KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Wani gigitacen mari ya wanka mata  yana  huci   ta  dafe  kuncinta  daidai Inda hannunsa ya sauka  tana  dubansa Ido fal  da  hawaye “akan na fad’a maka gaskiya  shine   ka  mareni ?” to karya ne baka  sata ,baka bin mata , baka…”a tsawace  yace ” Kada  ki  sake fad’a min  maganar   banza  idan  kika  sake fad’a  min maganar  banza   wallahi zanyi miki  abinda har ki mutu  ba  zaki manta  dani  ba  ko ubanki  bai Isa  ya Kalli  idona  ya fad’a  min maganar da kika  fad’a min   ba bareki”  .
tayi  shiru   tana   kallonsa ta  kasa  cewa   komai  kafin daga bisani  tayi  kasa da muryarta  “,Allah   ka saka min ” ya  sake d’aga hannu zai sauke mata  wani  marin  tayi  saurin kaucewa ta dube shi Ido cikin Ido “da gatana da komai  amman ka d’aukoni  ka rabani da gatana  ka  maidani  jaka to wallahi  na barka da Allah duk abinda ka min ka jira sakamako  ” tana gama  fad’ar haka ta juya zata bar d’akin ya biyota  ya shakota “,Ina  zaki  ki dawo ki  gama  tsine min  “,ni ka sakar min wuya  ,bazan saka ba muddin kina son zaman Lafiyarki  a gidan nan  ki iya bakinki  akan abubuwana dan wannan   halin   naki  yana d’aya daga  cikin  abinda  yasa na tsaneki yanzu  sam baki  da  kunya “.
“naji  kaima ka daina abinda zai sa na dinga   maka rashin kunya ,  da  kyar ta sanya  gbdy karfinta ta kwaci kanta tana haki fixgota  yayi  ya maka   akan gado yana mata  wani  irin  kallo  mai  firgitarwa bayan second biyu ya sawa  kofar key  ya d’auki towel din data  fito  dashi  ya   wuce   ya  shiga  bayi    yana  jan tsaki  .
tanweer  ta dafe kanta tana  jijigawa “na  shiga  uku  ni tanweer wani irin iftilai   ne haka  ya fad’a min ?  yawon  zagin  ubana  da yake yana mugun  bata min    rai  kusan  yafi duk wani wulakanci da yake mata  ,da  kyar  ta  rarrashi   kanta  ta  kwanta tana  tunani  adadin   kwanakinta a gidan a lisafinta ta share  wata  biyu kenan  zata  shiga  na uku a hannunsa  tana kwance lamo
 ya fito kungunsa d’aure da  towel  yana goge  jikinsa da alamun  wanka  yayi  gajeren  wondo ya  d’auka  ya saka ya  kwanta kusa  daita  tana ganin haka tayi  saurin  ta matsawa daga kusa dashi dan har lokacin warin wiwi  bai  bar  jikinsa ba  .”

ganin abinda tayi yasa  haushi ya kamashi  cikin fushi ya  fixgota   jikinsa da karfi  ta sake janyewa
ya sake rikota  sosai  “ke kin isa na kwanta kusa dake ki tashi ? “dame kike takama  dashi ? ta  bud’e  idanunta  sosai “bana takama da komai Amman gaskiya ka daina taba min jiki dan ni ba  matarka bace sannan ba karuwa  bace  da zaka dinga had’a jikinka da nawa  bazan  iya irin wannan  rayuwar ba, kawai ka kyaleni  idan bazaka  maidani gidanmu  ba zan hakura  na zauna amman bazan iya wannan shirmen da haukan ba wallahi idan baka farga ka tuba ba ka jira mako..” “ya Isa ! ya isheki haka    jaguwa ya fad’a a  fusace  “ke ni zaki  gayawa maganar  banza   akan  abinda  isana  ya bani  dama  ba”.tayi  saurin tashi daga  jikinsa ta  zauna tana dubansa  tace “ban fahimceka ba ?   menene Isan naka ya baka ba ? Yayi  mata  kallon banza kana  yace  “ke mana ni gani nake  kin zama mallakina duk  da  bana sonki kuma dole nayi abinda na gada  dama dake “.ranta ya dugunzuma a fusace tace  “wallahi karya ne , wiwin da kasha ya fada maka  karya  baka Isa  kayi abinda kaga dama dani  ba,  Kuma daga yau ka daina taba koina a  jikina  har sanda zan bar gidan nan tunda bana Uba.. …”
Ji tayi ya zabga mata mari  a fusace  tare da durowa daga kan gadon Yana  dubanta” Ina gargadinki  da ki iya bakinki  da furta min duk Kalmar  da kika ga dama domin idan  ba haka   zan miki rashin mutunci dan ni ko kusa ban d’auki mace   a komai ba illa abun  bukatata  ki sani Ina da halin da zan aje irinki  guda  hamsim idan naso  dan ma Kinga na barki  haka batare da na aikata wani abun asha dake   ba shine  zaki kawowa  mutane  salo ?
“to ni Ina ruwana idan kaga dama ka cika gidan nan  makil da karuwai   wannan  matsalarka ce  ni  dai  karka  tabani  “.
Ya Isa Inda ya ajiye wayoyinsa  ya  d’auki daya  daga ciki ya duba  lamba  pretty  ya  kira ya sa  a handsfree ringing biyu   muryata ta fito  tana cewa “Allah ya taimaki  jaguwa  uban gidana  , jaguwa yace “pretty  kina Ina ? Ta lankwashe murya kmr tana gabansa  tace “Ina gidansu ogechi yanxu muka shigo gida  “kuzo ku  duka  bai  gama maganar ba tanweer ta k’araso  ta fixge waya  hankalinta  a matukar tashe  da abinda ke Shirin  faruwa, a gabanta zai  kira karuwarsa wannan wacce irin rayuwa ce  ? “Wacce irin rayuwa ya saka kanshi  “ita da wasa tace ya cika gidan da karuwai   shine  zai  kirasu wayyo  Allah na shiga uku ”  akansa an kirata da  Kalmar karuwa ,yanzu km zai gayyato karuwai zuwa gidan “to me zai hana ka maidani ka samu damar yin iskancinka  da tushe tunda shine a gabanka ?  tayi maganar a matukar tsorace  dan tunda ya fara da maruka  tasan duka ma bazai masa wuya ba.

ta  juya cikin sauri ta bar d’akin zuwa bayi   tare da fashewa da kuka    “a she zata tsinci kanta cikin makauniyar soyayya irin haka , hakika so bai mata adalci  ba daya rasa Inda zai  Kai soyayyarta sai gurin  mutumin da bai san  darajan  mace ba bata  San tsawon lokacin data dauka ba a zaune a toilet  tana ayyana abubuwa da dama  akan rayuwarta  ” bazata taba yarda tsoransa yayi tasiri a zuciyarta ba  muddin soyayyar da take masa ta gaskiya ce ya dace tayi komai dan ta rabashi da irin rayuwar da yake, zata rabashi da kowacce karuwa acikin rayuwarsa ta yunkura da kyar ta mike ta fito  haniya ta dinga Jiyo sama sama aranta tace “sun zo kenan ?  ta fito  ta nufo babban  falon  gidan Inda tafi tunanin suke  ta iske mata zaune kusan tsirara domin kowaccesu daga ita sai pant da bra shi Kuma jaguwa yana nan   sanye da gajeren wando  ajikinsa  , hayakin taba  kawai  ke  tashi  da kwalayen taba   burjiki  akan tebul din gabansu Sam basu lura da fitowarta ba har sai data  karaso har  gabansu ta kira sunansa da fusatacciyar  murya “Adnan !” duk  sukayi  hanzarin  suka tsaya cak suka  bude  idanunsu suna dubanta Shima din idanunshi ya zuba mata cikin mamaki da fushi yace “me ya fito dake ?
“Ko nace ki fito ne “a fusace tace ban sani ba wato kana tunanin zaka kawo  karuwai cikin gidan  nan alhalin Ina cikinsa  in amince wallahi tallahi baka Isa ba , bazai  yiwu  ba sai dai  kayi daya cikin biyu ka  mayardani  gidanmu ko  ka bani damar na fita a gidan nan na kama gabana amman muddin Ina cikin gidan nan an daina alfasha   da kawo yan iska kana badala dasu   sai dai kaje waje kayi iskancinka  ta k’arasa  maganar tana fashewa  da kuka  “,wallahi bazan yarda ba ya  zama dole su bar gidan  nan kuma a yanzu  …”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button