuncin da yafi wannan “wani bincike zanyi bayan nasan babu me shegen naci a rayuwata kamarki ?ya matsota sosai ya cafki makoshinta idanunta suka yo waje “ki fad’a min gsky kece kikayi mata asiri ?ta shiga girgiza Kai alamun a’a “bazaki fad’a gsky ba ? girgiza masa Kai ta sake yi anas ya taso ya rikesa karka yi kisan Kai Adnan “ka rabu daita karka kashe yar mutane “kace mata ta fad’a min gsky da bakinta
“me yasa tayi wa yarinyar mutane asirin data kawo min kanta gareni na aikata abinda ban yi ra’ayi ba? ya fad’a yana filinging daita sauran kad’an kanta ya bugi bango anas yayi saurin riketa yana bawa jaguwa hakuri .wani sanyayyayen numfashi Zahra ta sauke da kyar tana jin dadi aranta burinta ya cika tunda ya kusanceta rabuwarsu tazo duk nacinsa dole su rabu ,abokansa kuwa da Ido suka bisa suna mamakin jin furuncinsa ,me yasa kika yiwa yarinyar mutane asirin da ta kawo min kanta gareni na aikata abinda ban yi ra’ayi ba? suka tambayi zukansu suna dubansa fuskokinsu d’auke da qarin bayani .
“Anas kaji abinda yake fad’a , dan jarabansa ya ciyosa ya kwana da yarinyar mutane shine zai d’aura laifina akaina , kasani babu hannuna acikin wannan aika aikan ” ,jaguwa juya mata baya ya tsuke fuska alamun bai son jin komai daga bakinta muryarsa a tsawace yace “anas ka sallameta daman Kaine kake gayyatota zuwa gidan nan ” da sauri anas ya riko hannunta ya nufi kofar fita daita “anas ka sakeni na fahimtar dashi gaskiya “bazai ta’ba fahimtarki ba kije kawai dan Allah nima daga yau karki sake kirana na yanke muamula dake bazan Kara kiranki ba banason na samu matsala da abokina, aminina ,farincikin rayuwata .
fixge hannunta tayi daga cikin nashi adaidai lokacin da suka fito zuwa haraban gidan ta tsaya a hassale tana dubansa “ka dade baka daina kirana ba ,bazan kiraka ba shima bazan kirasa ba Amman na rantse sai Adnan ya dawo ya nemeni da kansa ka rubuta ka ajiye a Inda bazai goge ba …”
Mmn sudais????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686
alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
????️16
“Kenan da gaske kin aikata abinda yake zarginki akan shi ?” idanunta da suka rikid’e sukayi jazur ta cigaba da kallon anas wanda yake tsaye a gabanta yana huci kamar zaki dasu “eh na aikata Kuma bazan tsaya iya nan ba ta fad’a a matukar fusace ” zan d’aura daga Inda na fara , zan tabbatar da na azabtar da yarinyar nan da azaba mafi muni , ba dai duk akanta ya mareni ba?” ya mareni akanta anas , ya ci mutuncina akanta ya wulakantani a rita lori akanta ,wallahi ya kwana da sanin zan fanshe duk abinda yayi min akanta ‘zan mata azaban da rad’ad’insa yafi zafin dalma , zan rikirkita mata rayuwa zan…..”saurin dakatar da ita yayi ta hanyar buga mata wata razananniyar tsawa yana cewa “enough !
“karki fara zahra dan bazaki ci riba ba , wad’an da ma suka fiki sunyi sun hakura sun barshi dan ba zasu iya ja dashi ba domin shi din dokin tsere ne bazaki iya karawa dashi ba ,shi guguwa ne idan ya tashi zai tashi da rayuwarki , zai juya rayuwarki daga sama zuwa kasa ki rasa gane kanki ……”ya k’arasa maganar yana nuna da yatsansa .
“Zahra !
Ya kira sunanta cikin tsananin ‘bacin rai ” ki tsaya daga Inda kike idan ba haka ba ki shiryawa gudun tsere da mutuwarki , dan akan ki ta’ba wannan yarinyar gara kin rungumi mutuwa da hannuwanki.” Adnan yace bai sonki ya nuna azahirin bai sonki, tunda ba tare aka halliceki da soyayyarsa ba ya kamata ki hakura ki rabu dashi ki tsira da rayuwarki dan akan yarinyar nan ba zai raga miki ba zai iya destroyed din rayuwarki, ki manta da kin ta’ba muamula da Adnan a rayuwarki “. wannan shine abinda zan fad’a miki idan Kinga dama ki d’auka ki cire hannunki akan mugun nufinki ki zauna lafiya idan kinga dama ki cigaba kece zaki kare rayuwarki a nadama “.