KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

“Dan  ranka  na so dai ka rikeni  idan ba haka ba meye aciki  ? tayi maganar a  matukar fusace  ” ka mayar dani  Inda ka d’auko  ko ka fad’i  wanda ya turaku  gidanmu  kawai  a wuce gurin , ya runtse idanunshi  yana nazari wasu  abubuwa akanta .
ta dubeshi  idanunta cike da ruwan  hawaye “adnan ka d’auke ni a daren nan  ka mayardani  gidanmu   dukkanin  alamun  sun nuna min  iyayena na cikin tsananin damuwar rashina da…. ….”
“na  sani Kuma zan mayar dake amman ba yau ba ki bani lokaci wallahi zan mayar dake akwai binciken da nake da  zarar  na gama zamammu  tare  zai zama  tarihi  “.
ta  matso kusa dashi sosai har gwiwowinsu na gogan juna “naji amman dan Allah ka sanar dani Wanda ya tura ku gidanmu  fashi ?ya girgiza mata Kai  sannan yace “idan ma kika ji ko waye ba lallai ki yarda ba, Killa Kuma  ma kiji kin tsanani kanki  sannan tabbas wasu rigingimu zasu  faru  saboda kusancin dake tsakanin mahaifinki da wanda ya bamu  aikin .” ta kamo hannunsa  ta rike gam cikin wani yanayi “cikin   dangin dad dina ne  ko na mum dina ke son ganin bayan iyayena  da ni kaina ? ya girgiza mata Kai alamun “a’a”to sanar dani dan Allah zan barwa cikina bazan ta’ba fad’awa  kowa ba  “.

Shiru yayi yana nazari akan  lamarin ya fad’a mata ne ko ya shareta “abinda yasani  tabbas  idan batun
ya fito ya sa’bawa dokarsu domin a aikinsu babu wannan tsarin ,duk  runtsi duk wuya ba’a tonawa juna asiri tunda tun farko da wajewa ake tsara komai ba’a juyawa juna baya.
ta katse masa tunani ta hanyar cewa  “kana  ganin zan iya tona maka asiri ne ?”  Allah na  dai fad’a ne amman  bazan iya aikata hakan  ba. “na sani  dan  fad’awa soyayya  ba  abu  ne me sauki  ba  da  har   zaki tona asirin masoyinki I know  you  can’t  do that to me tanweer    bazaki  iya fad’ar  komai akaina ba   saboda qaunar da  kike min.”

ta lumshe tsumammun idanunta na second biyu tare da jan tsaki acikin zuciyarta dan muddin tayi a fili balai zai mata a hankali   ta bud’e idanunta  akan kyakkyawar  fuskarsa  “ba  wannan story din   na  tambayeka ba ,ka ajiye  batun wani soyayya dan a yanzu  babu ita acikin  raina buqatata   ka min bayani wanda yasakaka aikin  bana son jan  aji  da salo  tayi  mgnr tana murgud’a masa  k’aramin bakinta .yayi  murmushin gefen baki yace “to  da gaske zaki rufa min asiri agurin iyayenki ? da sauri tace “me zai hana in bukatar hakan  ya  taso ?”
“sannan  Ina fatan zaki fahimceni  ?” ta gyada masa  alamun zata fahimcesa, shiru tayi tana jiran ya faiyace mata  Komai  kawai taga ya zare hannunsa ya mike tsaye tare da zura hannuwansa duka cikin aljihunsa , a hankali ya juya mata baya yayi taku zuwa  daf da kofar  bayinta  ya tsaya tare da waigowa yace “ni zaki yaudara  ko ? ta girgiza masa Kai alamun “a’a  “karya  kike  tanweer yaudarata  zakiyi  dan  zuciyata  bata yarda dake ba   duk  da d’arurar soyayyata dake cikin kwayar idanunki da zuciyarki   kina son na fad’a  miki wanda ya tura mu fashi gidanku sai  ku taru  ke da jami’an tsaro ku  cutar  damu ko  ? 
yana rufe baki yaji ta rungumesa tsam  ta bayansa tana cewa  “wallahi kaji na rantse maka  bazan sheidawa kowa ba ,bazan zamo me Saka hannu gurin cutar da kai ba  ,ya juyo daita gabansa suka  fuskanci juna  “dame zaki gamsar  dani  bayan tun farko kice da bakinki kika fad’a min zaki tona min asiri ?” ta tsugunna gwiwowinta  biyu a kasa “,ka  yarda dani Adnan na rantse  maka bazan aikata  hakan  ba “.  ya tako  a hankali ya tsugunna a gabanta “na sani bazaki fad’a ba amman ni ba mahaukaci bane da zan fad’a miki wanda ya tura mu a aiki gidanku ,  babu wannan ajandar  acikin aikinmu  ko gaban alqali za’a Kai d’aya daga cikinmu da wahala ya fad’a  ,kada ki damu ki bar son jin komai  gida ne dai zan kaiki a duk sanda wa’adi ya kai   ya fad’a yana janyota jikinsa  ya makaleta tare da Kai bakinsa daidai kunnenta   “ki K’ara natsuwa  da  jin  dumin jikina .”

Tayi  shiru zuciyarta na quna  da  tuttukin bakinciki ,duk  abinda take  tana  yi  ne dan ya fad’a mata wanda ya bashi aikin amman shine zai  rainawa kansa hankali  yace ita ya rainawa  ?”   cike da matsanacin  bakinciki  fixge jikinta  tace ” kar Allah yasa ka fad’a kuma Allah ya Isa da rungumata da kayi ban yafe maka ba  mugu kawai  me   zuciyar  dutse  duk  irin rantsuwar dana  yi maka bai sa ka  yarda dani ba  saboda muguwar zuciya irin taka  .” cikin  dariya ya sake  janyota jikinsa sosai ya  rungumeta tsam yana busa mata numfashinsa   tare da cewa “kada ki damu da irin zuciyata  dan babu abinda zai qareki dashi  Allah ya Isa  Kuma daman allah   isashe ne ko  baki ce  ba  , wayonki yayi  matukar  burgeni I love  it keep it  up  yayi  mata  kiss  a goshi sannan  yace “zaki cigaba da zama da Adnan har zuwa sanda yaga damar  maidake gidanku   sannan kiyi k’okari ki rage wannan  soyayyar da kike  masa  idan ma da hali ki cireta  gbdy  ya saketa ya koma jikin window  ya tsaya yana kallon farfajiyar  gidan  kusan minti biyar yana tsaye sannan ya juyo “me zaki  ce akawo miki  kici  ki sha magani ? babu abinda zanci ta fad’a a fusace  tana dubansa hawaye na tsiyayowa akan quncinta  “daman Kin saba  kwana da yunwa  idan shi kike ra’ayi  fine  ,I don’t care ya nufi  kofar fita daga d’akin ya barta cikin tsananin damuwa da sake  shiga tashin hankali .”

Yana fita number minister ya fara nema kira uku yayi kafin a d’auka ,hajiya zainab ce ta dauka cikin   sanyayyiyar   murya  tace” hello yana jin sautin muryar ya fahimci mahaifiyar tanweer ce dan bazai manta da muryar ba da irin kuka da kururuwan da tayi a daren  da zai taho da tanweer muryarsa a dikile ya soma magana cikin Isa ” Ina minister ?ta waiga a sukune ta Kalli Inda minister yake zaune aqasan tayis yayi tagumi da hannunsa d’aya cikin tsananin tashin hankali “wake magana ?ta tmby cike da faduwar gaba “babu buqatar sanin haka sai dai dalilin Kiran shine ki fad’awa mijinki idan yana kusa ” cewar ya dakatar da kawalayen daya tura haushi  gari dan nemammamu  wato jami’an tsaro  idan ba haka ba zai zama  sanadin rasa rayuwar diyarsa tanweer   “.
nan take jikin hjy zainab ya kama rawa hawayen dake makale a kwarnin idanunta suka sauka akan quncinta , a hankali ta soma karanta hasbinallahu wa ni’imal wakil  tana  cigaba da  sauraransa “ki fad’a masa ya janye if not you’ll lose your daughter  ko Kuma musa ayi reping dinta mu yada a social media  yana gama fad’ar haka yayi disconnecting din kira yana fesar da iska.
wani kuka hjy zainab ta fashe dashi ta zube kasa tana  furta kalmar  ” inna lillahi wa inna ilaihi rajiun da sauri minister ya matso kusa daita dan tunda ta d’auki wayar tana kallonsa shima ya tattara hankalinsa da natsuwarsa gurinta a rud’e yake tambayarta “menene zainab me akace miki   a  wayar  da’aka  kira ?” dan girman  Allah ka kira   office  din commissioner yanzu yanzu ka  sheida masa a tsaida jami’an tsaron nan bana son na rasa tanweer ,bana son wani mummunar abu ya faru daita  iya abinda ta fad’a kenan ta zube jikinsa tana sake fashewa da wani sabon kuka  numfashinta na sama da kasa. kamota yayi ya rungumeta yana shafa bayanta”is  okay zainab babu abinda zai samu tanweer dinmu da izinin allah  lafiya zata  dawo  garemu . yayinda ita Kuwa hjy zainab babu abinda take cewa sai “ka kira commissioner .”
Can  bangaren  jami’n tsaro kuwa suna  Isa 1829  plaza  dake  gaban isalo a  matukar  harzuke suka   firfito  suka  shiga  ciki  kmr  d’azu wasu suka tsaya a waje Wanda suka shiga suka fara  tambayar manager gurin, Kai tsaye aka nuna musu Inda yake  nan da nan suka fara aika masa tambayoyi akan mutane da suka shigo plaza din a wanni da suka gabata  “ai mutane dayawa sun shigo a yau din nan yalla’bai  “ko zaka iya gane fuskokin wanda da suka shigo ya fad’a  tare da nuna masa hoton jaguwa ?” gsky bazan iya ba  amman  tunda ga hoto  bari mu qunna cctv  camera mu duba  ” take  yayi rewarning   cctv   suka tsurawa   tv din dake gurin kusa guda biyar idanunsu , idanun manager ne ya Kai kan motar jaguwa   “yalla’bai  ga wata   mota nan ta tsaya a haraban plaza a awa biyu  data gabata nan  dukkaninsu  suka   bada attention dinsu suna duban motar suna sauraronsa ”  mutun d’aya ne ya fito daga cikin motar  fuskarsa  rufe da face   mask   nima Kuma a wannan  lokacin na fita  Kuma tabbas naga wannan motar mai number 2548 bayan ya shigo nima na dawo Ina kallonsa yana daukar dogayen  riguna na mata haka kawai naji hankalina bai kwanta dashi ba  idanuna na kanshi har sanda ya biya kudin kayan  ya wuce duk yadda akayi wannan mutumin ne duk da fuskarsa bata bayyana ba kamar yadda hotonsa yake  suna tsaka da sauraronsa kiran commissioner ya shigo wayar  dcp, ya d’auka cikin sauri yana cewa “hello sir “kuyi maza ku dawo akwai matsala “matsala Kuma sir ?
“Eh babba kuwa  domin rayuwar yarinyar na cikin hatsari idan aka cigaba da bibiyarsu ga dukkanin alamun akwai wanda yake yiwa  hukuma zagon kasa”.  aikuwa yayi babban kuskure ya cuci alluma har ma da zaqaqarun yansanda masu k’okarin ganin an kawar da ta’addanci a kasa  inji cewar dcp batare da bata lokaci ba dcp ya juya yana  bawa yaransa  umarni .”Tafiya kawai dcp yake baya ko gamin gabansa saboda takaici da bakinciki wai sai yaushe ne zasu yi nasara akan jaguwa ?sai yaushe zasu yi nasara akan shi Kawar dashi daga doron duniya da wannan tunani ya Isa gidansa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button