KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Bai jima da kwanciya ba aka  soma  knocking kofar  falonsa , yana  daga kwance ya bawa mai yin knocking ɗin izinin shigowa eku  ne ya shigo cikin falon hanunsa  riƙe da farar leda, cike da girmamawa ya rusunawa  ogan nasa a natse Jaguwa ya mike zaune ya zura silifas ya amsa  ledar    yana masa  godiya  eku  ya juya ya  fice daga  falon.mikewa tsaye  yayi ya  fito ya shiga   ɗakin  tan batare da yayi knocking ba  kamar yadda  ya saba  koda yaushe zai shiga Kai tsaye ne , sai kawai ya tura  ƙofar  ya shiga ciki, tun sanda ya kawota  gidan yake jin   haushi Kansa da bautan da yake mata  amman a yau din jin zuciyarsa yake fessss  akanta zai iya mata komai ciki kuwa har da zama bawanta .
Tana kwance akan gado ta  kwanta  ruf da ciki, bacci ta keyi har lokacin  hankalinta a kwance,  murmushin gefen baki yayi   kamar tana ganinsa  haɗe da aje ledar  hannunsa” sarkin rigima da rashin kunya  ya fad’a a ransa , har ya juya zai fita daga ɗakin kuma sai ya tsaya yana  kallonta   tun daga yatsun kafaunta har zuwa  kanta komai nata abun burgewa ne ,   ahankali ya taka zuwa inda take kwance,  tafin kafansa d’aya  yasa ya ɗan  shafa  tsakiyar kafarta .
azabure ta farka ta zauna tana murza   idanunta dan  har lokacin Jan da sukayi  bai baje  ba , sake kallonta  yayi, “Ki tashi kije kiyi wanka kiyi alwala kiyi  sallah , ke fa na lura sallah bata dameki ba  dan  zaki iya  wuni  bakiyi sallah ba  ki kuma kwana bakya damuwa”  yayi mgnr yana mai  tsareta da sexy eye’s dinsa.”

Tsura masa idanunta tayi tana kallonsa  tana Jin haushin abinda yake mata sai ya fad’awa  mutun mgn yayi kmr bashi  yayi maganar ba, saboda yanda yake fizgo mgnr da kyar Kallon agogon d’akin tayi yanzu ne ma hud’u   ta wuce muryarta a raunane tace “gara ni ko banyi sallahr akan lokaci ba zan rama Kai fa ?meye amfanin sallahrka akan lokacin tunda kana aikata aikin  haram, wad’amuhu haramun ,washarabahu haramun wa guziya bil haramun wa’anna …..”ki min shiru anan  stupid  ” ya fad’a a tsawace , ana tausayinki bakya tausayawa kanki “nace ka tausaya min ne? ko nace ka cigaba da rikeni dole ? Ko  nace dole sai ka zau…..”Idan kin   sake furta wata kalma  anan sai na tattakaki idan km  kin mutsa bismillah  kiyi  ”  yana gama faɗan haka ya fice daga cikin ɗakin ransa a bace, gsky yayi mugun  sakewa yarinyar dayawa shiyasa ta rainashi .

Saukowa tayi ta shiga bayi tai alwala ta fito tayi sallah  tana idarwa ta mike ta Isa gaban mirrow  ledan da ya aje mata ta ɗauka haɗe da buɗewa, robobin take away ne acikin  har guda  uku,  ɗaukan ɗaya tayi haɗe da buɗewa ta soma ci, kad’an taci dan zazzzabi take ji sosai bata jin dadin  bakinta   ta sha ruwa kad’an  .
 kamar ta koma ta kwanta   ta tsinci kanta da fitowa, kanta babu dankwali  ta fito zuwa falo da kyar take taka ka’fafunta , yana tsaye agaban tv  ya bawa cikin falon baya yana ƙoƙarin danna code din bude wayarsa ,  jin motsin mutun  a falon yasa  batare da ya juyoba yace.   “waye ? “Waye byn wacce ka sato ka ajiye a gidanka  ita ce ta fito  ta sha iska tayi mgnr da kyar tana kokarin zama akan kujera “shekaru sun ja wallahi ya kamata ka tuba ka daina harkar fashi ,nasan da mahaifiyarka tasan wannan aikin kake yi da bata yi alfahari da Kai ba a karshe  kashe kanta zatayi dan bakinciki  .”

A matukar fusace ya nufo Inda take  tamkar wani mayunwanci zaki ya damki wuyanta yana Shirin danne makoshinta ya fasa saboda zafin daya ratsa tafin hannunsa ya tsura mata Ido kawai yana kallonta  “ka shaki ne mana ai ni yanzu a shirye nake da mutuwa gara min mutuwa akan cigaba da zama da Kai ,a farkon had’uwa ta da Kai naji duk duniya Kai  mutumin kirki ne  ,Kai ne  mutumin da zuciya da gangar jikina suka mace akansa saboda a  tunanin zuciyarka me kyau ce a she ba haka bane mugun  ciwo ne daskare  a zuciyarka wannan mummunar sana’artaka yafi min komai zafi acikin zuciyata wanda adalilin haka  yanzu  babu kyakkyawan zaton da soyayyarka   acikin zuciyata  sai zallar tsana  ,na tsaneka tsanar da zan iya ganin bayanka ka rubuta ka ajiye muddin na bar gidan  nan sai nasa  ka shiga ha…….”

“karya ne ” ya fad’a  a tsawace yana  nuna ta da yatsansa  “karya ne baki Isa ba , baki Isa kisa akamani ba how could you tell someone  tanweer ?”  you can’t  do that , bazaki iya ba  sannan  jaguwa ba zai kamu ba cikin sauki ba  sai dai wani mutun dabam,  da zan kamu da ban Kai iyanzu ba” yayi mgnr yana furza mata iska a fuskarta  tayi saurin runtse idanunta gabanta na faduwa , ya juya mata baya tare da rike kugunsa da hannu d’aya ya fara zagaye falon zuciyarsa na tafarfasa can ya juyo a matukar fusace  “and     kikace me  byn zaki sa na shiga hannu ?” Kin tsaneni  tsanar da zaki iya ganin bayana Shima karya ne   zuciyarki  bazata  iya rabuwa da soyayyata ba  yadda  kika furta cewar kina sona haka zaki tabbata da sona  a karshe ciwon sona ne zai kasheki  saboda Ina ranki ,na  shigeki shigar  da bazaki iya cireni a ranki  ba ,zaki je gidan wani da tarin soyayyata gangar jikinki za’a Kai gidan wani zuciyarki kuwa tana nan  …..”ya nuna qirjinta daidai saitin zuciyarta .

wani  irin  sarawa kanta ya dinga yi da  karfi  kmr zai ra’be gida biyu  tayi matukar firgita da  Jin mgnr shi , ta d’auka zai tsorata da maganarta  sai dai taga sa’banin haka atattare dashi sam shi din ba matsoraci bane zuciyarsa  a dake take ,kallonsa tayi tare da ciza lips dinta  batare data sake yunkurin cewa komai ba “ki tashi ki ‘bace min da gani  banason ganin wannan banzar   fuskarki, karki qara kuskuren zuwa  Inda nake sannan   duk abinda kikaga  Ina yi miki karki d’auka so ne , ba so bane tanweer  dan ko digo d’aya na sonki babu shi acikin  zuciyata  bakya cikin  irin tsarin matan da zan  so , idan Kuma kin koma gaban iyayenki  dan  Allah karki fasa idar da nufinki  akaina  kiyi  Ina jiranki  wani irin zafi da ciwo kai ne me karfi   yayi mata diran makiya gbdy  jikinta ya sake d’aukar zafi tayi karfin halin dafe kanta cike da sanyi jiki ta mike  ta nufi hanyar komawa d’aki  sai da tayi da tasanin fitowarta .”

da kyar ta  dinga d’aga ka’fafunta da
idanu ya bi  bayanta  yana kallonta  rai a ‘bace  har ta bace wa  ganinsa sannan ya d’auke idanunshi  yana   fesar da iska zuciyarsa ban da zafi babu abinda  take sai  faman  tsaki yake ja da karfi  ya fad’a kan kujera  ya runtse idanunshi tare dafe goshinsa cikin haka abokansa suka shigo suka samu guri suka zauna   ganinsa haka yasa  suka fara tmbyrsa abinda ke damunsa shiru yayi yaki cewa komai  sai tsaki yake ja anas ya dafa kafadarsa “meye damuwarka  Kuma ? Still shiru yayi yana ciza lip’s dinsa jabir da jubi suka tashi suka fita  dan sun San  tunda yayi haka ba magana zai yi ba “ya kamata ka rage  damuwar nan  jaguwa nasan duk damuwarka  bata wuce akan yarinyar nan ba “Ina matukar tausayin yarinyar nan  anas amman ita  burinta bai wuce taga bayana ba
yayi mgnr a fusace idanunshi sun yi jajur “kayi hakuri nasan da haka nasan kana tausayinta da qau….” wani irin   kallo yayi masa wanda yasa anas ya hadiye abinda zai fad’a “na sha fad’a maka ka daina cewa Ina son yarinyar nan amman tunda haka kake tunani ka zuba Ido zan baka mamaki”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button