KUSKUREN BAYA 1 TO 48

gudu motocinsu suke sosai akan titi tare da jiniya ,kowacce mota ta gansu sai ta kauce ta basu hanya ,irin gudun da sukayi yasa cikin kankanin lokaci suka k’araso 1829 suka faka motocinsu suka firfito cikin sauri wasu suka nufi babban get din plaza din , yayinda wasu suka tsaya abakin kofar motocinsu rike da bindugu suna mazurai kamar wasu zakuna ,mutane kuwa tuni suka fara bawa kafarsu iska kar tsautsayi ya rutsa dasu .
a hankali police suka kusa cikin plaza din ,bincike suka fara yi kafin daga baya suka bukaci ganawa da manager gurin , Kai tsaye aka Kai su Inda yake , tun kafin su fito da Id card dinsu ya fahimce su din su waye , nan take ya rikice yana kallonsu .Jimi’an tsaro ne suka nuna masa I’d card “akwai wani mai laifi daya shigo plaza dina a mintunan da suka gabanta ko zamu iya ganin cctv camera dinku ?muryarsa na rawa yace babu matsala yalla’bai ya juya ya soma lalu’bo daukar yau dan Daman a qunne yake , a hankali suke kallo har ya kawo zuwa sanda suka shigo babu wanda ya shigo me irin fuskar da suke nema tare da yarinyar dan haka suka juya cikin sauri suka shishiga motocinsu suka nufi wani branch din dake ikotun .”
Jaguwa na isowa gida yayi parking yana ƙoƙarin bud’e mota domin ya fito da sauri tanweer ta rike shi gam ajikinta “dan Allah kada ka sake shigar dani cikin gidan nan “ya waigo a natse sai dai a fusace yake kallota sai daya d’auki second biyar yana kallon sannan yace “wai meke damun tunaninki ne ?”me ya samu gidan nan da kike son barinsa bayan rayuwarki ake k’okarin karewa ?
Tayi shiru tana kallonsa da nazarin maganarsa kullum maganarsa kenan rayuwarta yake son karewa “ka fad’a min waye wanda yake son d’aukar rayuwata da har kake k’okarin karewa ? tayi masa tambayar jikinta na rawa tare da sheshekan kuka.”ganin yadda ta rikice yasa ya kamo hannunta ya rike cikin nashi gam suna jin dumin juna “ki natsu zan fad’a miki amman ba yanzu ba “ni dai ka fad’a min ko waye shine samun kwanciyar hankalina da samun natsuwar zuciyata, Idan ma
ta kama zan hakura da gidanmu na cigaba da zama da Kai ,”ko Kuma ka siyo min sabon layi ka had’a min waya sannan ka fad’a min ko waye sai na fad’awa mahaifina a d’auki mataki akansa , wallahi nayi maka alkwarin bazan fad’awa kowa ba .”
Yayi d’an murmushin gefen baki wanda ya bayyana ainihin sirrin kyawun da Allah yayi masa “Ina ce kince zaki tona min asiri byn kin bar gidan nan ? “tayi saurin girgiza masa Kai alamun a’a “bazan yi ba na maka wannan alkwarin duk runtsi duk wuya bazan aikata hakan gareka ba muddin ka fad’a min “.
“kada ki damu idan kin shirya fad’awa duniya kiyi karki fasa , idan kin koma gida ki tara gbdy ‘yan jaridan garin nan ki sheida musu cewar Adnan dan fashi ne abinda nayi Imani dashi Allah bazai basu nasara akaina ba , mahaifiyata tana tsaye a kaina da adduointa haka mutane da dama suna min addua , duk da Ina aikata zunubai Allah zai tsareni daga sharrin duk wani jami’n tsaron albarkancin adduar mahaifiya data mutanen kirki .”
shiru tayi tana kallonsa hawaye na gangaro mata cike da sanyin jiki ta zare hannuwanta dake cikin nasa ta soma k’okarin zare jikinta daga garesa ,yana kallonta tayi baya da kujeran da take zaune ta maida jikinta ta kwanta tana mai runtse idanunta , yatsun hannunta ya kamo bai san yadda akayi ba ya tura cikin bakinsa ya fara tsotsa , wani iri ta dinga ji a sansar jikinta kmr ana zarar ranta , tayi k’okari cirewa ya rike yatsun da karfi yana cigaba da tsotsa kamar ya samu sweet sai daya tsotsa son ranshi sannan ya cire bakinsa ya ciro hanky ya goge mata hancinta dake digar jini yana cewa “ki kwantar da hankalinki zan fad’a miki ko waye amman ba yau ba “. yana gama fad’ar haka ya sakar mata hannu ya bud’e murfin motar ya fito ya zagayo bangarenta da take ya bud’e mata ta fito jiki a sanyaye, ya d’auki ledar maganin da aka basu ta dubeshi fuska da hawaye .
bai tsaya bi ta kanta ba ya riko hannunta ta turje alamun bazata ba ya juyo ya watsa mata idanunshi fuskarsa a d’aure “karki min taurin kai ” ya fada tare da sake juyawa suka shiga cikin gidan bakinsa d’auke da addua (bismillahi walajna
wa bismillahi kharajna wa’allahi rabana tawakkalna ) tana jinjinawa girman iliminsa, gashi tantiri gashi malami ta fad’a acikin ranta .
Kai tsaye d’akinta ya shiga daita ya kamota ya zaunar daita abakin gado ya janyo kujerar madubi ya zauna yana bin d’akin da Kallo duk ta hargitsa d’akin ko d’azu daya shigo yaso yayi magana yanayinta yasa ya share ya girgiza Kansa sannan ya fuskanceta ,baya jin dadin yadda take d’aga hankalinta akan gida ,
shi bashi da niyyar cutar daita , ko abinda ya faru daren shekaranjiya ma ba yin Kansa bane itace sila , tillastawarta ce ta janyo hakan ta faru ban cin haka babu abinda zai kai shi aikata zina daita.
“tan …!
Ya kira sunanta cikin kasalalliyar muryarsa yana sake kamo hannunta tare da kafeta da tsumammun idanunshi masu kashe mata sansar jiki , d’ago idanunta tayi ta zuba masa tana sauraronsa tare da jin wani iri a sansar jikinta duk sanda zata kalleshi sai taji wannan yanayi wanda babu tantama na qunar da take masa ne . “wanda ya tura mu fashi gidanku bashi da hannun cikin zamanki tare damu , rikeki da nayi Kuma nayi amfani da maganar da mukayi dashi a karshen maganarmu cewa “yayi yana da wasu target akanki a dawo dake ya aiwatar da nufinsa wannan shine dalilin da yasa na rikeki ba dan raina na so ba “.