KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Tunda  ya soma magana zuciyarta  ke bugu  very  fast ta kafe shi da   idanunta   ta cigaba da kallonsa  ,a yau gbdy babu  sauran  burbushin tausayin  data  saba hangowa  acikin kwayar idanunshi  a duk lokacin da hargitse ya shiga tsakaninta  da adnan , yau  ce  rana ta farko da anas yayi  hannun riga daita . ka’fafunta ne suka  kasa d’aukarta ta durkushe kasa  bisa gwiwowinta tana  wani irin kuka tana cewa “kasan  kuwa  yadda nake ji a zuciyata ? “maganganunka suna huda min    zuciya, me yasa  zaka    nisantani  da  Adnan  ? ya kalleta cike  da  matsanacin  bakinciki  dan gbdy ya  fuskanci  bata  da niyyar saduda  shi kuma  a yau gbdy  babu  wannan tausayin da yake ji nata,  da tayi  silar rabashi da masoyinsa  da yafi qauna akan  komai a rayuwarsa gara ya  yakiceta  ta  karfin tsiya  sunyi  hannun riga  daita “amman kai kana ganin zan iya rabuwa da Adnan dan yace bai sona  ?ko kana tunanin zan iya daina sonshi  ne ? Me yasa zaka ce na manta da soyayyata ?  “haba anas  idan kayi min haka baka kyauta min ba ,yanzu adalci ne  daka nuna  kafi   bukatar  rabuwarmu dashi   ?
ya gyada mata Kai alamar”eh! ” cikin firgici da tashin hankali ta shiga girgiza masa kanta  sannan ta cigaba da magana “ada tunanina kana sona da Adnan ne  a she duk ba haka bane karya ne baka qaunata dashi  ? to bari kaji  in fad’a maka maganganunka  ba zai sa  na  fasa duk abinda nayi niyyar aiwatarwa  ba  ko da kuwa zan mutu  .” ta  k’arasa  maganar tana sheshekar  kuka  “karki fasa  zahra bazan baki  hakuri  ba  kije kiyi  duk  abinda zakiyi amman Ina tabbatar miki wahalar banza   zakiyi dan ba zaki yi nasara ba hasarar  kudinki  da lokacinki  kawai zakiyi yana gama fad’ar haka yace ki  tashi ki  ‘bace min da gani yadda Adnan baya son ganinki  nima hakan take gareni  “.

Batace  masa   komai ba ta  mike da  kyar ka’fafunta na rawa  ta juya  ta soma tafiya  hawaye masu zafi  da ciwo   na sake   zubo mata akan  quncinta , zuciyarta bata ta’ba karaya ba atun sanda  jaguwa yake  furta mata kalma bai sonta sai a yau da anas ya sake maimaita mata  , duk da ba yau ta saba jin kalmar baya  sonta daga bakinsa  ba amman ciwon na yau daban ne a cikin zuciyarta sannan  ya mugu  mugun  tsaya mata  arai   ya d’aga mata hankali ya dagula mata lissafin tsarin rayuwarta   data shirya  dashi , Kuma duk runtsi  duk wuya sai tayi abinda zai furta mata  Kalmar so  da bakinsa , sai ya dawo  yayi  kuka da idanunshi yana rokon ta amshi  soyayyarsa,  ko zatayi yawo tsirara sai ta aureshi idan Kuma   hakan bai samu  ba   zata  saka rayuwarsa  ta quntata  . “

anas  ya  yabi bayanta da kallon bakinciki  ,ya rasa wani irin  naci ne  irin nata , mutun ya nuna miki  da Ido  ya nuna miki  da jikinsa  har ya fito ya furta miki amman ki tsaya kina hauka akanshi,  tsaki yaja ya juya ya  shiga ciki falon zuciyarsa cike da takaicin abinda zahra tayi  . Inda ya bar jaguwa anan ya  iskeshi   tsaye   a tsakiyar  falon   rungume  da duka hannuwansa a qirji  sai  faman cika yake  yana   batsewa .
jikin  anas a sanyaye  ya   samu guri   ya tsaya kusa dashi   ya  dafa  kafad’arsa,  jaguwa  ya  juyo  ya   kalleshi  yana cije lip’s dinsa  na  kasa a hankali ya sake juya masa  baya    yana  furzar  numfashi   kana yace  “ka   gama  munafurcin ?wani irin bugu qirjin anas yayi da karfi  ” a hankali  sautin  muryarsa  ya fito yana cewa”idan  zanyi  munafurcin  kowa  bazanyi  naka ba,  idan zan cuci kowa bazan  cuceka ba, kama  daina  min irin wad’an nan  abubuwan dan wallahi  suna  Kona min rai da  mugun   tayar  min da hankali “.
Jaguwa ya waigo  ya fuskanci anas sosai  yana  sake furzar da iska  mai zafi  daga bakinsa “muddin  kana son zuciyata  ta cigaba da amincewa da Kai    sannan  na daina fad’ar  haka akanka  anas  ya zama dole sai kayi hannun riga da zahra bana qaunarta bana qaunar ganinku tare muddin zaka kasance dani sai dai ka za’ba ko ni  ko ita ?  taku daya biyu yayi ya matsa daga  kusa da anas  yana tafiya a hankali  still yana rungume da hannunwansa.

“jaguwa !

anas ya kira sunanshi cikin yanayi na firgici  da tashin hankali , idanu kawai jaguwa  ya tsura masa  batare daya amsa masa  ba”  shakka babu duk duniya nafi sonka akan kowa, Ina qaunarka fiyye da ni  kaina  maganar zabi  ma  bata  taso  ba dan kasan waye  zabina”  yayi mgnr hawaye na ciccikowa a idanunshi  “Kai ne zabina Adnan  Ina  sonka fiyye da kowa da komai  nawa ”  tautausan murmushi  jaguwa ya  sakar  masa yana mai Jin sanyi  acikin  zuciyarsa , cike da  farinciki  ya mika masa hannunsa
da sauri anas ya mika masa nasa  hannun suka  rungume juna suna sakin numfashi   atare ,  jabir , jubi  ,kamil  da suke  zaune  duk sukayi  shiru suna dubansu  dan  ba wannan   bane karon    na   farko  da suke samun matsala  a tsakaninsu  kuma  cikin kankanin lokaci suke  daidaita kansu. 
kuka sosai anas yake  jaguwa na shafa bayansa kamar wani karamin yaro  “is okay  anas  na sani , nasan kana  qaunata  da gsky kmr yadda nake qaunarka   am really sorry for  my active  har  cikin  zuciyata nake jin  qaunarka , Kai  zinari ne acikin zuciyata  Ina sonka anas  “Nima Ina sonka  kyakkyawan abokina had’e da qauna  mai  karfi , cikin  kankanin  lokaci   komai  ya daidaita  a tsakaninsu  suka  samu guri suka zauna cikin sauran abokansa  nan hira  ta barke a tsakaninsu .
su jubi sun so kwarai su sake samun qarin haske akan maganar  jaguwa ta d’azu  akan yarinyar  amman    yaki bada dama   amman duk da haka sai da kamil yayi magana Cike da kulawa kamil yace “anyi maka tambaya  akan yarinyar nan  ka wani  share  mutane ” to  me  yasa meka a goshi  Kuma ?  ko baku  lura da goshinsa  ba  ?ya fad’a yana kallonsu  d’aya byn daya  ,kun san halin miskilancinsa  ai  ba lallai ya fad’a ba ni tun jiya  na gani sanin halinsa yasa na share  inji cewar jubi .
“ku manta da wannan maganar idan akwai wacce ta fita  mahimmam ku kawo  muyi  kawai  ” anas ya  fad’a  dan  jaguwa wayarsa ya d’auka yana duba sakonin mutane , basu  tashi a falon  ba sai da suka tsara yadda  tafiyarsu  Ogun state zata  kasance a gobe  .
” Yadda  suke  tsara  komai akan aikinsu   haka  Suma  jami’an tsaro dana  sirri  suke shirya yadda zasu  kamasu  a yanzu ma  Asst  Commissioner   of  police ne ya kira layin  d .c .p   baba abare  wato  lawan  numan   byn  ya  d’auka suka gaisa   ya fara magana  cikin   zafin rai ” wannan mutumin  bai  kamata a  barshi har zuwa  wannan  lokacin  batare da anka  mashi  ba , yayi mgn tare da yin shiru  “eh  to haka ne  amman  abinda nafi  bukata a Kara saka Ido sosai  akan  duk  wani  motsinsa  da shiga da fitarsa  bama  iya rayuwarsa ta fashi ba  hatta rayuwarsa ta duniya ma sai na tabbatar  da ta ru’bance idan yazo hannu , sun  dauki  lokaci  mai tsawo  suna tautaunawa akan jaguwa da  yaransa  kafin daga bisani suka yi sallama.  “

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button